Sashe 5
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mun saba a ƙalla koda yazo zance idan ya tafi kafin kwanciya bacci se munyi doguwar waya har se na fara bacci haka da Asuba shi ze tashe ni amma yau har na gama shirin tafiya makaranta banji wayarsa ba. Dake ban saba ba duk se abin ya dame ni na manta ma da fushin da na farayi hankali na ya sake tashi dana kira layinsa naji a kashe. Gaba ɗaya wunin ranar sururu nayi shi kowa ya ganni seya tambayi ko bani da lafiya ne haka dana dawo ƙarshe kawai nacewa Mama kaina ke ciwo na shige ɗaki naci gaba da kiran wayar Bilal amma har sannan ƙarfe biyar a kashe. Hansa'u na kira dan dama bata shiga makaranta ba ita bayan mun gaisa nace mata tazo dan Allah idan bata komai,
"Wlh lalle aka samun na ɗauka kema zaki zo ai ko kin fasa" ta bani amsa. Shaf na manta gobe za'a fara bikin Zainab dake tunda mukayi faɗa da Hansa'u ta ara ta yafa ni kuma da muka shirya banma bi takanta ba tunda tun asali dama ai shishshigi yasa ta shigarwa ƙawata faɗa bayan munfi kusa. Ko ankon dan dai mun rigada mun siya ne amma da bazan ba.
"Kina ina?" Na tambayeta ta bani amsa da tana gidansu Ummi me lalle se kawai na zura hijabi na Mama na mitar lallen se yamma sakaliya zan tafi me yasa bazan bari se da safe ba tunda bazani makaranta ba nace mata ai baƙi za'a mun ba ja ba. Naji daɗi da na samu Hansa'un ita kaɗai sauran duk an cire musu sun tafi kangon da za'ayi Hennah party, tas na kwashe yanda mukayi dashi jiya na gaya mata ta gama saurarona tayi shiru nace
"Baki ce komai ba"
"To me zance Halima? Ni da kika ce in cire baki na daga sabgarki da Bilal yanzu kuma in ce wani abu ki canza mun ma'ana?" Ta bani amsa. Se nayi tsaki nace
"Ke matsalarki ruƙo wlh ba komai ya rigada ya wuce ba kuma? Dan Allah ki bani shawara me ya kamata nayi? Wlh ji nake kamar nayi ta kurma ihu wlh ko abinci wlh daƙyar na iya shan tea ji nake komai ya tsaya mun"
"Lallai kinyi nisa to Allah ya taro ki" ta faɗa tana cire lallen hannunta. Zanyi magana wayata tayi ƙara, seda na sauke wawiyar ajiyar zuciya kafin na tashi daga kusa da ita inaji tana cewa
"Ai dama kin ƙarasa zubar da ajin ya taka wlh, ai dai Halima kin bada mata Allah ya yafe miki kawai".
Gefe can na koma na amsa, shiru nayi ina jinsa yayi sallama seda ya maimaita sau biyu kafin na amsa.
"Ina kika tafi?" Ya tambayeni kamar wani Babana. Na tura baki nace
"Gidan lalle"
"Ya miki kyau, to gani a ƙofar gida ya za'ayi yunwa nakeji na taso daga aiki naje gida kawai naga wai tuwo Hajja tayi da miyar kuka fa" ya faɗa. Sena rasa me zance masa ma, wato saboda anyi abinda baya ci a gidansu shiyasa ma ya kirani da haka nan ne baze kira ba yake nufi ko me?
"Hello" ya faɗa jin nayi shiru sena sauke ajiyar zuciya nace
"Ina zuwa toh" na miƙe ban ko cewa Hansa'u na tafi ba na wuce gida. Yana jingine jikin lifan ɗin sa kamar kullum cikin gayu irin na yan birni idan ka ganshi da yanayin shigarsa zaka ce ɗan wani hamshaƙin mai kuɗi ne. Wuce shi nayi na gida, ta ƙofar kitchen ta baya na shiga. Muma tuwon mukayi amma da lafiyayyar miyar ɗanyar kuɓewa data ji naman rago. Seda na ɗumama miyar kafin na zuba a flask na ƙulla manshanu a leda da yajin daddawa sannan na shirya komai cikin basket me murfi na haɗa masa da kwalin exotic ɗaya da robar ruwa. Ina zuge basket ɗin Mama ta shigo kitchen ɗin, kallo ɗaya tamun ta girgiza kai kawai ta fita nima sum sum na fice kamar wadda aka kama tayi sata, koda yake satar ma nayi ai.
Tabbacin abinda ya kawo sa kenan ina miƙa masa basket ɗin ya ɗora a gaban mashin ɗin ya hau ba tareda yace mun komai ba ya amsa key ya bar gurin, tsabar mamaki da al'ajabi kawai na bishi da kallo se naji zuciyata ta karye banma sani ba ashe hawaye sun ɓalle mun seda na fara ganin dishi dishi kafin na ankara.
[12/12/2024, 3:31 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 3*
Ranar ina idar da sallar isha'i nayi bacci saboda ɓacin rai seda na farka da asuba sannan naga missed calls ɗin Bilal guda biyu ya kirani tun ƙarfe tara na dare. Duk yanda nake cike da haushin abinda yamun jiya amma haka nan zuciyar dake sonsa ta angiza ni nabi kiran nasa. Murya ƙasa ƙasa muka gaisa ya shaida mun yana masallaci idanya fita ze kirani. Ko yasan ina fushi dashi ne se gashi bayan ya fito masallacin ya kira mun daɗe muna hirar soyayya nan da nan kuma na ware daga fushin na manta da komai. Har Mama seda ta lura da sauyina kan yanda na kwanta jiya na tashi cikin walwala wunin ranar kuwa haka nayi shi ga farin cikin gobe juma'a zamu kammala jarabawa. Safiyar Juma'a tun ƙarfe shida na shirya cikin rigar da mukayi ta graduation. Nayi kyau matuƙa ina kallon kaina a mirror a raina ina yarda da maganar Bilal da yake yawan faɗin ni kyakykyawa ce dukda ba wai ina da irin shahararren kyau ɗin nan bane na fitar hayyaci komai nawa ya dace da zubin halittata I'm just too cute.
Nayi mamakin tarar da Bilal a ƙofar gidanmu ba dan dama yana kaini makaranta idan yana da lokaci amma dake munyi magana na tambayeshi ko zeje mun sign out yace aa shiyasa nayi mamaki dana ganshi jingine jikin mashin ɗinsa yana ta buga mun murmushi. Ina ganin Hansa'u sun taho da Zainab Amarya data rufe fuska da niƙan yau zamuyi final exam kuma yau ne kamun bikinta gobe ɗaurin aure na ɗane Lifan ina ɗaga musu hannu muka wuce. Bilal be tafi ba seda muka fito, shi ya fara mun signing a farar rigata ta sign out muka sha hotuna sannan ya tafi muka cigaba da budurinmu har zuwa ƙarfe sha biyu kafin muka wuce gida.
Jakata kawai na aje na ɗauki yan abubuwan da zanyi amfani dasu nayiwa Mama sallama muka wuce gidan kwalliya dan ma mun kama layi dama ƙawar mu ce me kwalliyar. Kusan mu bakwai mukaje, seda mukayi sallar azahar muka ci awara kafin aka farayi dake mutum biyu ne kafin karfe huɗu ya rage ni da Hansa'u kawai. Muna zaune saurayin Baby Isma'il ya kirata a lokacin ita akeyiwa kwalliyar dan haka ta saka wayar a speaker. Na taɓe baki jin muryar saurayin da take mana kuri dashi, daga muryarsa na hasaso garan ƙauye ne. Uzuri ta bashi akan ana mata make up ne yace
"Zakije kwalliya amma baki gaya mun ba?" Se ta bashi amsa da "kayi haƙuri, munyi magana jiya ai na gaya maka yau kamun Zainab ko ka manta"
"Anyi haka, yanzu a ina kuke kwalliyar na gani ko zan samu zuwa na kaiki gurin bikin?" Ya tambayeta ta gaya masa daga nan sukayi sallama bayan yace ze sako mata kuɗin kwalliyar yanzu. Suna aje wayar ko minti biyu ba'a yi ba wayarta tayi ƙara alamar shigar saƙo, Zulaiha dake ɗaukar hoto da wayar tayi ihu tana nuna tace
"Dubu hamsin ya tura miki" nan suka riki ce da ihu tace
"Duk kunci albarka ci zan biya muku harda amarya" dama kwalliyar tamu 2k ce ta amarya dubu biyar gaba ɗaya in akayi total kuɗin ya kama dubu goma sha uku kenan suka shiga mata godiya ban da ni da seda Hansa'u ta taɓa ni kafin nace nagode.
Ko a jiki na, ba rainawa nayi ba ko hassada nake mata Aa kawai tunda mukayi faɗa da Hansa'u suka bi bayanta shikenan nima naja baya dasu, badan itan bama yanke alaƙa zanyi dasu dan duk wanda ya nuna baya so na da Bilal babu ni babu shi balle kuma naga suna wani fariya akan su samarinsu masu kuɗi ko da zamu taho daga makaranta saurayin Zulaihan ne ya dawo damu tana ta wani kauɗi bayan idan da naga damar kula samari saboda abin hannunsu kaf cikinsu babu wadda ta isa ta goga kafaɗa dani ko a yanzu alhamdulillah babu abinda Abbana be tsare mun ba shiyasa wani abun hannun samari baya burgeni su suka dogara dashi da har suke kula mutanen da kana gani kasan badan so bane ba. Niko Allah ya rufa mun asiri na samu me sona ina sonsa zamu mori ƙuruciyarmu tare.
"Wlh lalle aka samun na ɗauka kema zaki zo ai ko kin fasa" ta bani amsa. Shaf na manta gobe za'a fara bikin Zainab dake tunda mukayi faɗa da Hansa'u ta ara ta yafa ni kuma da muka shirya banma bi takanta ba tunda tun asali dama ai shishshigi yasa ta shigarwa ƙawata faɗa bayan munfi kusa. Ko ankon dan dai mun rigada mun siya ne amma da bazan ba.
"Kina ina?" Na tambayeta ta bani amsa da tana gidansu Ummi me lalle se kawai na zura hijabi na Mama na mitar lallen se yamma sakaliya zan tafi me yasa bazan bari se da safe ba tunda bazani makaranta ba nace mata ai baƙi za'a mun ba ja ba. Naji daɗi da na samu Hansa'un ita kaɗai sauran duk an cire musu sun tafi kangon da za'ayi Hennah party, tas na kwashe yanda mukayi dashi jiya na gaya mata ta gama saurarona tayi shiru nace
"Baki ce komai ba"
"To me zance Halima? Ni da kika ce in cire baki na daga sabgarki da Bilal yanzu kuma in ce wani abu ki canza mun ma'ana?" Ta bani amsa. Se nayi tsaki nace
"Ke matsalarki ruƙo wlh ba komai ya rigada ya wuce ba kuma? Dan Allah ki bani shawara me ya kamata nayi? Wlh ji nake kamar nayi ta kurma ihu wlh ko abinci wlh daƙyar na iya shan tea ji nake komai ya tsaya mun"
"Lallai kinyi nisa to Allah ya taro ki" ta faɗa tana cire lallen hannunta. Zanyi magana wayata tayi ƙara, seda na sauke wawiyar ajiyar zuciya kafin na tashi daga kusa da ita inaji tana cewa
"Ai dama kin ƙarasa zubar da ajin ya taka wlh, ai dai Halima kin bada mata Allah ya yafe miki kawai".
Gefe can na koma na amsa, shiru nayi ina jinsa yayi sallama seda ya maimaita sau biyu kafin na amsa.
"Ina kika tafi?" Ya tambayeni kamar wani Babana. Na tura baki nace
"Gidan lalle"
"Ya miki kyau, to gani a ƙofar gida ya za'ayi yunwa nakeji na taso daga aiki naje gida kawai naga wai tuwo Hajja tayi da miyar kuka fa" ya faɗa. Sena rasa me zance masa ma, wato saboda anyi abinda baya ci a gidansu shiyasa ma ya kirani da haka nan ne baze kira ba yake nufi ko me?
"Hello" ya faɗa jin nayi shiru sena sauke ajiyar zuciya nace
"Ina zuwa toh" na miƙe ban ko cewa Hansa'u na tafi ba na wuce gida. Yana jingine jikin lifan ɗin sa kamar kullum cikin gayu irin na yan birni idan ka ganshi da yanayin shigarsa zaka ce ɗan wani hamshaƙin mai kuɗi ne. Wuce shi nayi na gida, ta ƙofar kitchen ta baya na shiga. Muma tuwon mukayi amma da lafiyayyar miyar ɗanyar kuɓewa data ji naman rago. Seda na ɗumama miyar kafin na zuba a flask na ƙulla manshanu a leda da yajin daddawa sannan na shirya komai cikin basket me murfi na haɗa masa da kwalin exotic ɗaya da robar ruwa. Ina zuge basket ɗin Mama ta shigo kitchen ɗin, kallo ɗaya tamun ta girgiza kai kawai ta fita nima sum sum na fice kamar wadda aka kama tayi sata, koda yake satar ma nayi ai.
Tabbacin abinda ya kawo sa kenan ina miƙa masa basket ɗin ya ɗora a gaban mashin ɗin ya hau ba tareda yace mun komai ba ya amsa key ya bar gurin, tsabar mamaki da al'ajabi kawai na bishi da kallo se naji zuciyata ta karye banma sani ba ashe hawaye sun ɓalle mun seda na fara ganin dishi dishi kafin na ankara.
[12/12/2024, 3:31 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 3*
Ranar ina idar da sallar isha'i nayi bacci saboda ɓacin rai seda na farka da asuba sannan naga missed calls ɗin Bilal guda biyu ya kirani tun ƙarfe tara na dare. Duk yanda nake cike da haushin abinda yamun jiya amma haka nan zuciyar dake sonsa ta angiza ni nabi kiran nasa. Murya ƙasa ƙasa muka gaisa ya shaida mun yana masallaci idanya fita ze kirani. Ko yasan ina fushi dashi ne se gashi bayan ya fito masallacin ya kira mun daɗe muna hirar soyayya nan da nan kuma na ware daga fushin na manta da komai. Har Mama seda ta lura da sauyina kan yanda na kwanta jiya na tashi cikin walwala wunin ranar kuwa haka nayi shi ga farin cikin gobe juma'a zamu kammala jarabawa. Safiyar Juma'a tun ƙarfe shida na shirya cikin rigar da mukayi ta graduation. Nayi kyau matuƙa ina kallon kaina a mirror a raina ina yarda da maganar Bilal da yake yawan faɗin ni kyakykyawa ce dukda ba wai ina da irin shahararren kyau ɗin nan bane na fitar hayyaci komai nawa ya dace da zubin halittata I'm just too cute.
Nayi mamakin tarar da Bilal a ƙofar gidanmu ba dan dama yana kaini makaranta idan yana da lokaci amma dake munyi magana na tambayeshi ko zeje mun sign out yace aa shiyasa nayi mamaki dana ganshi jingine jikin mashin ɗinsa yana ta buga mun murmushi. Ina ganin Hansa'u sun taho da Zainab Amarya data rufe fuska da niƙan yau zamuyi final exam kuma yau ne kamun bikinta gobe ɗaurin aure na ɗane Lifan ina ɗaga musu hannu muka wuce. Bilal be tafi ba seda muka fito, shi ya fara mun signing a farar rigata ta sign out muka sha hotuna sannan ya tafi muka cigaba da budurinmu har zuwa ƙarfe sha biyu kafin muka wuce gida.
Jakata kawai na aje na ɗauki yan abubuwan da zanyi amfani dasu nayiwa Mama sallama muka wuce gidan kwalliya dan ma mun kama layi dama ƙawar mu ce me kwalliyar. Kusan mu bakwai mukaje, seda mukayi sallar azahar muka ci awara kafin aka farayi dake mutum biyu ne kafin karfe huɗu ya rage ni da Hansa'u kawai. Muna zaune saurayin Baby Isma'il ya kirata a lokacin ita akeyiwa kwalliyar dan haka ta saka wayar a speaker. Na taɓe baki jin muryar saurayin da take mana kuri dashi, daga muryarsa na hasaso garan ƙauye ne. Uzuri ta bashi akan ana mata make up ne yace
"Zakije kwalliya amma baki gaya mun ba?" Se ta bashi amsa da "kayi haƙuri, munyi magana jiya ai na gaya maka yau kamun Zainab ko ka manta"
"Anyi haka, yanzu a ina kuke kwalliyar na gani ko zan samu zuwa na kaiki gurin bikin?" Ya tambayeta ta gaya masa daga nan sukayi sallama bayan yace ze sako mata kuɗin kwalliyar yanzu. Suna aje wayar ko minti biyu ba'a yi ba wayarta tayi ƙara alamar shigar saƙo, Zulaiha dake ɗaukar hoto da wayar tayi ihu tana nuna tace
"Dubu hamsin ya tura miki" nan suka riki ce da ihu tace
"Duk kunci albarka ci zan biya muku harda amarya" dama kwalliyar tamu 2k ce ta amarya dubu biyar gaba ɗaya in akayi total kuɗin ya kama dubu goma sha uku kenan suka shiga mata godiya ban da ni da seda Hansa'u ta taɓa ni kafin nace nagode.
Ko a jiki na, ba rainawa nayi ba ko hassada nake mata Aa kawai tunda mukayi faɗa da Hansa'u suka bi bayanta shikenan nima naja baya dasu, badan itan bama yanke alaƙa zanyi dasu dan duk wanda ya nuna baya so na da Bilal babu ni babu shi balle kuma naga suna wani fariya akan su samarinsu masu kuɗi ko da zamu taho daga makaranta saurayin Zulaihan ne ya dawo damu tana ta wani kauɗi bayan idan da naga damar kula samari saboda abin hannunsu kaf cikinsu babu wadda ta isa ta goga kafaɗa dani ko a yanzu alhamdulillah babu abinda Abbana be tsare mun ba shiyasa wani abun hannun samari baya burgeni su suka dogara dashi da har suke kula mutanen da kana gani kasan badan so bane ba. Niko Allah ya rufa mun asiri na samu me sona ina sonsa zamu mori ƙuruciyarmu tare.