← Book details Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 158

Sashe 75

Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ko akwai wata matsala ne Halima?" Na toshe baki na da hannu dan kar sautin kukan da ya taho mun lokaci ɗaya ya isa kunnuwan sa daƙyar na iya saita kaina na ce
"Babu komai Abba, nima dama zama hakan ya isheni dama ina so na fara aikin na haɗa da business ɗin duka"
"Ya dai fi kam, Allah yayi miki albarka ki gaida maigidan naki" ya sake faɗa na amsa da " Amin" kafin na kashe wayar na kife kaina akan pillow na fashe da kukan tausayin kaina.

*KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*

*PAGE 31*

Nayi mamakin yanda Bilal bai musa ba lokacin da nayi masa maganar service. Nayi sa'a a lokacin ana dab da fara registration dama, ranar da aka buɗe kuwa banyi wasa ba na je na yi a matsayin mara aure saboda ko da na gaya masan ya ce toh nayi zaton zai je ya fitar da certificate of marriage da domicile letter waɗanda zan buƙata amma har ranar ta zo bai ce mun komai ba nima kuma banyi masa magana ba dan ina gudun kada ya canza ra'ayi.

Posting ya fito aka kaini, ban wani damu ba tunda ba nesa bane nasan zan iya zuwa nayi registration a ranar na dawo ba daga nan na nemi relocation dan ba zai yuwu nayi service ɗin a can ba. Sai ana gobe shiga camp ɗin sannan na faɗa masa Jigawa fa aka turani kuma gobe zan je.

"To me kike so na ce yanzu? Ai ba yau kika san Jigawa aka kaiki ba ko da yake yanzu sai kin gama yanke shawarar ki kike gaya mun kinga wata magana tawa bata da amfani sai ki je ai" amsar da ya bani kenan. Washe gari kuwa na kama hanyar Jigawa da sassafe, saboda ban san sanda zan dawo ba Al'amin bai je makaranta ba na kaishi gidan Mama. Cikin sa'a dake ranar farko ce kuwa kafin ƙarfe uku na gama komai na karɓi exit, a Kano shida ta mun dan ma mota ta ɗan tsaya mana a hanya na wuce gida kawai ba tare da na ɗakko Al'amin ba dan na gaji kuma goben Juma'a ce ya ƙara hutawa Monday sai ya koma makarantar.

Ina tayar da sallar magriba wayata ta fara ƙara, yanda kira ya ringa shigowa daga wani ya katse ya ɗaga mun hankali, daƙyar na kammala ina yin sallama na ɗauki wayar gaba na ya yanke ya faɗi ganin Bilal ne. Ina shirin bin bayan kiran wani ya sake shigowa na ɗaga, cikin muryar dake nuna yana cikin tashin hankali ya ce
"Halima kina ina?"
"Ina gida na dawo mai ya faru?" Na faɗa cikin sauri.
"Hajja ce sukayi accident gamu nan a Emergency na Aminu Kano" ya faɗa lokaci ɗaya kuma ya kashe wayar.

A fili na shiga nanata Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Hajja kuma Accident? A garin yaya? Ina suka je?
Bani da mai bani wannan amsar sai kawai na saka wayar a ajihun rigar dake jiki na na ɗauki Sharifa muka fita. Sai da na je get na tuna ban ɗauki kuɗin da zan hau mota ba na sake komawa na ɗauka. Daƙyar na samu abun hawa duk wanda na tare sai ya ce ba can ya yi ba, a hanya nayi ta sake gwada kiran Bilal amma wayar taƙi shiga. Yanda na ji muryar sa na san da alama yanayin babu daɗi a raina na ringa addu'ar koma menene Allah ya taƙaita wahala.

Hanani shiga securities sukayi duk yanda na roƙe su daga ƙarshe na koma gefe na cigaba da kiran Bilal har sannan kuma wayar taƙi shiga. Ga gajiya ga yunwa dake damuna ga sauron bala'i a gurin haka nan na tsaya a bakin ƙofa ina addu'ar Allah ya fito da shi ko wani da na sani ko zan samu su bar ni na shiga. Har ƙarfe tara muna tsaye kafin mai gadin yaga dama ya bari muka shiga. Ido na shiga warewa ina laluben ta inda zan hango su Hajjan amma ban dace ba. Wata Nurse na tambaya tace bata gane wa nake nufi ba, haka na ringa bi gado gado a can ciki na same su.

Hajja na kwace kanta da hannunta ɗaya naɗe da bandeji sai ledar jini da aka saka mata amma idon ta biyu. Ajiyar zuciya na sauke dan har ga Allah ban zaci haka zan ganta ba, irin yanda na ji muryar Bilal na ɗauka zanzo na tarar da ita a halin rai da mutuwa ne. Muna haɗa ido ta ɗauke kai gefe, na kalli sauran Anty Amina, Yaya Saude sai Fadila da Hadiza yar ƙanwar Hajja. Anty Amina ce kaɗai ta amsa sallamar da na yi musu, na jingina da gadon dan har jiri nake ji saboda yunwa da gajiya kafin na shiga gaishe su da tambayar mai jiki.

"Tun bayan magriba nake a waje maigadin ya hanamu shigowa ina ta kiran wayar sa kuma tun ina hanya bata shiga" na faɗa. Ina rufe baki Fadila tayi tsaki ta ce
"Ƙaryar banza"
"Ke Fadila meye haka?" Anty Aminan ta tsawatar mata. Murmushi kawai na yi kaina a ƙasa, kusan minti biyar duk munyi shiru sai ga Bilal da Hafiz sun ƙaraso gurin. A mutunce muka gaisa Bilal kuwa muna haɗa ido ya mun kallon da na fassara da harara. Hafiz ya karɓi Sharifa dake bacci a hannu na yana tambayar ina Dady na ce masa yana can gidan mu.

"Jikin nata ai da sauƙi ba kamar yanda na yi tunani ba" ya faɗa, a raina na ce
"Munyi biyu". Bilal ya ce
"Da sauƙi kam amma baka ga a yanda muka kawota asibitin bane Allah ya taimaka ta samu kulawa da wuri ne kawai amma da an ja wani lokaci irin jinin da ta zubar da ba wannan maganar akeyi ba".

"Toh Allah ya ƙara kiyaye gaba Allah kuma ya sa ya zame mata kaffara" cewar Hafiz gaba ɗaya muka amsa da "Amin".
Fita suka sakeyi da Bilal, na gyara tsayuwa ta dan ƙiris ya rage na faɗi babu kuma wanda ya mun tayin gurin zama a cikin su bayan wani lokaci suka sake dawowa. Sallama yayi musu bayan ya aje musu kuɗin da ban san ko nawa bane ba. Hajja ta ringa saka masa albarka haka su Yaya Saude kamar maroƙa sai faman zabga masa godiya suke. Ina lura da Anty Amina dake ta faman cika tana batsewa bani da tabbacin mai aka mata da alama kuma kamar bata ji daɗin rawar jikin da suke ta yi ba.

Sharifa ya miƙo mun ya na cewa Bilal
"Ba yanzu zaku wuce gida ba? Dare fa ya fara ga gurin da sauro kada a ɗibar ma Sharifa malaria". Naji daɗi har raina da Bilal ɗin ya ce tafiya zamuyi Fadila da Hadiza ma suka ce tafiyar zasuyi muka fita gaba ɗaya ya rage Anty Amina da Yaya Saude wadda zata kwana da Hajjan. A hanya Hadiza ta sauka Bilal ya tare mata Adaidaita da zau ƙarasa da ita muka wuce tare da Fadila ban so kwanan da ta ce zata yi a gidan mu ba. Har gida ya sauke mu, a hanya ya cewa Bilal
"Ya dai kamata fa ka samu mota ko ƙarama ce saboda irin haka" shi kuma yayi dariya ya ce

"Tukunna dai ai har yanzu ban isa riƙe mota ba, yanda rayuwa ta ƙara tsada mota ai sai irin ku dai manya mu dai barmu mu cigaba da hawa Adaidaita sahun da muka fi ganewa". Hafiz ɗin ya yi dariya ya ce
"Gara ma kace baka da ra'ayin siyan mota zan fi yarda idan kuma haka ne ai ita Madam na san ba zata ƙi ba sai ka siya mata ko dan saboda hidimar yara ko kema kin fi ganewa hawa Adaidaita sahun?" Ya jefo mun tambayar, murmushi kawai nayi na ce
Hawa Adaidaita ai sai dole gara dai ya taimaka ya siya mana motar mu huta"
"To ka dai ji abinda Madam ta faɗa" Cewar Hafiz ɗin. Zancen motar suka cigaba dayi har muka isa. Ua zaro kuɗi daga aljihun sa ya sakawa Sharifa a hannu sanda zamu sauka nayi masa godiya muka wuce.

Muna ƙoƙarin shiga falo Fadila ta ce mun
"Yanzu ko kunya bakya ji da auren ki a gaban mijin ki kike washe baki kina magana da wani namijin daban? To tun wuri idan ma zaki shiga hankalinki ki shiga dan Yaya Hafiz da iri na ya dace" ta faɗa tana wani watsa hannu da juya ido.
Kallonta nayi cike da mamakin kalamanta na ce
"Da alama kinyi hauka ko Fadila? Ban gane na washe baki ina masa dariya ba? kin san me kike cewa?"

"Tsaki ta yi ta shige ciki kamar gidan ta. Na bita da kallo kafin na bi bayan ta zuciya ta na tafarfasa na ce
"A zaton ki kowa shashasha ce irin? Ko zamanin yammatanci na ban banzatar da kaina nayi alaƙar banza da maza ba balle yanzu da nake da aure kuma wai da abokin miji na. Kije ke da Allah ƙazafin da kika mun" na nufi ɗaki dai dai lokacin Bilal ya shigo, tana ganin sa ta shiga matsar hawayen ƙarya tana cewa
"Ni kike cewa karuwa Halima?"

"Da Allah malama dakata duk naji abinda kowaccen ku ta faɗa, ki shiga hankalin ki ba kowanne iskanci zan ɗauka ba yanzu" ya faɗa yana nuna ta da yatsa. Murmushi na saki raina fes da yanda karo na farko ya tsaya mun na kalleta na ce
"Ba a koda yaushe ƙarya da munafunci suke cin nasara ba nan gaba kin san me zaki faɗa" na wuce ɗaki Bilal ya biyo baya na.
Chapter 75 · 0% Book details