Sashe 115
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki dena kuka, kowa da kalar ƙaddararsa a rayuwa kuma na gaya miki ko me kika aikata a baya ina sonki a haka tunda dai kin tuba kin dena kuma har kika iya faɗa mun na tabbatar dagaske ne kin bari karki ji komai In sha Allahu daga ni har dangina ba zaki samu matsala da kowa ba".
Ya ringa juya maganar a ransa, to ko dai abun iya ita Nuratun ya shafa shiyasa Zulaiha bata gaya masa ba? To menene ma? Ya ringa tambayar kansa a garin tunani har ya wuce gidan Anty Jalilan ma sai da Nasir ya ankarar dashi.
A falon baƙi suka zauna, ya ringa kallon Al'amin da yayi kamar bai sanshi ba dan da suka shiga yana kallon su ya juya ya wuce sai da Nasir ya kira shi ne ya tsaya amma yaƙi zuwa gurin Bilal ɗin Nasir ɗin ma daya riƙe masa hannu bai sake da shi ba Alhaji Sale na shigowa kuma ya fizge ya tafi gurin sa.
Faran faran suka gaisa da Alhaji Salen da bai daɗe da shiga gidan ba daga tafiya, masallaci zai fita sallar isha'i dan haka suka tafi gaba ɗaya. Can falon ya ce a kai musu abinci bayan sun dawo suka ci tare Nasir dai ya ware ya kashi abincin sa Bilal kuwa dukda yana jin yunwa kaɗan ya ci dan haka kawai yake ji kamar wata manaƙisar aka shirya masa idan ba haka ba shida yake da laifi a gurinsu shine harda bashi abinci?
Sai da aka kwashe kwanukan kafin Alhaji Salen ya wuce ciki ya turo musu Halima. Ta shiga da ƙaramar sallama kai a ƙasa kamar farin shigar maita haka Bilal ya zuba mata ido yana kallonta, rabon da ya sakata a ido tun ranar daya kaita gida. Ramar da tayi ta taɓa shi dan sukda hijab ne har ƙasa a jikinta ramarta ta fito ƙarara.
A hankali ta ringa tafiya harta isa kujerar da tafi kusa da ƙofa ta zauna, murya ba amo ta gaida Nasir da tausayinta ya rufe shi lokaci ɗaya. Halima mace yar gayu amma kalli yanda ta lalace lokaci ɗaya ta zama kalar tausayi. Miƙewa yayi ya fita dan ya basu guri, yana rufo ƙofa Bilal ya tashi da sauri ya nufeta, da sauri itama ta miƙe tayi baya ganin rungumarta yake shirinyi.
Ta galla masa hararar da ta saka gabansa faɗuwa domin ko a mafarki bai taɓa ganin ta da irin kallon nan ba.
HALIMA
Ganinsa nayi tamkar baƙin kumurci lokacin daya nufoni, hoton fuskarsa akan cinyar Jalilah ya gifta mun da sauri na miƙe na ja baya ganin yana rungumata.
"Meye haka Halims? Kin san adadin kewarki da nayi kuwa? Dan Allah ki tsaya inji ɗumin ki ko zan samu nutsuwar zuciya nayi kewarki har bansan adadi ba wlh" ya faɗa yana sake nufo ni.
Tsawa na buga masa da dukkan ƙarfin daya rage mun, ya tsaya can a inda yake cikin mamakina, ban damu ba na nuna shi ina cewa
"Ka koma in da ka taso idan ba haka ba zan tafi ba kuma zaka sake samun damar magana dani ba har abadah"
"Haba my Halims sai kace wacce zata mutu?" Ya faɗa yana ja baya bai dai koma kan kujerar daya tashi ba, nayi tsaki na ce
"Ba wasa nakeyi ba, minti goma kake dashi idan kuma ya cika baka nutsu munyi maganar data kawoka ba kada ka tsammaci zaka sake samun irin wannan damar a gaba". Ganin da gaske nake ya saka ya koma kan kujerar ya zauna yana kallo na, nima zama nayi kaina a ƙasa dan ba ƙaramin ƙarfin hali nake ba ji nake kamar an jona mun mayen ƙarfe yana jana in je gare shi amma na dake.
"Wlh Halima duk abinda ya faru ba laifi na bane sharrin shaiɗan ne" ya faɗa yana zamowa daga kujerar kamar zai durƙusa a ƙasa. Ban kalle shi ba ya cigaba da cewa
"Kuma wlh duk abinda kike zato ba haka bane tsakanina da Jalilah. Kawai ƙananan romance ne irin abubuwan da na so mu ringayi lokacin da nake neman aurenki kika ƙi amma wlh ban taɓa kusantarta ba kuma idan baki yarda ba zan kira miki ita ta faɗa miki da bakinta".
Kallonsa nayi ina murmushin da ya fi kuka ciwo na ce
"Amma mai ka ce mun tun a sanda kake neman auren nawa akan hakan? Wane alƙawari ka ɗaukar mun?"
Shiru yayi dan shi bai tuna abinda take magana akai ba, ya san dai ƙi tayi, duk yanda ya kaɗata ya raya ko hannunta ya kama bisa kuskure a lokacin ne kaɗai yake ganin ɓacin ranta har ta iya rufe ido ta masa rashin mutunchi daga baya ya rabu da ita tunda bata so kuma yana samu a wasu gurin a bati ma wasu so suke ya taɓa su.
"Kiyi haƙuri" ya faɗa. Na ɗaga kai na sama saboda hawayen da yake shirin zubo mun sai da suka ɗan tsahirta kafin na kalle shi na ce
"Yanzu ni duk ba wannan maganar nake so muyi ba... "
"Kin haƙura ko my Halims? Ni dama na san soyayyar da kike mun ba zata bari ki yarda a rabamu ba"
"Sonka, soyayyarka kullum maganarka kenan, duk idan zakayi magana sai kace son da nake maka ya saka ko soyayyar da nake maka ba zata bari nayi kaza ba Bilal mai ka ɗauke ni?" Na faɗa ina cije leɓe na. Ya ɗan yi shiru kafin ya ce
"Masoyiyata mana Halims"
"Bilal ka taɓa so na?" Na jefa masa tambayar da take cin raina, ya zaburo zai matso in da nake na ɗaga masa hannu sai ya koma baya yace
"Ina sonki mana Halims ai kema kin sani"
"Mai ya sa duk sanda ka tashi magana baka taɓa cewa nayi abu saboda son da kake yi mun ba sai dai kace saboda son da nake maka" na sake jefa masa wata tambayar.
Kamar an doki bakinsa maganar ta fito
"Saboda son ki ya fi nawa yawa".
Da hannu biyu ya dafe baki bayan daya fuskanci abinda ya faɗa. Na saki murmushin daya taho tareda hawayen da nake ta riƙewa na sake ɗaga masa hannu ganin ya sakw nufoni yana cewa
"Wlh ba abinda zan faɗa ba kenan, cewa zanyi son da nake miki yafi wanda kike mun yawa".
"Amsar da nake buƙata kenan kuma na sameta. Nagode da alfarmar da kayi mun ka zauna dani tsahon lokacin nan albarkacin son da nake maka, nagode da duk abinda ka mun a tsayin zamanmu.
Na san yanda zuciya takeji a lokacin da abinda bata so yake mata naci, kayi ƙoƙari daka iya kasancewa tareda ni tsayin lokacin nan, daga yau ka yantu, ba zaka sake kwanciya ka tashi da tunanin ganin wacce zuciyarka bata muradi ba.." kukan daya sarƙe ni ya hanani cigaba da magana. Biro da takardar da na taho dasu na zaro daga aljihun rigar jiki na na ɗora akan center table ina cewa
"Gashi nan, ka datse alaƙar da take tsakanina da kai ka samarwa zuciyoyinmu yanci".
"Ba zan iya sakin ki ba Halima wlh ina sonki" ya faɗa bayan daya rarrafo ya kama ƙafafu na. Haɗe kai da cinya nayi na shiga rusa kuka tamkar wacce za'a rataye, jin yana ɗagoni, lokaci ɗaya cikin wani fushi da ban san sanadinsa ba na ɗago na wanke shi da marin da ni kaina sai da naji a jikina saboda raɗaɗin da tafin hannuna har zuwa ƙasusuwan hannun suka ɗauka saboda ƙarfin marin.
Yayi baya ya zauna wanwar yana kallona cikin mamaki, takardar na nuna masa na ce
"Ka ɗauki takardar nan ka rubuta abinda na buƙata. Sanyin halin Halima ka sani, kada ka bari in nuna maka ɗaya ɓangaren domin ba lallai idanuwanka su iya jurar kallo ba".
"Ke karki ga ina lallaɓa ki ki nemi raina mun hankali, ba dai a hannuna igiyar auren take ba? To ba zan saki ba idan kina da ƙarfi ki danne ni ki ƙwata ko ki turo wani ya ƙwatar miki. Ƙaryar banza ƙaryar wofi kawai ni da ke mun sani Halima wlh ba zaki iya rayuwa babu ni ba gara ma ki rufawa kanki asiri mu koma tun lokaci bai ƙure miki ba" ya faɗa cikin fushi bayan daya miƙe tsaye.
Tashi nayi nima ina kallon sa na ce
"Ba dan kar inyi saɓo ba dana tsinewa ƙaddarar data haɗa ni da kai, wlh Bilal ko ban ce komai akanka ba da sannu sai kaga sakayyar butulcin da kayi mun, kaje Allah ya isa tsakanina da kai za kuma ka gani tunda kaƙi sakina ta lallami wahala zata sa ka saki ko baka ƙaunar Allah" na faɗa ina fashewa da kuka na juya zan bar falon dai dai lokacin da Nasir ya shigo da alama hayaniyarmu ta janyo hankalinsa.
"Tsaya Halima, kai Bilal menene haka? Mu da muka zo sulhu kuma zaka ɓige da rashin hankali?" Nasir ɗin ya faɗa. Na coge a tsaye dan ya tare hanyar ina jin Bilal na cewa
"Dallah rabu da ita aikin banza laifi na ne da na zo shiyasa har ta samu damar yi mun wata fuffuka. Na faɗa kuma ba zanyi sakin ba a saka kaina gabas a yanka. Ya ne iyayen naki basuyi su hanaki aure na ba amma kika nace, kina gidana sau nawa suna cewa ki kashe auren kika ƙi, sau nawa kika zaɓe farin ciki na akan nasu sai yanzu ne zaki zo kina wasu maganganu? To ba'a son naki kuma ba za'a sakeki ba kiyi abinda zakiyi. Idan kinga dama ki dawo in ma kin so kiyi ta zama a gidan naku har duniya ta tashi ni ba matsalata bace"
ya nufi ƙofa fuuuu ya bangaje Nasir sai ganin sa mukayi kamar an chillo shi ya dawo baya ya faɗi tim a ƙasa.
[5/12, 9:44 PM] Zainab Madawaki Dahiru: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
Ya ringa juya maganar a ransa, to ko dai abun iya ita Nuratun ya shafa shiyasa Zulaiha bata gaya masa ba? To menene ma? Ya ringa tambayar kansa a garin tunani har ya wuce gidan Anty Jalilan ma sai da Nasir ya ankarar dashi.
A falon baƙi suka zauna, ya ringa kallon Al'amin da yayi kamar bai sanshi ba dan da suka shiga yana kallon su ya juya ya wuce sai da Nasir ya kira shi ne ya tsaya amma yaƙi zuwa gurin Bilal ɗin Nasir ɗin ma daya riƙe masa hannu bai sake da shi ba Alhaji Sale na shigowa kuma ya fizge ya tafi gurin sa.
Faran faran suka gaisa da Alhaji Salen da bai daɗe da shiga gidan ba daga tafiya, masallaci zai fita sallar isha'i dan haka suka tafi gaba ɗaya. Can falon ya ce a kai musu abinci bayan sun dawo suka ci tare Nasir dai ya ware ya kashi abincin sa Bilal kuwa dukda yana jin yunwa kaɗan ya ci dan haka kawai yake ji kamar wata manaƙisar aka shirya masa idan ba haka ba shida yake da laifi a gurinsu shine harda bashi abinci?
Sai da aka kwashe kwanukan kafin Alhaji Salen ya wuce ciki ya turo musu Halima. Ta shiga da ƙaramar sallama kai a ƙasa kamar farin shigar maita haka Bilal ya zuba mata ido yana kallonta, rabon da ya sakata a ido tun ranar daya kaita gida. Ramar da tayi ta taɓa shi dan sukda hijab ne har ƙasa a jikinta ramarta ta fito ƙarara.
A hankali ta ringa tafiya harta isa kujerar da tafi kusa da ƙofa ta zauna, murya ba amo ta gaida Nasir da tausayinta ya rufe shi lokaci ɗaya. Halima mace yar gayu amma kalli yanda ta lalace lokaci ɗaya ta zama kalar tausayi. Miƙewa yayi ya fita dan ya basu guri, yana rufo ƙofa Bilal ya tashi da sauri ya nufeta, da sauri itama ta miƙe tayi baya ganin rungumarta yake shirinyi.
Ta galla masa hararar da ta saka gabansa faɗuwa domin ko a mafarki bai taɓa ganin ta da irin kallon nan ba.
HALIMA
Ganinsa nayi tamkar baƙin kumurci lokacin daya nufoni, hoton fuskarsa akan cinyar Jalilah ya gifta mun da sauri na miƙe na ja baya ganin yana rungumata.
"Meye haka Halims? Kin san adadin kewarki da nayi kuwa? Dan Allah ki tsaya inji ɗumin ki ko zan samu nutsuwar zuciya nayi kewarki har bansan adadi ba wlh" ya faɗa yana sake nufo ni.
Tsawa na buga masa da dukkan ƙarfin daya rage mun, ya tsaya can a inda yake cikin mamakina, ban damu ba na nuna shi ina cewa
"Ka koma in da ka taso idan ba haka ba zan tafi ba kuma zaka sake samun damar magana dani ba har abadah"
"Haba my Halims sai kace wacce zata mutu?" Ya faɗa yana ja baya bai dai koma kan kujerar daya tashi ba, nayi tsaki na ce
"Ba wasa nakeyi ba, minti goma kake dashi idan kuma ya cika baka nutsu munyi maganar data kawoka ba kada ka tsammaci zaka sake samun irin wannan damar a gaba". Ganin da gaske nake ya saka ya koma kan kujerar ya zauna yana kallo na, nima zama nayi kaina a ƙasa dan ba ƙaramin ƙarfin hali nake ba ji nake kamar an jona mun mayen ƙarfe yana jana in je gare shi amma na dake.
"Wlh Halima duk abinda ya faru ba laifi na bane sharrin shaiɗan ne" ya faɗa yana zamowa daga kujerar kamar zai durƙusa a ƙasa. Ban kalle shi ba ya cigaba da cewa
"Kuma wlh duk abinda kike zato ba haka bane tsakanina da Jalilah. Kawai ƙananan romance ne irin abubuwan da na so mu ringayi lokacin da nake neman aurenki kika ƙi amma wlh ban taɓa kusantarta ba kuma idan baki yarda ba zan kira miki ita ta faɗa miki da bakinta".
Kallonsa nayi ina murmushin da ya fi kuka ciwo na ce
"Amma mai ka ce mun tun a sanda kake neman auren nawa akan hakan? Wane alƙawari ka ɗaukar mun?"
Shiru yayi dan shi bai tuna abinda take magana akai ba, ya san dai ƙi tayi, duk yanda ya kaɗata ya raya ko hannunta ya kama bisa kuskure a lokacin ne kaɗai yake ganin ɓacin ranta har ta iya rufe ido ta masa rashin mutunchi daga baya ya rabu da ita tunda bata so kuma yana samu a wasu gurin a bati ma wasu so suke ya taɓa su.
"Kiyi haƙuri" ya faɗa. Na ɗaga kai na sama saboda hawayen da yake shirin zubo mun sai da suka ɗan tsahirta kafin na kalle shi na ce
"Yanzu ni duk ba wannan maganar nake so muyi ba... "
"Kin haƙura ko my Halims? Ni dama na san soyayyar da kike mun ba zata bari ki yarda a rabamu ba"
"Sonka, soyayyarka kullum maganarka kenan, duk idan zakayi magana sai kace son da nake maka ya saka ko soyayyar da nake maka ba zata bari nayi kaza ba Bilal mai ka ɗauke ni?" Na faɗa ina cije leɓe na. Ya ɗan yi shiru kafin ya ce
"Masoyiyata mana Halims"
"Bilal ka taɓa so na?" Na jefa masa tambayar da take cin raina, ya zaburo zai matso in da nake na ɗaga masa hannu sai ya koma baya yace
"Ina sonki mana Halims ai kema kin sani"
"Mai ya sa duk sanda ka tashi magana baka taɓa cewa nayi abu saboda son da kake yi mun ba sai dai kace saboda son da nake maka" na sake jefa masa wata tambayar.
Kamar an doki bakinsa maganar ta fito
"Saboda son ki ya fi nawa yawa".
Da hannu biyu ya dafe baki bayan daya fuskanci abinda ya faɗa. Na saki murmushin daya taho tareda hawayen da nake ta riƙewa na sake ɗaga masa hannu ganin ya sakw nufoni yana cewa
"Wlh ba abinda zan faɗa ba kenan, cewa zanyi son da nake miki yafi wanda kike mun yawa".
"Amsar da nake buƙata kenan kuma na sameta. Nagode da alfarmar da kayi mun ka zauna dani tsahon lokacin nan albarkacin son da nake maka, nagode da duk abinda ka mun a tsayin zamanmu.
Na san yanda zuciya takeji a lokacin da abinda bata so yake mata naci, kayi ƙoƙari daka iya kasancewa tareda ni tsayin lokacin nan, daga yau ka yantu, ba zaka sake kwanciya ka tashi da tunanin ganin wacce zuciyarka bata muradi ba.." kukan daya sarƙe ni ya hanani cigaba da magana. Biro da takardar da na taho dasu na zaro daga aljihun rigar jiki na na ɗora akan center table ina cewa
"Gashi nan, ka datse alaƙar da take tsakanina da kai ka samarwa zuciyoyinmu yanci".
"Ba zan iya sakin ki ba Halima wlh ina sonki" ya faɗa bayan daya rarrafo ya kama ƙafafu na. Haɗe kai da cinya nayi na shiga rusa kuka tamkar wacce za'a rataye, jin yana ɗagoni, lokaci ɗaya cikin wani fushi da ban san sanadinsa ba na ɗago na wanke shi da marin da ni kaina sai da naji a jikina saboda raɗaɗin da tafin hannuna har zuwa ƙasusuwan hannun suka ɗauka saboda ƙarfin marin.
Yayi baya ya zauna wanwar yana kallona cikin mamaki, takardar na nuna masa na ce
"Ka ɗauki takardar nan ka rubuta abinda na buƙata. Sanyin halin Halima ka sani, kada ka bari in nuna maka ɗaya ɓangaren domin ba lallai idanuwanka su iya jurar kallo ba".
"Ke karki ga ina lallaɓa ki ki nemi raina mun hankali, ba dai a hannuna igiyar auren take ba? To ba zan saki ba idan kina da ƙarfi ki danne ni ki ƙwata ko ki turo wani ya ƙwatar miki. Ƙaryar banza ƙaryar wofi kawai ni da ke mun sani Halima wlh ba zaki iya rayuwa babu ni ba gara ma ki rufawa kanki asiri mu koma tun lokaci bai ƙure miki ba" ya faɗa cikin fushi bayan daya miƙe tsaye.
Tashi nayi nima ina kallon sa na ce
"Ba dan kar inyi saɓo ba dana tsinewa ƙaddarar data haɗa ni da kai, wlh Bilal ko ban ce komai akanka ba da sannu sai kaga sakayyar butulcin da kayi mun, kaje Allah ya isa tsakanina da kai za kuma ka gani tunda kaƙi sakina ta lallami wahala zata sa ka saki ko baka ƙaunar Allah" na faɗa ina fashewa da kuka na juya zan bar falon dai dai lokacin da Nasir ya shigo da alama hayaniyarmu ta janyo hankalinsa.
"Tsaya Halima, kai Bilal menene haka? Mu da muka zo sulhu kuma zaka ɓige da rashin hankali?" Nasir ɗin ya faɗa. Na coge a tsaye dan ya tare hanyar ina jin Bilal na cewa
"Dallah rabu da ita aikin banza laifi na ne da na zo shiyasa har ta samu damar yi mun wata fuffuka. Na faɗa kuma ba zanyi sakin ba a saka kaina gabas a yanka. Ya ne iyayen naki basuyi su hanaki aure na ba amma kika nace, kina gidana sau nawa suna cewa ki kashe auren kika ƙi, sau nawa kika zaɓe farin ciki na akan nasu sai yanzu ne zaki zo kina wasu maganganu? To ba'a son naki kuma ba za'a sakeki ba kiyi abinda zakiyi. Idan kinga dama ki dawo in ma kin so kiyi ta zama a gidan naku har duniya ta tashi ni ba matsalata bace"
ya nufi ƙofa fuuuu ya bangaje Nasir sai ganin sa mukayi kamar an chillo shi ya dawo baya ya faɗi tim a ƙasa.
[5/12, 9:44 PM] Zainab Madawaki Dahiru: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*