Sashe 149
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shikenan na yarda, toh ya kike ya dare?" Ya faɗa daga haka muka shiga hira wacce zancen tafiyarsa gobe ne. Dama shi hirarsa kenan aiki da sabgoginsa na rayuwar yau da kullum ni kuma sai dai nayita binsa da Eh ko Aa dan a gurina wannan ba hira bace, a matsayinsa na mai neman gurin zama a ganina ya kamata hirar sa ta kasance ta ƙoƙarin kafa kansa a gurina amma shi sam ba haka yake ba. Sha biyu na bugawa yayi mun sallama, kashe wayar nayi gaba ɗaya dan tun muna magana nake ta jin shigowar kiran Bilal.
Tunanin fara maganarmu da Dr Salman na tafi, washe garin ranar da muka haɗu dashi a gidan Uncle Mudassir mun fita tareda su Al'amin da yamma siyo Popsicles muka haɗu dashi a gurin. Har ga Allah ban so kulashi ba dukda mun haɗa ido musamman da na ganshi tareda wata mace da wani abokinsa ina tsaye gurin biyan kuɗi ya tarar dani sai jin muryarsa nayi a bayana yana cewa
"Barka da yamma Malama Leemah". Da farko dukda naga tsayuwarsa ban ɗauka dani yake ba musamman sunan daya kira wai Leemah dan haka ban amsa ba, sai da ya sake matsoni sosai yana kallona ya maimaita maganar kafin kuma kunya ta kamani na shiga gaishe shi kai a ƙasa. Shi ya biya kuɗin abinda muka siya ya rakamu har mota kawai ya miƙa mun wayarsa wai na saka masa number na. Haka na koma gida cike da mamakinsa bai kirani ba sai washe gari Monday lokacin mun fita break, tsarin number dama gani kawai jikina ya bani shine, ilai kuwa bayan na amsa yace naje na sameshi a office, tareda Uncle Mudassir na tarar dasu babu kuma jeka ka dawo a gaban Uncle Mudassir ɗin ya ce wai nayi masa tun ranar daya fara ganina a lokacin ma bai san nice Niece ɗin Mudassir ba kawai yaji yana so na dagaske kuma idan na amince aurena yake so yayi.
Uncle Mudassir yace masa babu ruwansa shima yace bai sakashi a ciki ba abinda ya saka ya faɗa a gabansa kawai saboda ya san dagaske yakeyi koda yaji labarin wani zai masa shige ya faɗa cewar yana ciki, ni dai na tafi na barsu kawai, shikenan ya fara kirana a waya, ban kuma ɓoye masa ba na faɗa masa na taɓa aure har ina da yara biyu, nayi mamakin jin wai bai sani ba dan na faɗa masa ne saboda ya ji daga bakina dukda ina da yaƙinin ya sani Uncle Mudassir ba zai ƙi ya gaya masa ba amma yace mun bai sani ba.
"Bakiyi kama da wacce ta taɓa aure ba har kuma ace kin haifi yara biyu amma ke nake so, aure ko haihuwa ba zasu canza hakan ba" abinda ya faɗa mun kenan. Soyayyar sa a bayyane take kuma da zafi yake yinta.
Dukda cewar baya faɗarta da baki amma a bayyane take a duk ayyukansa ba kuma ya shakka ko jin nauyin wani ya sani kamar yanda nake jin tsoron fallasuwar alaƙarmu a office ɗin, ya mutane zasu kalli abun ace daga zuwansa kawai soyayya ta ƙullu tsakaninmu? Ba yan office ba hatta da mutanen gidanmu bana bana so maganar ta fita su ji ban kuma san dalilin haka ba.
Ban sani ba ko kulawar da yake bani ce ta saka zuciyata ƙoƙarin kware masa, yanda yake mun idan yana tareda ni yana sakani ina jina tamkar sarauniya, abu ɗaya ne cikas ɗin, baya mun kalaman soyayya irin waɗanda kunnuwana suke da muradin sauraro, amma dukda hakan zan gwada.
HAJJA.
Cikin yanayin damuwa ta kalli su Anty Amina tace
"Kunji wai bata da lambar sai dai a tambayi Nasir"
"Toh ki kira Nasir ɗin aji, ni bari na wuce duk yanda zake ciki sai muyi waya" Amina ta sake faɗa tana miƙewa daga haka tayi musu sallama Anty Habiba ma ta miƙe suka bar Hajjan ita kaɗai.
Abubakar ta kira tace ya kirawo mata Nasir ɗin a waya,
"Kana kallo duk sunyi tafiyarsu kamar ma halin da ɗanuwanku yake ciki bai damesu ba" ta faɗawa Abubakar. Yana danna waya ya ce mata
"Toh Hajja me kike so suyi? Shi fa ya jefa kansa a koma menene idan sun zauna mai hakan zai canza?"
"Amma ai sa ɗebe mun kewa su kwantar mun da hankali ko?" Ta sake faɗa, ya miƙa mata waya ganin Nasir ya amsa kiran ya fice ba tareda ya sake cewa komai ba. Nasir ɗin ma kamar Halima ce mata yayi ya kwana biyu rabonsa da Bilal yana ta kiran layukansa kuma baya samu sai da yaje can gidan matarsa tace ai yayi tafiya. Ya ce mata
"Na san dai kin san mai yake faruwa Hajja, ki faɗa masa duk ma inda ya tafi ya dawo dan wannan ba mafita bace gara yazo kawai ayi abunda za'ayi asiri ya rufu".
"Wai har dubu nawa ne kuɗin da zai saka ya gudu?" Hajja ta tambayi Abubakar bayan data gama wayar, ya watsa hannu kafin ya ce
"Ni ban sani ba Hajja idan ya dawo sai ki tambayeshi"
"Ai shikenan" Hajjan ta faɗa kamar abar tausayi, har ya miƙe sai kuma ya koma ya zauna ganin tayi tagumi lokaci ɗaya fuskarta harta wani rame damuwa ta cikata.
WASHE GARI
HALIMA
Ƙarar waya ta ce ta tayar dani daga baccin da ban jima da komawa ba dan tun asuba bayan na idar da sallah Dr Salman ya kirani bai kuma barni ba har sai da aka fara sanarwar jirginsu zai tashi zuwa Abuja wayar sama da awa biyu kunnuwana har ciwo naji suna neman kamawa daga ƙarshe a speaker na sakata na kwanta ina amsa shi da Eh da Aa. Ban jima da komawa baccin ba aka sake kira, na tashi zaune daƙyar, har wani yaji-yaji kaina yake mun, na ɗaga nayi sallama cikin muryar bacci, sai daya amsa sannan na fahimci wanene mai kiran dan banga sunan da kyau ba.
"Na tashe ki daga bacci Anty Halima na ɗauka ai kina gurin aiki ma" ya faɗa, nace
"Yau banida aiki shiyasa" daga haka muka gaisa ya ɗan yi jimm kafin ya ce
"Jiya Hajja ta kiraki ko?"
"Eh ta kira tana tambayar ko ina da wata number Abbansu Al'amin" na bashi amsa, ya sakeyin shiru kafin ya ce
"Na san ko ba zai kira kowa ba zai kiraki ta yuwu ma ya faɗa miki in da yake, dan Allah ki bani number da ake samunsa Anty Halima idan kuma ba haka ba nazo ki kirashi sai ki haɗa mu a wayarki"
"Ni bamuyi magana dashi ba amma akwai wata number sa da nake tunanin zaka iya samunsa a ita bari na tura maka". Sallama mukayi na aika masa da number kafin na kashe wayata na koma bacci.
Abubakar kuwa tana tura masa number ya dannawa Bilal kira, sau uku ya kira bai amsa ba sai ya tura masa message cewar Hajja tana kwance a Asibiti kuma tace a kirawo mata shi dan jikin yayi tsanani ya zo idan ba yana so ya mutu da nadamar ƙin zuwan ba.
Yana turawa ya kashe wayarsa ya tafi uzurinsa, ya sani Bilal ɗin yana girmama lamarin Hajja da wahala kuma ya share alhalin an ce tana kwance a gadon Asibiti.
Tunaninsa kuwa ya zama gaskiya dan lokacin daya kirashi yana zaune yana karyawa ne kuma cikin shiri yake dan yana so yaje gurin Yusuf da yake ta kira tun daren jiya baya ɗauka bayan sunyi magana ya gaya masa an sauke kaya ya sauraresu a kowanne lokaci zai iya jin alert tunda sun karɓi details ɗin sa da komai dama, yana ganin kiran Abubakar ya san tabbas Halima ce ta bashi number.
Niyyar kashe wayar yayi gaba ɗaya ganin yana ta kira sai ga saƙonsa ya shigo take kuwa hankalinsa ya tashi ba shiri ya kama hanyar Kano. Yana tafe a hanya yana sake gwada kiran Yusuf ɗin shiru har sannan tana ringing amma ba'a ɗauka, yana guraren Yankaba ya same shi, haƙuri ya bashi wai wayar ce yara suka saka masa a silent bai lura ba sai yanzu daya ɗakkota yaga tarin missed calls yace ya sameshi a office yanzu dan haka ya karya akalar motar daga hanyar asibitin da suke zuwa in da yayi tunanin an kai Hajja zuwa gurin Yusuf ɗin.
Ji ya ringayi kamar ana jijjigashi tsakanin sama da ƙasa, dukda sanyin Ac daya cika office ɗin amma zufa ta shiga keto masa ya ringa kallon Yusuf ɗin yana sake kallon Tablet ɗin daya kunna masa video.
"Kayi haƙuri Alhaji Bilal, shiyasa na ringa maka magana akan ka rage yawan kuɗin nan amma kaƙi ji, yanzu ka shiga harkar nan mu mun daɗe da yin wayo a cikinta. Yanda ake samun riba kamar hauka haka idan Allah ya juyo abun asara ta afku nan ma sai kaji kamar zaka haukace amma kuma idan ka tuna a baya Allah ya baka dan ya jarabceka yanzu dole kayi haƙuri. Toh yanzu ma haƙurin zakayi mu kumayi addu'ar Allah ya kawo ninkinsu a gaba, amma gaskiya nafi zargin canza kayan nan sukayi dan irin packing ɗin da akayi da wahala ace wai ruwa ne ya tarar dasu har yayi wannan ɓarnar sai dai idan dama can lalatattun ne" Alhaji Yusuf ya faɗa yana dafa kafaɗarsa.
Cike da ƙarfin hali kawai Bilal yake ɗaga masa kai, gaba ɗaya basu fi buhu goma sha zuwa ashirin bane aka buɗe su lafiya lau sauran komai ya lalace ba ga Zoɓon ba ba cittar ba sun yi funfuna cittar kuwa da yawan buhunhunan har ta siƙe kamar yanda sukace ta zama kamar ƙurar katako.
"Kaga lissafin iya abinda aka samu nan, sai ka sake turawa da Abu Amar details ɗin sai ku ƙarasa magana, yanzu bari naje ana jirana idan kuma yanzu zaka wuce sai mu tafi tare ka saukeni dan ba da mota na fito ba" Alhaji Yusuf ɗin ya sake faɗa, yanda yake magana ba zaka ɗauka da wanda ya tafka asarar Miliyoyin kuɗaɗe yakeyi ba kamar ma ba komai. Da laluben bango Bilal ya fita daga office ɗin, Yusuf ɗin ne yaja motar dan ce masa yayi baya gani sosai ya taimaka ya kaishi gida kawai.
Tunanin fara maganarmu da Dr Salman na tafi, washe garin ranar da muka haɗu dashi a gidan Uncle Mudassir mun fita tareda su Al'amin da yamma siyo Popsicles muka haɗu dashi a gurin. Har ga Allah ban so kulashi ba dukda mun haɗa ido musamman da na ganshi tareda wata mace da wani abokinsa ina tsaye gurin biyan kuɗi ya tarar dani sai jin muryarsa nayi a bayana yana cewa
"Barka da yamma Malama Leemah". Da farko dukda naga tsayuwarsa ban ɗauka dani yake ba musamman sunan daya kira wai Leemah dan haka ban amsa ba, sai da ya sake matsoni sosai yana kallona ya maimaita maganar kafin kuma kunya ta kamani na shiga gaishe shi kai a ƙasa. Shi ya biya kuɗin abinda muka siya ya rakamu har mota kawai ya miƙa mun wayarsa wai na saka masa number na. Haka na koma gida cike da mamakinsa bai kirani ba sai washe gari Monday lokacin mun fita break, tsarin number dama gani kawai jikina ya bani shine, ilai kuwa bayan na amsa yace naje na sameshi a office, tareda Uncle Mudassir na tarar dasu babu kuma jeka ka dawo a gaban Uncle Mudassir ɗin ya ce wai nayi masa tun ranar daya fara ganina a lokacin ma bai san nice Niece ɗin Mudassir ba kawai yaji yana so na dagaske kuma idan na amince aurena yake so yayi.
Uncle Mudassir yace masa babu ruwansa shima yace bai sakashi a ciki ba abinda ya saka ya faɗa a gabansa kawai saboda ya san dagaske yakeyi koda yaji labarin wani zai masa shige ya faɗa cewar yana ciki, ni dai na tafi na barsu kawai, shikenan ya fara kirana a waya, ban kuma ɓoye masa ba na faɗa masa na taɓa aure har ina da yara biyu, nayi mamakin jin wai bai sani ba dan na faɗa masa ne saboda ya ji daga bakina dukda ina da yaƙinin ya sani Uncle Mudassir ba zai ƙi ya gaya masa ba amma yace mun bai sani ba.
"Bakiyi kama da wacce ta taɓa aure ba har kuma ace kin haifi yara biyu amma ke nake so, aure ko haihuwa ba zasu canza hakan ba" abinda ya faɗa mun kenan. Soyayyar sa a bayyane take kuma da zafi yake yinta.
Dukda cewar baya faɗarta da baki amma a bayyane take a duk ayyukansa ba kuma ya shakka ko jin nauyin wani ya sani kamar yanda nake jin tsoron fallasuwar alaƙarmu a office ɗin, ya mutane zasu kalli abun ace daga zuwansa kawai soyayya ta ƙullu tsakaninmu? Ba yan office ba hatta da mutanen gidanmu bana bana so maganar ta fita su ji ban kuma san dalilin haka ba.
Ban sani ba ko kulawar da yake bani ce ta saka zuciyata ƙoƙarin kware masa, yanda yake mun idan yana tareda ni yana sakani ina jina tamkar sarauniya, abu ɗaya ne cikas ɗin, baya mun kalaman soyayya irin waɗanda kunnuwana suke da muradin sauraro, amma dukda hakan zan gwada.
HAJJA.
Cikin yanayin damuwa ta kalli su Anty Amina tace
"Kunji wai bata da lambar sai dai a tambayi Nasir"
"Toh ki kira Nasir ɗin aji, ni bari na wuce duk yanda zake ciki sai muyi waya" Amina ta sake faɗa tana miƙewa daga haka tayi musu sallama Anty Habiba ma ta miƙe suka bar Hajjan ita kaɗai.
Abubakar ta kira tace ya kirawo mata Nasir ɗin a waya,
"Kana kallo duk sunyi tafiyarsu kamar ma halin da ɗanuwanku yake ciki bai damesu ba" ta faɗawa Abubakar. Yana danna waya ya ce mata
"Toh Hajja me kike so suyi? Shi fa ya jefa kansa a koma menene idan sun zauna mai hakan zai canza?"
"Amma ai sa ɗebe mun kewa su kwantar mun da hankali ko?" Ta sake faɗa, ya miƙa mata waya ganin Nasir ya amsa kiran ya fice ba tareda ya sake cewa komai ba. Nasir ɗin ma kamar Halima ce mata yayi ya kwana biyu rabonsa da Bilal yana ta kiran layukansa kuma baya samu sai da yaje can gidan matarsa tace ai yayi tafiya. Ya ce mata
"Na san dai kin san mai yake faruwa Hajja, ki faɗa masa duk ma inda ya tafi ya dawo dan wannan ba mafita bace gara yazo kawai ayi abunda za'ayi asiri ya rufu".
"Wai har dubu nawa ne kuɗin da zai saka ya gudu?" Hajja ta tambayi Abubakar bayan data gama wayar, ya watsa hannu kafin ya ce
"Ni ban sani ba Hajja idan ya dawo sai ki tambayeshi"
"Ai shikenan" Hajjan ta faɗa kamar abar tausayi, har ya miƙe sai kuma ya koma ya zauna ganin tayi tagumi lokaci ɗaya fuskarta harta wani rame damuwa ta cikata.
WASHE GARI
HALIMA
Ƙarar waya ta ce ta tayar dani daga baccin da ban jima da komawa ba dan tun asuba bayan na idar da sallah Dr Salman ya kirani bai kuma barni ba har sai da aka fara sanarwar jirginsu zai tashi zuwa Abuja wayar sama da awa biyu kunnuwana har ciwo naji suna neman kamawa daga ƙarshe a speaker na sakata na kwanta ina amsa shi da Eh da Aa. Ban jima da komawa baccin ba aka sake kira, na tashi zaune daƙyar, har wani yaji-yaji kaina yake mun, na ɗaga nayi sallama cikin muryar bacci, sai daya amsa sannan na fahimci wanene mai kiran dan banga sunan da kyau ba.
"Na tashe ki daga bacci Anty Halima na ɗauka ai kina gurin aiki ma" ya faɗa, nace
"Yau banida aiki shiyasa" daga haka muka gaisa ya ɗan yi jimm kafin ya ce
"Jiya Hajja ta kiraki ko?"
"Eh ta kira tana tambayar ko ina da wata number Abbansu Al'amin" na bashi amsa, ya sakeyin shiru kafin ya ce
"Na san ko ba zai kira kowa ba zai kiraki ta yuwu ma ya faɗa miki in da yake, dan Allah ki bani number da ake samunsa Anty Halima idan kuma ba haka ba nazo ki kirashi sai ki haɗa mu a wayarki"
"Ni bamuyi magana dashi ba amma akwai wata number sa da nake tunanin zaka iya samunsa a ita bari na tura maka". Sallama mukayi na aika masa da number kafin na kashe wayata na koma bacci.
Abubakar kuwa tana tura masa number ya dannawa Bilal kira, sau uku ya kira bai amsa ba sai ya tura masa message cewar Hajja tana kwance a Asibiti kuma tace a kirawo mata shi dan jikin yayi tsanani ya zo idan ba yana so ya mutu da nadamar ƙin zuwan ba.
Yana turawa ya kashe wayarsa ya tafi uzurinsa, ya sani Bilal ɗin yana girmama lamarin Hajja da wahala kuma ya share alhalin an ce tana kwance a gadon Asibiti.
Tunaninsa kuwa ya zama gaskiya dan lokacin daya kirashi yana zaune yana karyawa ne kuma cikin shiri yake dan yana so yaje gurin Yusuf da yake ta kira tun daren jiya baya ɗauka bayan sunyi magana ya gaya masa an sauke kaya ya sauraresu a kowanne lokaci zai iya jin alert tunda sun karɓi details ɗin sa da komai dama, yana ganin kiran Abubakar ya san tabbas Halima ce ta bashi number.
Niyyar kashe wayar yayi gaba ɗaya ganin yana ta kira sai ga saƙonsa ya shigo take kuwa hankalinsa ya tashi ba shiri ya kama hanyar Kano. Yana tafe a hanya yana sake gwada kiran Yusuf ɗin shiru har sannan tana ringing amma ba'a ɗauka, yana guraren Yankaba ya same shi, haƙuri ya bashi wai wayar ce yara suka saka masa a silent bai lura ba sai yanzu daya ɗakkota yaga tarin missed calls yace ya sameshi a office yanzu dan haka ya karya akalar motar daga hanyar asibitin da suke zuwa in da yayi tunanin an kai Hajja zuwa gurin Yusuf ɗin.
Ji ya ringayi kamar ana jijjigashi tsakanin sama da ƙasa, dukda sanyin Ac daya cika office ɗin amma zufa ta shiga keto masa ya ringa kallon Yusuf ɗin yana sake kallon Tablet ɗin daya kunna masa video.
"Kayi haƙuri Alhaji Bilal, shiyasa na ringa maka magana akan ka rage yawan kuɗin nan amma kaƙi ji, yanzu ka shiga harkar nan mu mun daɗe da yin wayo a cikinta. Yanda ake samun riba kamar hauka haka idan Allah ya juyo abun asara ta afku nan ma sai kaji kamar zaka haukace amma kuma idan ka tuna a baya Allah ya baka dan ya jarabceka yanzu dole kayi haƙuri. Toh yanzu ma haƙurin zakayi mu kumayi addu'ar Allah ya kawo ninkinsu a gaba, amma gaskiya nafi zargin canza kayan nan sukayi dan irin packing ɗin da akayi da wahala ace wai ruwa ne ya tarar dasu har yayi wannan ɓarnar sai dai idan dama can lalatattun ne" Alhaji Yusuf ya faɗa yana dafa kafaɗarsa.
Cike da ƙarfin hali kawai Bilal yake ɗaga masa kai, gaba ɗaya basu fi buhu goma sha zuwa ashirin bane aka buɗe su lafiya lau sauran komai ya lalace ba ga Zoɓon ba ba cittar ba sun yi funfuna cittar kuwa da yawan buhunhunan har ta siƙe kamar yanda sukace ta zama kamar ƙurar katako.
"Kaga lissafin iya abinda aka samu nan, sai ka sake turawa da Abu Amar details ɗin sai ku ƙarasa magana, yanzu bari naje ana jirana idan kuma yanzu zaka wuce sai mu tafi tare ka saukeni dan ba da mota na fito ba" Alhaji Yusuf ɗin ya sake faɗa, yanda yake magana ba zaka ɗauka da wanda ya tafka asarar Miliyoyin kuɗaɗe yakeyi ba kamar ma ba komai. Da laluben bango Bilal ya fita daga office ɗin, Yusuf ɗin ne yaja motar dan ce masa yayi baya gani sosai ya taimaka ya kaishi gida kawai.