Sashe 131
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani tunanin ne ya sake gifta masa wai me yasa ita bata tsoronsa?
Kashe shower yayi ya zauna akan toilet yayi shiru kamar mai jira wani ya bashi amsar. Ya tafi tunanin farkon aurensu da Halima daƙyar sai ya matsa take iya kallonsa babu riga amma ita wannan haka take ƙure shi da ido kamar mayya har lashe baki takeyi idan da ya biye mata ma da tuni tun kafin ɗinkin nata ya warke ma zata bashi kanta kwata kwata babu kunya ko jin nauyinsa a tareda ita ko da kuwa tayi ƙoƙarin nuna hakan bai san mai yasa yake ganin kamar na ƙarya ne ba.
Ji yayi kansa na nema ya fara ciwo dole ya kore tunanin ya miƙe ya shiga wanka, sanda ya fito tana kwance akan Gadon amma ya san ba bacci takeyi ba tunda bai ji munshari ba, ya wuce gaban mirror zai ɗauki wayarsa ya bar mata ɗakin hancinsa ya fara shaƙo masa wani ƙamshi, kansa ya sara, kamar wanda aka ja da igiya haka ya tafi kamar kuma waccen ranar yau ɗin ma haka ya ringa aiki tun yana na jin daɗi har ya koma na wahala sai gashi yana kuka wiwi duk kuma yanda ya so ya bari abu ya gagara sai da ita da kanta ta gaji kafin ta yakiceshi daƙyar ta gudu banɗaki ta kulle ƙofa.
Bilal kuwa kwanciya yayi riƙe da ciki yana juyi cikin azaba, ya gaji amma kuma so yake yayi abun, daƙyar ya lallaɓa ya fice daga ɗakin ya koma nasa ya shiga wanka, sai da yayi kusan saɓi uku har cikin hancinsa ya wanke kafin ya daina jin ƙamshin turaren a hankali kuma nutsuwa ta fara saukar masa ya fita ya kwanta akan gado yana sauke ajiyar zuciya a jere. Gaskiya ba haka kawai ba akwai wani abu dan shi dai a rayuwarsa bai taɓa gamuwa da irin wannan bala'in ba. Sai gurin ƙarfe tara ya iya tashi yayi sallar magriba da Isha'i, yana zaune ya jiyo tana ƙwanƙwasa masa ƙofa haɗi da kiran sunansa kamar na zai tashi ba sai kuma ya miƙe yana rangaji yaje ya buɗe mata.
Sum sum ta wuce ta ajiye try ɗin data shiryo masa kayan abinci akai, ba tareda ta kalle shi ba ta miƙa masa wayarsa tana cewa
"Tun ɗazu ake kira" ya karɓa yana kallonta sai kuma ya ji tausayinta yana ratsashi babu dalili. Abincin data zuba masa ya jata jikinsa suka shiga ci, jollop ɗin shinkafa taji nama ga kuma peppered chicken daban a gefe da salad sai lemon exotic babban kwali mai sanyi sosai. Sai da ya kai geji kafin ya shiga tantance abincin. Ɗanɗanon da ƙamshi harda yanda aka shirya abincin ma bai yi kama da girkinta ba.
Zulaiha bata iya girki ba bai kuma yi mamakin hakan ba domin ya fi kowa sanin daga gidan daya ɗakkota, yayi gyaran murya ya ce
"Daga ina aka kawo abinci?" Ta kalle shi a shagwaɓe ta ce
"Ni na girka mana" ɗan murmushi yayi ya ce
"Ai nasan bamu da ingredients ɗin da zakiyi irin wannan girkin, ya kamata ma a samo fridge gaskiya saboda ajiyar nama da kayan miya na gaji da siyan guntu guntun nan" daga haka ya ɗauki wayarsa ya shiga duba missed calls ita kuma ta kwashe kwanuka ta fita da su ranta ƙal.
Kiran Kamalu ya fara bi dukda yaga missed calls ɗin Hajja kusan guda goma, basu wani ja gaisuwa mai tsayi ba Kamalu ya ce masa
"An ce kayi ta zuwa nemana Allah ya sa lafiya dai"
"Eh wlh kuma nayi ta kiran layinka kullum a kashe, dama maganar shagunan nan ce na bawa lawyer na takardun ya duba amma ya ce fake ne" Bilal ya bashi amsa.
"Fake kuma?" Kamalu ya tambaya cikin mamaki Bilal ya amsa masa da
"Haka ya ce, nima nayi mamaki amma kuma dana haɗa su da wasu takardu na ga banbancin da ya ce akwai tsakaninsu da original ɗin".
"Gaskiya toh bansan a inda aka samu matsala ba dan kai shaida ne takardun nan hannu da hannu yanda aka bani su take na miƙa maka ban ko tafi dasu wani guri ba balle ace ni na canza su" Kamalu ya faɗa.
"Ai ba ina zarginka bane Alhaji Kamalu nima abun ya bani mamaki ne kaga kenan daga can gurinsu da suka siyar mana sune macutan, sun karɓi kuɗin mu ƙila zasu sake siyarwa da wasu kuma"
"Gaskiya a sanin da nayiwa Alhaji Balarabe ba zai taɓa yin haka ba, na fi shekara goma sha biyar muna harkar ƙasa da shi ba'a taɓa samun saɓani ba, amma abinda zai faru gobe idan Allah ya kaimu kazo office ka sameni sai muje gurinsa duk ma abinda ya faru sai a warware" Kamalu ya sake faɗa daga haka sukayi sallama.
Dukd dare ya farayi haka ya tafi gidan Hajja tareda Zulaiha, sai da ya tsaya a hanya yayi mata siyayyar toshiyar baki kafin suka isa gidan. Fadila na falo tana kallo ita da Abubakar shi kuma yana cin abinci suka shiga, ta gaishe shi ba tareda ta ko kalli Zulaihan ba Abubakar dai tamkar bai ji shigarsu ba sai da Bilal ɗin yayi masa magana kafin ya ɗaga kai tareda yi masa sannu a taƙaice ya cigaba da cin abincin sa.
Ɗaki ya wuce da Fadila ta ce masa Hajjan ta kwanta, ya zauna daga gefen ƙafarta yana gaisheta dan ba bacci takeyi ba kafin ta miƙe zaune fuska ba yabo ba fallasa ta ce
"Ashe kuma ka saki Halima"
Kai a ƙasa yana shafa ƙeya ya ce
"Kotu suka ce zasu kai ni Hajja ni kuma naji tsoro kar su fitar da waccen maganar shiyasa kawai na saketa".
"Ai shikenan, yanzu yaushe zaka karɓo yaran toh?" Hajja ta sake faɗa. Da sauri ya kalleta ya ce
"A karɓo yara kuma Hajja?"
"Da bar mata su zakayi shikenan an rabu kake nufi ko me?"
"Aa ba haka nake nufi ba, da niyyata dai a barsu su ƙara tasawa tunda yanzu idan an ɗakko su nan idan aka kawosu wahala zasu zamar miki" ya sake faɗa kai a ƙasa. Hajja dake kallonsa ta ce
"Au, ni kake zaton zan riƙe maka yaran ma kenan? Ita waccen ɗin daka auro menene amfanin ta? Da zuwa kawai tayi ta samu guri taci arziƙi kenan ko me?"
"Ba haka nake nufi ba Hajja" ya faɗa a hankali ta katseshi da cewa
"Ka saurareni da kyau dole ka karɓo yaran nan saboda ta hakane zaka ƙuntata mata da ita da iyayen nata kuma zamu samu damar jansu a ƙasa yanda muke so a dalilin yaran sannan itama wannan yar matsiyatan daka ɗakko ba zaman banza zatayi ba dole tayi maka wahalar yaya".
Shiru yayi ya kasa ce mata komai, Hajjan ce ta sake cewa
"Wai ina Hafizu ne kwana biyu?"
"Yayi tafiya ne kusan wata uku baya ƙasar" ya shata mata ƙarya, ta taɓe baki ta ce
"Yanzu saboda mugunta da hassada ƙiri ƙiri kaƙi kayi masa maganar Fadila ko? Tunda kai kayi mana baƙin ciki Allah ya kawo mana mai taimakonmu har gida amma ka kwaɓar da damar shine itama kake mata baƙin ciki karta samu in da zata huta har muma mu mora"
"Amma Hajja na gaya miki maganar nan ba mai yuwuwa ba ce ba, mutumin nan da matarsa yana sonta bai taɓa kallon Fadila a matsayin wacce zai iya so ba kina gani saboda rashin hankalinta ta ringa shige masa har sai da ya fahimci abinda take nufi in da yana ra'ayi ai da zai amsa amma daga haka mai ta janyo? Janye jikinsa yayi ya daina zuwa gidan nan kuma shine kike so ni na tallata masa ita gaskiya ba zan iya ba" ya bata amsa ba tareda ya kalleta ba.
Tayi ƙwafa ta ce
"Ai shikenan nan"
"Kiyi haƙuri idan na ɓata miki rai Hajja" ya sake faɗa cikin sigar rarrashi,
"Yanzu ita yaushe zata dawo ayi maganar auren?" Ta sake soko masa wata maganar, ya fahimci wa take nufi amma ya waske da tambayar wacece
"Ita shaiɗaniyar yarinyar nan mana" ta bashi amsa a fusace. Ya marairaice fuska ya ce
"Yanzu Hajja ko ni na dage zan aureta dan Allah sai ki barni nayi?"
"Akan mai zan hanaka? Dama ai abinda ya kamata kenan ko kuwa kana nufin taci banza ta lalataka sannan taƙi aurenka? Toh wlh ba zai yuwu ba" ta bashi amsa. Ya buɗe baki zai sake magana wayarsa ta shiga ƙara dan haka ya dakata ya zarota gabansa ya yanke ya faɗi ganin international number ko ba'a faɗa ba kuma ya san Jalilah ce.
Ji yayi zufa ta fara keto masa ya danna wayar a silent ya mayar da ita Aljihu ya miƙe yana kallon Hajja ya ce
"Bari naje Hajja sai gobe" ta amsa masa da
"Allah ya tashe mu lafiya" tana karantar sauyin da yayi lokaci ɗaya.
A falo Zulaiha kaɗai ya tarar tana ganinsa kuwa ta miƙe yayi gaba ta bi bayansa. Sai da suka zauna a mota kafin ta ce masa tana so taci Shawarma ta faɗa masa kuma ta inda take so. Ya kalleta da mamaki jin inda ta faɗo ɗin, kallon daya mata ya saka ta gane ta kwafsa dan haka tayi saurin cewa
"Saurayin Zahra ne yake siyo mata ya kai mata School, na taɓa ci sau biyu tayi mun daɗi sosai shiyasa na riƙe sunan gurin". Bai amsa mata ba suka tafi, tana ta sako masa hira dan ta kawar masa da tunani amma da Eh ko Uhm yake amsa mata kawai. ATM ɗin sa ya bata ya ce taje tayi order dukda yanda gurin yake cike da Maza amma yana buƙatar space ɗin ne saboda number ɗazu da ake ta sake kiransa da ita. Tana fita kuwa kiran ya sake shigowa, saida ya kashe motar kafin ya ɗaga murya can ƙasa kamar mai bacci yayi sallama.
Muryar Jalilah ta sauka raɗau a kunnensa
"Yau dai Allah yayi na sameka a waya" ta faɗa, ya sake narke murya ya ce
"Nayi kewarki Babe, mai nayi miki? Kin toshe duk wata hanya da zan iya samunki phone call, Whatsapp, IG duk kinyi blocking ɗina what have i done to deserve such punishment Jalilah?"
Kashe shower yayi ya zauna akan toilet yayi shiru kamar mai jira wani ya bashi amsar. Ya tafi tunanin farkon aurensu da Halima daƙyar sai ya matsa take iya kallonsa babu riga amma ita wannan haka take ƙure shi da ido kamar mayya har lashe baki takeyi idan da ya biye mata ma da tuni tun kafin ɗinkin nata ya warke ma zata bashi kanta kwata kwata babu kunya ko jin nauyinsa a tareda ita ko da kuwa tayi ƙoƙarin nuna hakan bai san mai yasa yake ganin kamar na ƙarya ne ba.
Ji yayi kansa na nema ya fara ciwo dole ya kore tunanin ya miƙe ya shiga wanka, sanda ya fito tana kwance akan Gadon amma ya san ba bacci takeyi ba tunda bai ji munshari ba, ya wuce gaban mirror zai ɗauki wayarsa ya bar mata ɗakin hancinsa ya fara shaƙo masa wani ƙamshi, kansa ya sara, kamar wanda aka ja da igiya haka ya tafi kamar kuma waccen ranar yau ɗin ma haka ya ringa aiki tun yana na jin daɗi har ya koma na wahala sai gashi yana kuka wiwi duk kuma yanda ya so ya bari abu ya gagara sai da ita da kanta ta gaji kafin ta yakiceshi daƙyar ta gudu banɗaki ta kulle ƙofa.
Bilal kuwa kwanciya yayi riƙe da ciki yana juyi cikin azaba, ya gaji amma kuma so yake yayi abun, daƙyar ya lallaɓa ya fice daga ɗakin ya koma nasa ya shiga wanka, sai da yayi kusan saɓi uku har cikin hancinsa ya wanke kafin ya daina jin ƙamshin turaren a hankali kuma nutsuwa ta fara saukar masa ya fita ya kwanta akan gado yana sauke ajiyar zuciya a jere. Gaskiya ba haka kawai ba akwai wani abu dan shi dai a rayuwarsa bai taɓa gamuwa da irin wannan bala'in ba. Sai gurin ƙarfe tara ya iya tashi yayi sallar magriba da Isha'i, yana zaune ya jiyo tana ƙwanƙwasa masa ƙofa haɗi da kiran sunansa kamar na zai tashi ba sai kuma ya miƙe yana rangaji yaje ya buɗe mata.
Sum sum ta wuce ta ajiye try ɗin data shiryo masa kayan abinci akai, ba tareda ta kalle shi ba ta miƙa masa wayarsa tana cewa
"Tun ɗazu ake kira" ya karɓa yana kallonta sai kuma ya ji tausayinta yana ratsashi babu dalili. Abincin data zuba masa ya jata jikinsa suka shiga ci, jollop ɗin shinkafa taji nama ga kuma peppered chicken daban a gefe da salad sai lemon exotic babban kwali mai sanyi sosai. Sai da ya kai geji kafin ya shiga tantance abincin. Ɗanɗanon da ƙamshi harda yanda aka shirya abincin ma bai yi kama da girkinta ba.
Zulaiha bata iya girki ba bai kuma yi mamakin hakan ba domin ya fi kowa sanin daga gidan daya ɗakkota, yayi gyaran murya ya ce
"Daga ina aka kawo abinci?" Ta kalle shi a shagwaɓe ta ce
"Ni na girka mana" ɗan murmushi yayi ya ce
"Ai nasan bamu da ingredients ɗin da zakiyi irin wannan girkin, ya kamata ma a samo fridge gaskiya saboda ajiyar nama da kayan miya na gaji da siyan guntu guntun nan" daga haka ya ɗauki wayarsa ya shiga duba missed calls ita kuma ta kwashe kwanuka ta fita da su ranta ƙal.
Kiran Kamalu ya fara bi dukda yaga missed calls ɗin Hajja kusan guda goma, basu wani ja gaisuwa mai tsayi ba Kamalu ya ce masa
"An ce kayi ta zuwa nemana Allah ya sa lafiya dai"
"Eh wlh kuma nayi ta kiran layinka kullum a kashe, dama maganar shagunan nan ce na bawa lawyer na takardun ya duba amma ya ce fake ne" Bilal ya bashi amsa.
"Fake kuma?" Kamalu ya tambaya cikin mamaki Bilal ya amsa masa da
"Haka ya ce, nima nayi mamaki amma kuma dana haɗa su da wasu takardu na ga banbancin da ya ce akwai tsakaninsu da original ɗin".
"Gaskiya toh bansan a inda aka samu matsala ba dan kai shaida ne takardun nan hannu da hannu yanda aka bani su take na miƙa maka ban ko tafi dasu wani guri ba balle ace ni na canza su" Kamalu ya faɗa.
"Ai ba ina zarginka bane Alhaji Kamalu nima abun ya bani mamaki ne kaga kenan daga can gurinsu da suka siyar mana sune macutan, sun karɓi kuɗin mu ƙila zasu sake siyarwa da wasu kuma"
"Gaskiya a sanin da nayiwa Alhaji Balarabe ba zai taɓa yin haka ba, na fi shekara goma sha biyar muna harkar ƙasa da shi ba'a taɓa samun saɓani ba, amma abinda zai faru gobe idan Allah ya kaimu kazo office ka sameni sai muje gurinsa duk ma abinda ya faru sai a warware" Kamalu ya sake faɗa daga haka sukayi sallama.
Dukd dare ya farayi haka ya tafi gidan Hajja tareda Zulaiha, sai da ya tsaya a hanya yayi mata siyayyar toshiyar baki kafin suka isa gidan. Fadila na falo tana kallo ita da Abubakar shi kuma yana cin abinci suka shiga, ta gaishe shi ba tareda ta ko kalli Zulaihan ba Abubakar dai tamkar bai ji shigarsu ba sai da Bilal ɗin yayi masa magana kafin ya ɗaga kai tareda yi masa sannu a taƙaice ya cigaba da cin abincin sa.
Ɗaki ya wuce da Fadila ta ce masa Hajjan ta kwanta, ya zauna daga gefen ƙafarta yana gaisheta dan ba bacci takeyi ba kafin ta miƙe zaune fuska ba yabo ba fallasa ta ce
"Ashe kuma ka saki Halima"
Kai a ƙasa yana shafa ƙeya ya ce
"Kotu suka ce zasu kai ni Hajja ni kuma naji tsoro kar su fitar da waccen maganar shiyasa kawai na saketa".
"Ai shikenan, yanzu yaushe zaka karɓo yaran toh?" Hajja ta sake faɗa. Da sauri ya kalleta ya ce
"A karɓo yara kuma Hajja?"
"Da bar mata su zakayi shikenan an rabu kake nufi ko me?"
"Aa ba haka nake nufi ba, da niyyata dai a barsu su ƙara tasawa tunda yanzu idan an ɗakko su nan idan aka kawosu wahala zasu zamar miki" ya sake faɗa kai a ƙasa. Hajja dake kallonsa ta ce
"Au, ni kake zaton zan riƙe maka yaran ma kenan? Ita waccen ɗin daka auro menene amfanin ta? Da zuwa kawai tayi ta samu guri taci arziƙi kenan ko me?"
"Ba haka nake nufi ba Hajja" ya faɗa a hankali ta katseshi da cewa
"Ka saurareni da kyau dole ka karɓo yaran nan saboda ta hakane zaka ƙuntata mata da ita da iyayen nata kuma zamu samu damar jansu a ƙasa yanda muke so a dalilin yaran sannan itama wannan yar matsiyatan daka ɗakko ba zaman banza zatayi ba dole tayi maka wahalar yaya".
Shiru yayi ya kasa ce mata komai, Hajjan ce ta sake cewa
"Wai ina Hafizu ne kwana biyu?"
"Yayi tafiya ne kusan wata uku baya ƙasar" ya shata mata ƙarya, ta taɓe baki ta ce
"Yanzu saboda mugunta da hassada ƙiri ƙiri kaƙi kayi masa maganar Fadila ko? Tunda kai kayi mana baƙin ciki Allah ya kawo mana mai taimakonmu har gida amma ka kwaɓar da damar shine itama kake mata baƙin ciki karta samu in da zata huta har muma mu mora"
"Amma Hajja na gaya miki maganar nan ba mai yuwuwa ba ce ba, mutumin nan da matarsa yana sonta bai taɓa kallon Fadila a matsayin wacce zai iya so ba kina gani saboda rashin hankalinta ta ringa shige masa har sai da ya fahimci abinda take nufi in da yana ra'ayi ai da zai amsa amma daga haka mai ta janyo? Janye jikinsa yayi ya daina zuwa gidan nan kuma shine kike so ni na tallata masa ita gaskiya ba zan iya ba" ya bata amsa ba tareda ya kalleta ba.
Tayi ƙwafa ta ce
"Ai shikenan nan"
"Kiyi haƙuri idan na ɓata miki rai Hajja" ya sake faɗa cikin sigar rarrashi,
"Yanzu ita yaushe zata dawo ayi maganar auren?" Ta sake soko masa wata maganar, ya fahimci wa take nufi amma ya waske da tambayar wacece
"Ita shaiɗaniyar yarinyar nan mana" ta bashi amsa a fusace. Ya marairaice fuska ya ce
"Yanzu Hajja ko ni na dage zan aureta dan Allah sai ki barni nayi?"
"Akan mai zan hanaka? Dama ai abinda ya kamata kenan ko kuwa kana nufin taci banza ta lalataka sannan taƙi aurenka? Toh wlh ba zai yuwu ba" ta bashi amsa. Ya buɗe baki zai sake magana wayarsa ta shiga ƙara dan haka ya dakata ya zarota gabansa ya yanke ya faɗi ganin international number ko ba'a faɗa ba kuma ya san Jalilah ce.
Ji yayi zufa ta fara keto masa ya danna wayar a silent ya mayar da ita Aljihu ya miƙe yana kallon Hajja ya ce
"Bari naje Hajja sai gobe" ta amsa masa da
"Allah ya tashe mu lafiya" tana karantar sauyin da yayi lokaci ɗaya.
A falo Zulaiha kaɗai ya tarar tana ganinsa kuwa ta miƙe yayi gaba ta bi bayansa. Sai da suka zauna a mota kafin ta ce masa tana so taci Shawarma ta faɗa masa kuma ta inda take so. Ya kalleta da mamaki jin inda ta faɗo ɗin, kallon daya mata ya saka ta gane ta kwafsa dan haka tayi saurin cewa
"Saurayin Zahra ne yake siyo mata ya kai mata School, na taɓa ci sau biyu tayi mun daɗi sosai shiyasa na riƙe sunan gurin". Bai amsa mata ba suka tafi, tana ta sako masa hira dan ta kawar masa da tunani amma da Eh ko Uhm yake amsa mata kawai. ATM ɗin sa ya bata ya ce taje tayi order dukda yanda gurin yake cike da Maza amma yana buƙatar space ɗin ne saboda number ɗazu da ake ta sake kiransa da ita. Tana fita kuwa kiran ya sake shigowa, saida ya kashe motar kafin ya ɗaga murya can ƙasa kamar mai bacci yayi sallama.
Muryar Jalilah ta sauka raɗau a kunnensa
"Yau dai Allah yayi na sameka a waya" ta faɗa, ya sake narke murya ya ce
"Nayi kewarki Babe, mai nayi miki? Kin toshe duk wata hanya da zan iya samunki phone call, Whatsapp, IG duk kinyi blocking ɗina what have i done to deserve such punishment Jalilah?"