Sashe 142
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kawu Ɗayyabun ya ringa faɗa yana cewa
"Wane irin rashin hankali ne haka? Ita Hajara wai sai yaushe zata girma ta fara abu irin na mutane masu hankali? Dama mace ta taɓa aurar da kanta ne ko kuwa uwa ce take bayar da auren yarta? Daga ku har uwar taku sai a rasa wayafi wani tunani, kaima nan zancen ya iskeni ance ka saki uwargidanka dama kuma duk ina jin labarin irin ɗiban albarkar da kai da uwarka da yan uwanka kuka ringayi mata, toh hausawa dai suka ce duk wanda bai yi sharar kasuwa ba zaiyi ta masallaci dan haka tun wuri in dai da gyara ina baka shawarar ka dawo da matarka dan ba zaka gane illar da kayiwa kanka ba sai a gaba. Ita kuma Hajara zan kirata" akan haka suka rabu.
Washe gari kuwa ya kira Hajjan yace taje gida ta sameshi yana son magana da ita ba musu kuma ta shirya ta tafi yayi mata tatas sannan yace su dakatar da duk wani shiri da sukeyi Fadila ta gayawa yaron yaje ya gaida iyayenta maza tukunna idan sukayi bincike sukaga bashida wani aibu sannan su bashi lokacin da zai turo ayi magana.
Ta koma gida ta saukewa Bilal tijarar da batayi a gaban Kawu Ɗayyabun ba tunda shi ya kai masa gulmar amma kuma dole tayi abinda yace ta kira Baba Sani yaƙi ɗauka sai a wayar matarsa ta sameshi shima daƙyar ya karɓa sukayi magana tana gaya masa dalilin kiran kuma yace babu shi a cikin wannan magana
"Kin manta kashedin da kika mun akan yayanki Hajara? Ai ko ni na kawo rashin zuciya duniya ba zan sake tsoma baki cikin abinda ya shafeku ba, bani kaɗai bane ɗan uwan ubansu ai muna da yawa ki nemi wani" ya bata amsa daga haka kuma ya katse wayar. Daga ƙarshe dai sai babban yayansu Bilal ɗin Alhaji Salisu ta taka har gida ta samu dan Kawunnansu duk wanda ta kira sai yace yana Aa dan kowa nada labarin ɗibar albarkar da tayiwa Baba Sani da Aminu akan zancen Bilal.
Fadilan ce ta raka shi gurin Yayan nasu akayi sa'a ashe ma sun san juna akwai hulɗa ta cinikayya tsakaninsu, kamar yanda ya cewa Hajja a tsayin lokacin daya san Alhaji Ahlan saurayin Fadilan ya san mutumin kirki ne kuma yayi tambaya akansa an tabbatar masa da mutumin kirki be kuma yana da asali mai kyau dan Babansa nada sarauta acan Zarian ma. Ya taɓa aure sau biyu, ta farkon rasuwa tayi suna da yara biyu Mace da Namiji ta biyun kuma rabuwa sukayi, shikenan aka cigaba da shirin biki, maza sunzo sun sake kawo kuɗin aure da Sadaki bayan wanda ya rigada ya bata.
Bayan ya gama sauke musu kayan miyan a tsaitsaye suka gaisa ya wuce saboda zaije ya ɗakko Jalilah ne a airport.
Motarsa ce taƙi tashi, ganin zata ɓata masa lokaci ya barta ya kira wani abokinsa dake siyar da motoci a Gadon ƙaya yace zaizo ya karɓi mota yanzu, da wannan saurin ya faɗa Adaidaitan daya gani a bakin layin ashe rabon su haɗu da Halima ne.
Harga Allah har ya zauna bai san ita bace a ciki dan hankalinsa na kan wayarsa sai da tayi magana kafin yaji muryarta ya kuma yi mamaki matuƙa amma bai nuna hakan ba har ransa kuma sai yaji rashin daɗi da bai san dalilin sa musamman ganin da yayi mata ta canza tayi wani kyau fatarta har wani ƙyalli takeyi baka buƙatar a faɗa maka ta samu hutu da kwanciyar hankali. Shi da yake nan yana tunanin tana can cikin halin ƙaƙanikayi soyayyarsa ta hanata sakata ko wacce daƙiƙa cikin dakon kiranta yakeyi domin ya tabbatar ba zata taɓa iya rayuwa mai ma'ana ba tareda dashi ba.
Daɗewar da akayi yanzun ma bata waiwayeshi ba ya sani cikin biyu, ko dai an ƙwace wayarta ne tunda kowa nata ba son su tare yakeyi ba ya san zasu iya ƙwacewa dan kar ta kirashi kuma a hanata fita idan kuma ba haka ba toh bata da lafiya, yana kuma lissafe da kwanaki jira yakeyi sai ya rage saura kwanaki ta fara period ɗin ta na ƙarshe sannan zaije ya mayar da ita sai dai su mutu da baƙin ciki a lissafi kuma yau saura kwana goma sha biyu ya aiwatar da shirinsa tunda saura kwana sha biyar a calendar ta da take cikin wayarsa sai kuma kwatsam gata a yanayin da bai tsammaci ganinta ba ita ashe tuni tayi move on har ta buɗe sabon babi a rayuwarta.
Ya daki stirring a fili ya ce
"Ba zai yuwu ba, ba zan taɓa barinki ba Halima. Kece silar lalacewar komai dan haka duk yanda rayuwa ta juya tare zamu fuskanceta".
Daga Airport ɗin kai tsaye store suka wuce, a hanya Jalilah take ce masa
"Amma ban taɓa zaton Sudais zai iya cin amanata ba"
"Ai kallonki kawai nakeyi, ban fahimci ko rashin yarda bane ko menene ya saka ni baki bani keys ɗin gurin ba kika bawa wani, gashi yanzu abinda ya faru" ya faɗa ba tareda ya kalleta ba. Jalilah dake danna waya ta ɗaga kai ta kalleshi haɗi da yin ƙaramin murmushi amma bata ce komai ba. Da suka isa shi ya riƙe mata jakarta, ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke sanda ya zura mata keys ɗin daya zare ranar da zata koma Abuja yabi bayanta kamar yana wani murmushi irin na samun nasara.
Bai zaci komai zai zo masa da sauƙi ba, ana gobe zata tafi wancan zuwan da tayi suka zo ta nuna masa store ɗin da kuma kayan da aka sauke ta kuma nuna masa Sudais da tace ɗan ƙawar Momynta ne store ɗin na Babansa ne ya basu aro. Ko a fuska bai nuna mata jin haushi ba sanda ta maidawa da Sudais ɗin muƙulli da zasu tafi a hanya tana ta yabon yaron da irin amanarsa ransa ya ƙara ɓaci ya ringa ji kamar jurwaye take masa mai kamar wanka wato shine mara amana kenan?
A mota ya tsinci muƙullin bayan ya dawo daga kaita Airport, har yayi niyyar kiranta kuma ya fasa da daddare kuwa sai gashi ta kirashi akan yaje ɗakin data zauna ya duba mata ta manta spare keys na store da Sudais ya bata, har yayi niyyar ya ce mata suna gurinsa kuma kawai ya fasa yace mata toh kawai, da safe kuwa bai ko je Hotel ɗin ba ya kirata yace yaje an duba basu ga komai ba daga nan kuma zuciyarsa ta fara raya masa akan ya ɗibi wasu daga cikin kayan ya siyar tunda yana tsaka da buƙatar kuɗi kuma babu yanda za'ayi asirinsa ya tonu tunda dai ba'a sakashi a cikin sabgar ba.
Sai da ya saita hanya ta yanda ba wata ƙura da zata iya biyo baya kafin ya fitar da kayan ya karɓi kuɗaɗen sa yake ta kashe gararin gabansa dasu, ko da yake a yanzu yanda yake ji baya tsoron Jalilan ta sani dan a shirye yake domin daga yanda Alhaji Lawan yake threatening nasa ya san dole allura zata tono garma duk kuma abinda zai faru ba dai za'a kashe shi ba kuma ba zai kullu ba dan shari'a yanzu kuɗi ce kuma ya shirya shiyasa ko da ya tura masa da message jiya akan kowanne lokaci za'a iya kawo masa sammaci mayar masa amsa yayi da cewa
"Do your worst" yayi blocking layin.
Bayan sun gama da can suka kama hanya yana murmushin da shi kaɗai ya san ma'anar sa ya tambayeta ina zai kaita yanzu?
"Muje can gida na huta tukunna idan yamma tayi sai ka kaini gidan Hajja na gaisheta kwanaki da yawa ko a waya idan na kira bana samunta" ta faɗa tana lafewa a cikin kujera. Gabansa ya faɗi, wai mai take nufi da mayar da gidansa gurin saukarta yanzu? Amma dai bai ce mata komai ba ya kama hanya abinda ya sa bai damu sosai ba ya san zuwa yanzu Zulaiha ta tafi gidan Hajja tunda sunyi magana tun sanda zai fito ta faɗa masa zataje.
Clashing sukayi da wata mota suna shiga layin ita kuma tana fita sai da suka wuce ƙwaƙwalwarsa ta tariyo kamar fuskar Zulaiha ya gani a gaban motar, ita kanta motar sai yaga kamar ya santa a wani guri amma ya manta a ina ne. Saida yayi parking Jalilah ta fita ta wuce part ɗin sa kafin ya kira Zulaiha.
"Kina ina?" Ya tambayeta bayan data amsa daga can tace masa
"Ina gidan Umma mai ya faru?"
"Gidan Umma kuma? Baki tafi gidan bikin ba kenan?" Ya sake tambayarta bayan daya sauke ajiyar zuciya ta samun nutsuwa. Sanar masa tayi wai Umman ce bata jin daɗi tana shiri zata fita Nuratu ta kirata shine ta fara zuwa can gidan kuma ta kira wayarsa ta gaya masa amma bata sameshi daga nan sukayi sallama bayan yace ta zauna a gidan Umman kawai ta kula da ita zaije ya ɗakko ta bayan isha'i.
Ganin Jalilah ta fito ya saka yayi saurin kashe wayar yana kallonta, ta yamutsa fuska ta ce
"Na fasa ka kaini Hotel kawai". Bai damu ba suka sake fita, yana tareda ita har gurin goma kafin ya mata sallama ya biya gidansu Zulaiha ya ɗauketa suka wuce gida.
Washe gari bayan an sakko daga sallar Juma'a aka ɗaura auren Fadila da angonta Alhaji Ahlan. Kusan suman zaune Bilal yayi lokacin da sukayi arba da angon Fadilan, mutumin daya siyi gidan Jalilah, wanda ya biyo Zulaiha ranar da sukaje siyan shawarama kenan gidan ne za'a saka Fadila a ciki. Ji yayi kansa ya na nema ya kama ciwo ya sulale ya fita daga masallacin yana shiga mota wayarsa ta fara ƙara ganin Zulaiha ce ya ɗauka a taƙaice ta sanar masa wai yayi baƙi, ya tambayeta su waye tace wai bata sansu ba Mace da Namiji ne.
"Toh ke mai kika zauna yi dama baki taho gidan bikin ba?" Ya tambayeta, daga can tace
"Ina shirin fitowa suka zo ai ko sai in kulle in hana su shiga?"
"Wane irin rashin hankali ne haka? Ita Hajara wai sai yaushe zata girma ta fara abu irin na mutane masu hankali? Dama mace ta taɓa aurar da kanta ne ko kuwa uwa ce take bayar da auren yarta? Daga ku har uwar taku sai a rasa wayafi wani tunani, kaima nan zancen ya iskeni ance ka saki uwargidanka dama kuma duk ina jin labarin irin ɗiban albarkar da kai da uwarka da yan uwanka kuka ringayi mata, toh hausawa dai suka ce duk wanda bai yi sharar kasuwa ba zaiyi ta masallaci dan haka tun wuri in dai da gyara ina baka shawarar ka dawo da matarka dan ba zaka gane illar da kayiwa kanka ba sai a gaba. Ita kuma Hajara zan kirata" akan haka suka rabu.
Washe gari kuwa ya kira Hajjan yace taje gida ta sameshi yana son magana da ita ba musu kuma ta shirya ta tafi yayi mata tatas sannan yace su dakatar da duk wani shiri da sukeyi Fadila ta gayawa yaron yaje ya gaida iyayenta maza tukunna idan sukayi bincike sukaga bashida wani aibu sannan su bashi lokacin da zai turo ayi magana.
Ta koma gida ta saukewa Bilal tijarar da batayi a gaban Kawu Ɗayyabun ba tunda shi ya kai masa gulmar amma kuma dole tayi abinda yace ta kira Baba Sani yaƙi ɗauka sai a wayar matarsa ta sameshi shima daƙyar ya karɓa sukayi magana tana gaya masa dalilin kiran kuma yace babu shi a cikin wannan magana
"Kin manta kashedin da kika mun akan yayanki Hajara? Ai ko ni na kawo rashin zuciya duniya ba zan sake tsoma baki cikin abinda ya shafeku ba, bani kaɗai bane ɗan uwan ubansu ai muna da yawa ki nemi wani" ya bata amsa daga haka kuma ya katse wayar. Daga ƙarshe dai sai babban yayansu Bilal ɗin Alhaji Salisu ta taka har gida ta samu dan Kawunnansu duk wanda ta kira sai yace yana Aa dan kowa nada labarin ɗibar albarkar da tayiwa Baba Sani da Aminu akan zancen Bilal.
Fadilan ce ta raka shi gurin Yayan nasu akayi sa'a ashe ma sun san juna akwai hulɗa ta cinikayya tsakaninsu, kamar yanda ya cewa Hajja a tsayin lokacin daya san Alhaji Ahlan saurayin Fadilan ya san mutumin kirki ne kuma yayi tambaya akansa an tabbatar masa da mutumin kirki be kuma yana da asali mai kyau dan Babansa nada sarauta acan Zarian ma. Ya taɓa aure sau biyu, ta farkon rasuwa tayi suna da yara biyu Mace da Namiji ta biyun kuma rabuwa sukayi, shikenan aka cigaba da shirin biki, maza sunzo sun sake kawo kuɗin aure da Sadaki bayan wanda ya rigada ya bata.
Bayan ya gama sauke musu kayan miyan a tsaitsaye suka gaisa ya wuce saboda zaije ya ɗakko Jalilah ne a airport.
Motarsa ce taƙi tashi, ganin zata ɓata masa lokaci ya barta ya kira wani abokinsa dake siyar da motoci a Gadon ƙaya yace zaizo ya karɓi mota yanzu, da wannan saurin ya faɗa Adaidaitan daya gani a bakin layin ashe rabon su haɗu da Halima ne.
Harga Allah har ya zauna bai san ita bace a ciki dan hankalinsa na kan wayarsa sai da tayi magana kafin yaji muryarta ya kuma yi mamaki matuƙa amma bai nuna hakan ba har ransa kuma sai yaji rashin daɗi da bai san dalilin sa musamman ganin da yayi mata ta canza tayi wani kyau fatarta har wani ƙyalli takeyi baka buƙatar a faɗa maka ta samu hutu da kwanciyar hankali. Shi da yake nan yana tunanin tana can cikin halin ƙaƙanikayi soyayyarsa ta hanata sakata ko wacce daƙiƙa cikin dakon kiranta yakeyi domin ya tabbatar ba zata taɓa iya rayuwa mai ma'ana ba tareda dashi ba.
Daɗewar da akayi yanzun ma bata waiwayeshi ba ya sani cikin biyu, ko dai an ƙwace wayarta ne tunda kowa nata ba son su tare yakeyi ba ya san zasu iya ƙwacewa dan kar ta kirashi kuma a hanata fita idan kuma ba haka ba toh bata da lafiya, yana kuma lissafe da kwanaki jira yakeyi sai ya rage saura kwanaki ta fara period ɗin ta na ƙarshe sannan zaije ya mayar da ita sai dai su mutu da baƙin ciki a lissafi kuma yau saura kwana goma sha biyu ya aiwatar da shirinsa tunda saura kwana sha biyar a calendar ta da take cikin wayarsa sai kuma kwatsam gata a yanayin da bai tsammaci ganinta ba ita ashe tuni tayi move on har ta buɗe sabon babi a rayuwarta.
Ya daki stirring a fili ya ce
"Ba zai yuwu ba, ba zan taɓa barinki ba Halima. Kece silar lalacewar komai dan haka duk yanda rayuwa ta juya tare zamu fuskanceta".
Daga Airport ɗin kai tsaye store suka wuce, a hanya Jalilah take ce masa
"Amma ban taɓa zaton Sudais zai iya cin amanata ba"
"Ai kallonki kawai nakeyi, ban fahimci ko rashin yarda bane ko menene ya saka ni baki bani keys ɗin gurin ba kika bawa wani, gashi yanzu abinda ya faru" ya faɗa ba tareda ya kalleta ba. Jalilah dake danna waya ta ɗaga kai ta kalleshi haɗi da yin ƙaramin murmushi amma bata ce komai ba. Da suka isa shi ya riƙe mata jakarta, ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke sanda ya zura mata keys ɗin daya zare ranar da zata koma Abuja yabi bayanta kamar yana wani murmushi irin na samun nasara.
Bai zaci komai zai zo masa da sauƙi ba, ana gobe zata tafi wancan zuwan da tayi suka zo ta nuna masa store ɗin da kuma kayan da aka sauke ta kuma nuna masa Sudais da tace ɗan ƙawar Momynta ne store ɗin na Babansa ne ya basu aro. Ko a fuska bai nuna mata jin haushi ba sanda ta maidawa da Sudais ɗin muƙulli da zasu tafi a hanya tana ta yabon yaron da irin amanarsa ransa ya ƙara ɓaci ya ringa ji kamar jurwaye take masa mai kamar wanka wato shine mara amana kenan?
A mota ya tsinci muƙullin bayan ya dawo daga kaita Airport, har yayi niyyar kiranta kuma ya fasa da daddare kuwa sai gashi ta kirashi akan yaje ɗakin data zauna ya duba mata ta manta spare keys na store da Sudais ya bata, har yayi niyyar ya ce mata suna gurinsa kuma kawai ya fasa yace mata toh kawai, da safe kuwa bai ko je Hotel ɗin ba ya kirata yace yaje an duba basu ga komai ba daga nan kuma zuciyarsa ta fara raya masa akan ya ɗibi wasu daga cikin kayan ya siyar tunda yana tsaka da buƙatar kuɗi kuma babu yanda za'ayi asirinsa ya tonu tunda dai ba'a sakashi a cikin sabgar ba.
Sai da ya saita hanya ta yanda ba wata ƙura da zata iya biyo baya kafin ya fitar da kayan ya karɓi kuɗaɗen sa yake ta kashe gararin gabansa dasu, ko da yake a yanzu yanda yake ji baya tsoron Jalilan ta sani dan a shirye yake domin daga yanda Alhaji Lawan yake threatening nasa ya san dole allura zata tono garma duk kuma abinda zai faru ba dai za'a kashe shi ba kuma ba zai kullu ba dan shari'a yanzu kuɗi ce kuma ya shirya shiyasa ko da ya tura masa da message jiya akan kowanne lokaci za'a iya kawo masa sammaci mayar masa amsa yayi da cewa
"Do your worst" yayi blocking layin.
Bayan sun gama da can suka kama hanya yana murmushin da shi kaɗai ya san ma'anar sa ya tambayeta ina zai kaita yanzu?
"Muje can gida na huta tukunna idan yamma tayi sai ka kaini gidan Hajja na gaisheta kwanaki da yawa ko a waya idan na kira bana samunta" ta faɗa tana lafewa a cikin kujera. Gabansa ya faɗi, wai mai take nufi da mayar da gidansa gurin saukarta yanzu? Amma dai bai ce mata komai ba ya kama hanya abinda ya sa bai damu sosai ba ya san zuwa yanzu Zulaiha ta tafi gidan Hajja tunda sunyi magana tun sanda zai fito ta faɗa masa zataje.
Clashing sukayi da wata mota suna shiga layin ita kuma tana fita sai da suka wuce ƙwaƙwalwarsa ta tariyo kamar fuskar Zulaiha ya gani a gaban motar, ita kanta motar sai yaga kamar ya santa a wani guri amma ya manta a ina ne. Saida yayi parking Jalilah ta fita ta wuce part ɗin sa kafin ya kira Zulaiha.
"Kina ina?" Ya tambayeta bayan data amsa daga can tace masa
"Ina gidan Umma mai ya faru?"
"Gidan Umma kuma? Baki tafi gidan bikin ba kenan?" Ya sake tambayarta bayan daya sauke ajiyar zuciya ta samun nutsuwa. Sanar masa tayi wai Umman ce bata jin daɗi tana shiri zata fita Nuratu ta kirata shine ta fara zuwa can gidan kuma ta kira wayarsa ta gaya masa amma bata sameshi daga nan sukayi sallama bayan yace ta zauna a gidan Umman kawai ta kula da ita zaije ya ɗakko ta bayan isha'i.
Ganin Jalilah ta fito ya saka yayi saurin kashe wayar yana kallonta, ta yamutsa fuska ta ce
"Na fasa ka kaini Hotel kawai". Bai damu ba suka sake fita, yana tareda ita har gurin goma kafin ya mata sallama ya biya gidansu Zulaiha ya ɗauketa suka wuce gida.
Washe gari bayan an sakko daga sallar Juma'a aka ɗaura auren Fadila da angonta Alhaji Ahlan. Kusan suman zaune Bilal yayi lokacin da sukayi arba da angon Fadilan, mutumin daya siyi gidan Jalilah, wanda ya biyo Zulaiha ranar da sukaje siyan shawarama kenan gidan ne za'a saka Fadila a ciki. Ji yayi kansa ya na nema ya kama ciwo ya sulale ya fita daga masallacin yana shiga mota wayarsa ta fara ƙara ganin Zulaiha ce ya ɗauka a taƙaice ta sanar masa wai yayi baƙi, ya tambayeta su waye tace wai bata sansu ba Mace da Namiji ne.
"Toh ke mai kika zauna yi dama baki taho gidan bikin ba?" Ya tambayeta, daga can tace
"Ina shirin fitowa suka zo ai ko sai in kulle in hana su shiga?"