Sashe 158
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Kwanansa uku a Asibiti kafin aka sallameshi tunda ya yanke jiki ya faɗi bayan kyakkyawan ganin da yayi. Zulaihan ce tayi jinyar sa dan bayan da aka kaishi Asibiti ita Hajja tace a kira tunda ta gudu yanzu da wahala tazo sai ta dawo tayi jinyar Mijinta. Da ace Hajja ta ganta a gidan Fadilan iya kumburin da idanuwanta sukayi ya isa ya sa ta fahimci mai ya faru dan Ahlan da Fadilan ce mata sukayi yana shiga falon ya yanke jiki ya faɗi tunda kuma ta san dama bashi da lafiya suka tafi bata musa ba.
Daga Asibiti bayan an sallame su ya cewa Zulaiha ta wuce gida, shi da ita ne a ɗakin ta fashe da kuka haɗi da durƙushewa a gurin tana cewa
"Wlh tilastani yayi. Cewa yayi idan ban amince ba zasu mayar da kai gidan yari dan girman Allah kayi haƙuri karka sakeni ina sonka kum wlh iya abinda ka gani ne kawai babu abunda ya shiga tsakaninmu banda wasannin daka gani".
Yanda take magana ya tuna masa da kansa sai dai a maimakon nadamar daya gani tattare da ita shi a lokacin cikin izza da nuna isa yake nasa bayanin. Dama tun ranar daya fahimci shine wanda ya gani tareda Jalilah jikinsa ya bashi hatta da auren Fadila shirinta ne, ashe ba Fadila kaɗai ba harda matarsa cikin tarkon nata wannan ne abinda take zata masa da har ya mutu ba zai taɓa mantawa ba kenan gashi kuwa tayi nasara domin har ta mutu ba zai taɓa goge wannan mugun ganin daga idanuwansa ba kamar yanda ya barwa Halima tunani mafi muni irin wannan akansa. Wai ta yaya ma har Halima ta iya sake kallonsa da idanun rahma? Lallai ta cika jaruma. Haƙƙin ta ne, yaga sakayya tun a duniya yana fatan kuma ya zama iyaka hukuncinsa ba zai tafi lahira da haƙƙin Halima ba.
"Ki faɗa mun gaskiya kada ki ɓoye mun komai hakan ne zai saka na yarda dake ko akasin haka, bayan shi sai kuma wa kike kulawa" ya faɗa da ƙyar dan wani abu yaji ya tsaya masa a wuya shi bai fita ba kuma bai koma ciki ba.
"Wlh tun bayan da mukayi aure babu abinda ya haɗani da wani Namiji shi kaɗai ne kawai kum dole ya mun" ta faɗa cikin tsananin kuka, ya girgiza kai ya ce
"Halinki ne ba dole yayi miki ba Zulaiha. Na daɗe ina zargin haka amma a koda yaushe zuciyata tana cikin yi miki uzuri kwatankwacin uzurin da Halima ta ringa yi mun akan laifukana. Ki tafi gida ba zan sakeki ba domin idan na rabu dake akan laifin da nima na aikata bansan wace kalar jarabar ubangiji zai ƙara ɗora mun ba. Ki tafi kawai har zuwa lokacin da zan nemeki amma ina so wannan maganar ta zama sirri a tsakaninmu bana fatan wani ya jita.
MURFI
A ba zata saƙon ɗaurin aurena da Salman ya iskeni domin ko da ya samar mun a safiyar Juma'ar iyayensa zasu zo tambayar masa aurena kamar yanda Abba ya buƙata a wasa na ɗauki al'amarin, a lokacin da Mu'azzam ya shigo yayi kirana kawai na amsawa Baba Salahu cewa na amince a ɗaura mun aurene badan na yarda da gaske hakan ce zata faru ba sai dai amincewar da nayi ta zamo hukuncin da bana nadamar yinsa, kuma idan ana sake aure sau dubu toh tabbatas Salman zan zaɓa.
Ya zame mun Mijin, Aboki, Yayan da duk wani matsayi da wani ɗan adam yake iya takawa a rayuwa. Rayuwar auren dana ringa mafarki wacce ta zamemun Fantasy a gidan Bilal comes to reality bayan dana auri Salman. Ya gatatani, ya riritani, yan uwansa sun ƙaunace ni tamkar jininsu, har bayan shekaru goma da aurenmu daya ƙaro mun abokiyar zama domin ni ba kishiya aka yi mun ba na cigaba da kasancewa lamba ɗaya a duniyar Salman.
Na gasgata zancen Mama Fauziyya da tace akwai sanda za'a wayi gari na manta da Bilal tabbas hakan ta kasance domin sai da takai a wasu lokutan na kan manta da cewar ba Salman ne uban yarana biyu na farko ba saboda kyakkyawar alaƙar daya gina tsakaninsu bai taɓa banbantasu da yaya ukun dana haifa masa bayan su ba. Na godewa Allah na kuma godewa dalilin da yayi silar barina rayuwar da bani da gurbi a cikinta.
ALHAMDULILLAH
Daga Asibiti bayan an sallame su ya cewa Zulaiha ta wuce gida, shi da ita ne a ɗakin ta fashe da kuka haɗi da durƙushewa a gurin tana cewa
"Wlh tilastani yayi. Cewa yayi idan ban amince ba zasu mayar da kai gidan yari dan girman Allah kayi haƙuri karka sakeni ina sonka kum wlh iya abinda ka gani ne kawai babu abunda ya shiga tsakaninmu banda wasannin daka gani".
Yanda take magana ya tuna masa da kansa sai dai a maimakon nadamar daya gani tattare da ita shi a lokacin cikin izza da nuna isa yake nasa bayanin. Dama tun ranar daya fahimci shine wanda ya gani tareda Jalilah jikinsa ya bashi hatta da auren Fadila shirinta ne, ashe ba Fadila kaɗai ba harda matarsa cikin tarkon nata wannan ne abinda take zata masa da har ya mutu ba zai taɓa mantawa ba kenan gashi kuwa tayi nasara domin har ta mutu ba zai taɓa goge wannan mugun ganin daga idanuwansa ba kamar yanda ya barwa Halima tunani mafi muni irin wannan akansa. Wai ta yaya ma har Halima ta iya sake kallonsa da idanun rahma? Lallai ta cika jaruma. Haƙƙin ta ne, yaga sakayya tun a duniya yana fatan kuma ya zama iyaka hukuncinsa ba zai tafi lahira da haƙƙin Halima ba.
"Ki faɗa mun gaskiya kada ki ɓoye mun komai hakan ne zai saka na yarda dake ko akasin haka, bayan shi sai kuma wa kike kulawa" ya faɗa da ƙyar dan wani abu yaji ya tsaya masa a wuya shi bai fita ba kuma bai koma ciki ba.
"Wlh tun bayan da mukayi aure babu abinda ya haɗani da wani Namiji shi kaɗai ne kawai kum dole ya mun" ta faɗa cikin tsananin kuka, ya girgiza kai ya ce
"Halinki ne ba dole yayi miki ba Zulaiha. Na daɗe ina zargin haka amma a koda yaushe zuciyata tana cikin yi miki uzuri kwatankwacin uzurin da Halima ta ringa yi mun akan laifukana. Ki tafi gida ba zan sakeki ba domin idan na rabu dake akan laifin da nima na aikata bansan wace kalar jarabar ubangiji zai ƙara ɗora mun ba. Ki tafi kawai har zuwa lokacin da zan nemeki amma ina so wannan maganar ta zama sirri a tsakaninmu bana fatan wani ya jita.
MURFI
A ba zata saƙon ɗaurin aurena da Salman ya iskeni domin ko da ya samar mun a safiyar Juma'ar iyayensa zasu zo tambayar masa aurena kamar yanda Abba ya buƙata a wasa na ɗauki al'amarin, a lokacin da Mu'azzam ya shigo yayi kirana kawai na amsawa Baba Salahu cewa na amince a ɗaura mun aurene badan na yarda da gaske hakan ce zata faru ba sai dai amincewar da nayi ta zamo hukuncin da bana nadamar yinsa, kuma idan ana sake aure sau dubu toh tabbatas Salman zan zaɓa.
Ya zame mun Mijin, Aboki, Yayan da duk wani matsayi da wani ɗan adam yake iya takawa a rayuwa. Rayuwar auren dana ringa mafarki wacce ta zamemun Fantasy a gidan Bilal comes to reality bayan dana auri Salman. Ya gatatani, ya riritani, yan uwansa sun ƙaunace ni tamkar jininsu, har bayan shekaru goma da aurenmu daya ƙaro mun abokiyar zama domin ni ba kishiya aka yi mun ba na cigaba da kasancewa lamba ɗaya a duniyar Salman.
Na gasgata zancen Mama Fauziyya da tace akwai sanda za'a wayi gari na manta da Bilal tabbas hakan ta kasance domin sai da takai a wasu lokutan na kan manta da cewar ba Salman ne uban yarana biyu na farko ba saboda kyakkyawar alaƙar daya gina tsakaninsu bai taɓa banbantasu da yaya ukun dana haifa masa bayan su ba. Na godewa Allah na kuma godewa dalilin da yayi silar barina rayuwar da bani da gurbi a cikinta.
ALHAMDULILLAH