Sashe 98
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai na girgiza masa alamar Aa, ya sake cewa
"Eh mana, Tunaninki kenan saboda har yanzu ƙwaƙwalwarki bata hasko miki illar rayuwar da kike ciki ba. Halima babu iyayen da zasu so yar su tayi aure ta dawo sai dai idan abun yafi ƙarfin su domin burin kowanne iyaye ne yayansu suyi aure a inda zasu rayu cikin aminci da walwala da kuma mutuntaka wanda gaba ɗaya kika rasa. Ko wanda bai sanki ba kuka haɗu a hanya ya kalle ki in dai maganar nutsuwa akeyi ta bayyana ƙarara baki da ita. Ko shekara talatin baki cika ba kin ɗorawa kanki hawan jini harda kumburin zuciya akan namijin da kina raye ma ya wofantar dake ya auri wata balle kuma ki kashe kanki saboda dashi bana zaton ko a addu'a zai ringa tunaki.
Ba shawara nazo baki ba, kamar yanda na tsaya tsayin daka na haɗa ki da shi haka yanzu nake so ki rama mun nima ki faranta mun zuciya ta hanyar rabuwa dashi. Da na so na kira shi da kaina ya bani takardar sakin sai dai kuma na tuna bani da sauran mutunchi a idon sa ko na kira shi ma ba zuwa zai yi ba tunda mun sha haɗuwa a ƙofar gidana ma ya kalle ni na kalle shi ya wuce ba tareda ko ci kanka ya ce mun ba balle kuma in ɗaga waya na kirashi ai sai abunda kuma na gani. Dan haka ko ki kirashi ko ma duk ta yanda kika san saƙo zai fi saurin isa ki gaya masa kada ki kurkura satin nan ya ƙare kina cigaba da amsa sunan matar sa a cikin gidan nan".
Tunda ya fara maganar kuka na ya tsaya tsak, yanda kasan zuciyata zatayi tsalle ta fito haka naji sanda ya ce wai Bilal ya rubuto takardar saki ya kawo mun, ganin ya miƙe tsaye alamar ya gama magana daƙyar na lalubo yawu na jiƙa maƙoshi na kafin na samu na fizgo maganar data tsaya mun a wuya na ce
"Abba amma da wasa kake yi?" Murmushin takaici yayi kafin ya ce
"Dama ina wasa dake ne Halima?" Daga haka ya saka kai ya fita ba tareda ya sake ce mun komai ba.
Zumbur na miƙe kamar wacce aka tsikarawa Allura na shiga zagaye ɗakin ina nanata Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, nayi zagaye ya kai hamsin kafin na zube gefen gado lokaci ɗaya na fashe da kukan rashin mafita. Ya Abba zaiyi mun haka? Na ɗauki tsayin lokaci ina kukan kafin na fahimci hakan ba zai sama mun mafita ba, falo na fito, Mama, Mu'azzam da Imam suna zaune gabansu ƙaton tray da gasasshen kifi suna ci suna hira cikin nishaɗi irin su basu da wata matsala a rayuwarsu. A gaban Maman na zube na kama guiwarta lokaci ɗaya na fashe da kuka har jikina yana jijjiga tsabar yanda nake janyo kukan tun daga can ƙasan raina, ta sauke Sharifa daga kan cinyarta jiki na tsuma itama ta kamoni tana cewa
"Menene?" Ban iya ce mata komai ba in banda kukan dana ƙara ta hanyar ɗaga murya, Mu'azzam ya ce
"Wlh sai Allah ya saka mata wannan faɗuwar gaban da kike sakata, banda tsabar iskanci kawai idan kika bushi iska sai ki hau kuka duk ki ɗagawa mutane hankali ke ko shekarunsu bakya dubawa? Ai gasu nan kema kin haifa idan da daɗi abinda kikeyi zaki ji wata rana" yayi tsaki ya miƙe zai bar gurin dai dai nan Abba ya shigo falon, ban yarda na kalle shi ba ina jin sa yana cewa Mu'azzam ɗin
"In sha Allahu yaranta ba zasu mata haka ba ita ma ɗin da takeyi mun yafe". Ya ƙarasa ya zauna kan kujera ban saki Mama ba haka ban daina kukan ba sai da ya daka mun tsawar da tunda nake ban taɓa jin ko wani can a waje yayiwa ba balle mu ɗin, cikin tsawa yace
"Saketa ki tashi daga nan sakaryar banza kawai wacce bata san ciwon kanta ba" ba shiri na saketa na mataa gefe na haɗe kai da guiwa kamar marainiya na cigaba da kuka, Mama ta ce
"Wai me ya faru ne Abba wlh duk ta tsinkar mun da zuciya".
"Saboda na ce ta karɓo takardar sakinta gurin wancan yaron ko?" Ya bata amsa, sai ta dafe ƙirji ta ce
"Kai wa ya aike ka?" Ya bita da kallon mamaki da kuma rashin fahimta sai ta ce
"So kake ta saka ka a bakin duniya tace kai ka kashe mata aure? Ai da kayi shawara dani da baka fara wannan ɗanyan aikin ba". Tsaki yayi ya miƙe yana cewa
"Ni dai na faɗa mata, kuma dama gobe in Allah ya kaimu ta wuce ta karɓo posting letter ta idan ba haka ba wlh Halima zakiga other side of me wanda baki sani ba tunda naga alamar sako sakon da ake miki ya saka yanda kika mayar da kanki shashasha kowa ma kike so ki mayar dashi haka" ya wuce ɓangarensa. Mama ma miƙewa tayi bayan da tace
"Allah ya rufa asiri toh" Imam ko yanda ka san baya falon kifin sa kawai yake ci yana bawa Sharifa, da yaga kukana zai cika masa kunne ma remote ya ɗauka ya ƙara volume ɗin Tv, haka na ja jiki na sake komawa ɗaki na cigaba da kuka kamar wacce aka ce za'a fillewa kai gobe. Sai da na gaji kafin nayi shiru ina jan ajiya zuciya, ciwon da kaina yake mun kuwa ba zai mislatu ba har wani ɗin ɗin nake jin ƙara kamar ta agogo a cikin kan nawa.
Dare ya tsala kowanne mai rai dake da nutsuwar zuciya yana kwance yana bacci amma banda ni ina dai kwance akan gadon ina juyi daga wannan kusurwa zuwa waccen na gagara bacci haka nan ƙwaƙwalwata ta kasa bani haɗin kan da zanyi tunani mai ma'ana da zai sama mun da mafita gashi, da ina da tsarki ne ma sai inyi sallah ko zan samu nutsuwa. Ina tunanin firgici ne ya matso mun da period dan a lissafi sai nan da kusan kwana huɗu zai zo amma ɗazu ina shiga banɗaki na ganshi.
Bansan me zanyi ba, umarnin Abba yayi mun tsauri, dukda cewar ni a karon kaina har yanzun ban yanke shawara dangane da yuwuwar cigaba ko ƙarewar zamana da Bilal ba na bar hakan ne tukunna har sai ni da shi mun zauna munyi magana ta gaskiya daga nan ne zan yanke hukunci akan abinda ya kamata nayi amma shi Abba kai tsaye ya yanke nasa hukuncin yanzu yaya ake so nayi?
Idan kuma ya zama duk abinda Hafiz ɗin ya faɗa ƙarya ne ko ma duk abinda ya faru tsakaninsa da Jalilan setup ne fa tunda ai da bakinsa ya ce basu san ya sani ba toh ta ina ya sani kenan bibiyarsu yakeyi idan kuma haka ne dama akwai abinda yake so ya cimma shiyasa har yake binsu kenan?
"Amma kuma wace riba zai ci idan yayi hakan?" Ni da kaina na jefawa kaina tambayar da bani da amsarta. A zahirance ma bani da wata hujja da zan jefa masa kowanne irin zargi domin Bilal bashi da wani abu da har zai saka mutum irin Hafiz yayi framing nasa. Kuma ko da ace da gaske shirin ne idan dama ba halin sa bane ko yana so ai babu yanda za'ayi ya biye mata tunda babu inda naga alamar ta masa dole a cikin hirar su duk ba wannan bama ai da ba zai haɗa ta da danginsa ba har tazo duba mahaifiyarsa da bata da lafiya.
"Ta yuwu ma ita ya aura tunda tana da kyau kuma tana da kuɗi dama kuma ai ya ce shi baya tarayya da mutumin da ba zai ƙaru da shi ba" na faɗa a fili. Sababbin hawaye ne suka ɓalle mun na koma na kwanta ina jin ƙuna a ƙirji na, na ringa tuna fuskarta haɗuwar mu a asibiti fara kyakkyawa mai diri duk hassadar mutum bai isa ya kushe halittarta ba. Ji na ringayi tamkar numfashi na zai tsaya har saida na tashi zaune, abunda na tabbatar shi ake kira da kishi ya turnuƙeni, lokaci ɗaya kuma hotunan waccen ranar suka shafe na kyakkyawar fuskar Jalilah da nake gani, muryoyin da sukayi musaya suka shiga mun amsa kuwwa a kunne, hannu biyu na saka na toshe kunnuwana na fashe da kuka mai sauti.
BILAL
Hankalinsa ya kwanta yanzu saboda ya samu nutsuwa akan kokonton dake neman hargitsa masa lissafi akan Zulaiha. Dukda dama zuciyarsa bata yarda zai samu akasin abinda yake tsammani daga Zukaihan ba sai dai canjin halayyarta na lokaci guda ne ya bashi tsoro, amma zuwan da yayi jiyan da hirar da sukayi ya kwantar masa da hankali dan har haƙuri ta bashi sosai kamar zatayi kuka akan ɗaga masa muryar da tayi a waya. Sun daɗe suna hira sosai irin yanda suka saba, da zai tafi ya shiga suka gaisa da Ummansu, har ya miƙe ta dakatar dashi tana cewa
"Dama yan uwana ne sukayi magana akan suna so suje ganin gurin da zata zauna". Kansa na ƙasa dan bala'in kunyarta yakeji har mamaki yake yanda bayajin nauyin Mamansu Halima irin yanda yakejin ma Umman Zulaihan.
"Dama zuwa wani satin nake so idan an ƙarasa gyaran gurin nayi magana je a gani" ya bata amsa, ta muskuta tana gyara hijabinta tace
"Toh madallah, kasan da yake sune jikokin ya mace na farko ni a gidanmu da za'a fara aurarwa duk yayyena matan yayayensu maza ne shine fa kowa hankalinsa yana kan bikin nan, ga zancen kawo lefe ma kasan abunka da masu ƙaramin ƙarfi sai anyi tanadi ya kamata idan za'a zo afaɗa da wuri saboda a tanadi abun tarbar baƙi, su dai na Nuratu sun ce Asabar ta sama nan da sati biyu kenan da kawo lefen da tariya duk rana ɗaya dan ya ɗauke ta ma sunje gurin tela an gwadata a ɗinke zasu kawo abunsu. To itan ma ya kamata kaga mu sani in kuma kuɗin za'a bayar ma duk kaga sai a san shirin da ake ciki" ta ƙarasa tana sosa kai kamar wata mara gaskiya.
"Eh mana, Tunaninki kenan saboda har yanzu ƙwaƙwalwarki bata hasko miki illar rayuwar da kike ciki ba. Halima babu iyayen da zasu so yar su tayi aure ta dawo sai dai idan abun yafi ƙarfin su domin burin kowanne iyaye ne yayansu suyi aure a inda zasu rayu cikin aminci da walwala da kuma mutuntaka wanda gaba ɗaya kika rasa. Ko wanda bai sanki ba kuka haɗu a hanya ya kalle ki in dai maganar nutsuwa akeyi ta bayyana ƙarara baki da ita. Ko shekara talatin baki cika ba kin ɗorawa kanki hawan jini harda kumburin zuciya akan namijin da kina raye ma ya wofantar dake ya auri wata balle kuma ki kashe kanki saboda dashi bana zaton ko a addu'a zai ringa tunaki.
Ba shawara nazo baki ba, kamar yanda na tsaya tsayin daka na haɗa ki da shi haka yanzu nake so ki rama mun nima ki faranta mun zuciya ta hanyar rabuwa dashi. Da na so na kira shi da kaina ya bani takardar sakin sai dai kuma na tuna bani da sauran mutunchi a idon sa ko na kira shi ma ba zuwa zai yi ba tunda mun sha haɗuwa a ƙofar gidana ma ya kalle ni na kalle shi ya wuce ba tareda ko ci kanka ya ce mun ba balle kuma in ɗaga waya na kirashi ai sai abunda kuma na gani. Dan haka ko ki kirashi ko ma duk ta yanda kika san saƙo zai fi saurin isa ki gaya masa kada ki kurkura satin nan ya ƙare kina cigaba da amsa sunan matar sa a cikin gidan nan".
Tunda ya fara maganar kuka na ya tsaya tsak, yanda kasan zuciyata zatayi tsalle ta fito haka naji sanda ya ce wai Bilal ya rubuto takardar saki ya kawo mun, ganin ya miƙe tsaye alamar ya gama magana daƙyar na lalubo yawu na jiƙa maƙoshi na kafin na samu na fizgo maganar data tsaya mun a wuya na ce
"Abba amma da wasa kake yi?" Murmushin takaici yayi kafin ya ce
"Dama ina wasa dake ne Halima?" Daga haka ya saka kai ya fita ba tareda ya sake ce mun komai ba.
Zumbur na miƙe kamar wacce aka tsikarawa Allura na shiga zagaye ɗakin ina nanata Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, nayi zagaye ya kai hamsin kafin na zube gefen gado lokaci ɗaya na fashe da kukan rashin mafita. Ya Abba zaiyi mun haka? Na ɗauki tsayin lokaci ina kukan kafin na fahimci hakan ba zai sama mun mafita ba, falo na fito, Mama, Mu'azzam da Imam suna zaune gabansu ƙaton tray da gasasshen kifi suna ci suna hira cikin nishaɗi irin su basu da wata matsala a rayuwarsu. A gaban Maman na zube na kama guiwarta lokaci ɗaya na fashe da kuka har jikina yana jijjiga tsabar yanda nake janyo kukan tun daga can ƙasan raina, ta sauke Sharifa daga kan cinyarta jiki na tsuma itama ta kamoni tana cewa
"Menene?" Ban iya ce mata komai ba in banda kukan dana ƙara ta hanyar ɗaga murya, Mu'azzam ya ce
"Wlh sai Allah ya saka mata wannan faɗuwar gaban da kike sakata, banda tsabar iskanci kawai idan kika bushi iska sai ki hau kuka duk ki ɗagawa mutane hankali ke ko shekarunsu bakya dubawa? Ai gasu nan kema kin haifa idan da daɗi abinda kikeyi zaki ji wata rana" yayi tsaki ya miƙe zai bar gurin dai dai nan Abba ya shigo falon, ban yarda na kalle shi ba ina jin sa yana cewa Mu'azzam ɗin
"In sha Allahu yaranta ba zasu mata haka ba ita ma ɗin da takeyi mun yafe". Ya ƙarasa ya zauna kan kujera ban saki Mama ba haka ban daina kukan ba sai da ya daka mun tsawar da tunda nake ban taɓa jin ko wani can a waje yayiwa ba balle mu ɗin, cikin tsawa yace
"Saketa ki tashi daga nan sakaryar banza kawai wacce bata san ciwon kanta ba" ba shiri na saketa na mataa gefe na haɗe kai da guiwa kamar marainiya na cigaba da kuka, Mama ta ce
"Wai me ya faru ne Abba wlh duk ta tsinkar mun da zuciya".
"Saboda na ce ta karɓo takardar sakinta gurin wancan yaron ko?" Ya bata amsa, sai ta dafe ƙirji ta ce
"Kai wa ya aike ka?" Ya bita da kallon mamaki da kuma rashin fahimta sai ta ce
"So kake ta saka ka a bakin duniya tace kai ka kashe mata aure? Ai da kayi shawara dani da baka fara wannan ɗanyan aikin ba". Tsaki yayi ya miƙe yana cewa
"Ni dai na faɗa mata, kuma dama gobe in Allah ya kaimu ta wuce ta karɓo posting letter ta idan ba haka ba wlh Halima zakiga other side of me wanda baki sani ba tunda naga alamar sako sakon da ake miki ya saka yanda kika mayar da kanki shashasha kowa ma kike so ki mayar dashi haka" ya wuce ɓangarensa. Mama ma miƙewa tayi bayan da tace
"Allah ya rufa asiri toh" Imam ko yanda ka san baya falon kifin sa kawai yake ci yana bawa Sharifa, da yaga kukana zai cika masa kunne ma remote ya ɗauka ya ƙara volume ɗin Tv, haka na ja jiki na sake komawa ɗaki na cigaba da kuka kamar wacce aka ce za'a fillewa kai gobe. Sai da na gaji kafin nayi shiru ina jan ajiya zuciya, ciwon da kaina yake mun kuwa ba zai mislatu ba har wani ɗin ɗin nake jin ƙara kamar ta agogo a cikin kan nawa.
Dare ya tsala kowanne mai rai dake da nutsuwar zuciya yana kwance yana bacci amma banda ni ina dai kwance akan gadon ina juyi daga wannan kusurwa zuwa waccen na gagara bacci haka nan ƙwaƙwalwata ta kasa bani haɗin kan da zanyi tunani mai ma'ana da zai sama mun da mafita gashi, da ina da tsarki ne ma sai inyi sallah ko zan samu nutsuwa. Ina tunanin firgici ne ya matso mun da period dan a lissafi sai nan da kusan kwana huɗu zai zo amma ɗazu ina shiga banɗaki na ganshi.
Bansan me zanyi ba, umarnin Abba yayi mun tsauri, dukda cewar ni a karon kaina har yanzun ban yanke shawara dangane da yuwuwar cigaba ko ƙarewar zamana da Bilal ba na bar hakan ne tukunna har sai ni da shi mun zauna munyi magana ta gaskiya daga nan ne zan yanke hukunci akan abinda ya kamata nayi amma shi Abba kai tsaye ya yanke nasa hukuncin yanzu yaya ake so nayi?
Idan kuma ya zama duk abinda Hafiz ɗin ya faɗa ƙarya ne ko ma duk abinda ya faru tsakaninsa da Jalilan setup ne fa tunda ai da bakinsa ya ce basu san ya sani ba toh ta ina ya sani kenan bibiyarsu yakeyi idan kuma haka ne dama akwai abinda yake so ya cimma shiyasa har yake binsu kenan?
"Amma kuma wace riba zai ci idan yayi hakan?" Ni da kaina na jefawa kaina tambayar da bani da amsarta. A zahirance ma bani da wata hujja da zan jefa masa kowanne irin zargi domin Bilal bashi da wani abu da har zai saka mutum irin Hafiz yayi framing nasa. Kuma ko da ace da gaske shirin ne idan dama ba halin sa bane ko yana so ai babu yanda za'ayi ya biye mata tunda babu inda naga alamar ta masa dole a cikin hirar su duk ba wannan bama ai da ba zai haɗa ta da danginsa ba har tazo duba mahaifiyarsa da bata da lafiya.
"Ta yuwu ma ita ya aura tunda tana da kyau kuma tana da kuɗi dama kuma ai ya ce shi baya tarayya da mutumin da ba zai ƙaru da shi ba" na faɗa a fili. Sababbin hawaye ne suka ɓalle mun na koma na kwanta ina jin ƙuna a ƙirji na, na ringa tuna fuskarta haɗuwar mu a asibiti fara kyakkyawa mai diri duk hassadar mutum bai isa ya kushe halittarta ba. Ji na ringayi tamkar numfashi na zai tsaya har saida na tashi zaune, abunda na tabbatar shi ake kira da kishi ya turnuƙeni, lokaci ɗaya kuma hotunan waccen ranar suka shafe na kyakkyawar fuskar Jalilah da nake gani, muryoyin da sukayi musaya suka shiga mun amsa kuwwa a kunne, hannu biyu na saka na toshe kunnuwana na fashe da kuka mai sauti.
BILAL
Hankalinsa ya kwanta yanzu saboda ya samu nutsuwa akan kokonton dake neman hargitsa masa lissafi akan Zulaiha. Dukda dama zuciyarsa bata yarda zai samu akasin abinda yake tsammani daga Zukaihan ba sai dai canjin halayyarta na lokaci guda ne ya bashi tsoro, amma zuwan da yayi jiyan da hirar da sukayi ya kwantar masa da hankali dan har haƙuri ta bashi sosai kamar zatayi kuka akan ɗaga masa muryar da tayi a waya. Sun daɗe suna hira sosai irin yanda suka saba, da zai tafi ya shiga suka gaisa da Ummansu, har ya miƙe ta dakatar dashi tana cewa
"Dama yan uwana ne sukayi magana akan suna so suje ganin gurin da zata zauna". Kansa na ƙasa dan bala'in kunyarta yakeji har mamaki yake yanda bayajin nauyin Mamansu Halima irin yanda yakejin ma Umman Zulaihan.
"Dama zuwa wani satin nake so idan an ƙarasa gyaran gurin nayi magana je a gani" ya bata amsa, ta muskuta tana gyara hijabinta tace
"Toh madallah, kasan da yake sune jikokin ya mace na farko ni a gidanmu da za'a fara aurarwa duk yayyena matan yayayensu maza ne shine fa kowa hankalinsa yana kan bikin nan, ga zancen kawo lefe ma kasan abunka da masu ƙaramin ƙarfi sai anyi tanadi ya kamata idan za'a zo afaɗa da wuri saboda a tanadi abun tarbar baƙi, su dai na Nuratu sun ce Asabar ta sama nan da sati biyu kenan da kawo lefen da tariya duk rana ɗaya dan ya ɗauke ta ma sunje gurin tela an gwadata a ɗinke zasu kawo abunsu. To itan ma ya kamata kaga mu sani in kuma kuɗin za'a bayar ma duk kaga sai a san shirin da ake ciki" ta ƙarasa tana sosa kai kamar wata mara gaskiya.