Sashe 141
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun daga sanda ta tabbatar da yayi blocking ɗin ta ta gasgata abinda zuciyarta ta daɗe tana raya mata akan Bilal yana so yayi amfani da ita ne kawai ya cimma burinsa sannan ya watsar da ita kamar yanda ya yiwa matarsa Halima. Harga Allah da aure take son Bilal dukda banbancin matsayi da yake tsakaninsu amma da yake shi So babu ruwansa da wannan tunda ta ganshi taji yayi mata, tayi masa uzuri a lokacin daya nuna mata cewar ba zai iya aurenta ba wannan dalilin ya saka ta buɗe masa bakin aljihunta a ganinta rashin wadatace ta saka yace ba zai aureta ɗin a lokacin ba amma a maimakon aure sai ya bijiro mata da abinda take ƙoƙarin bari harta yanke hukuncin auren nasa.
Tabbas Bilal shi ya fara nemar su ƙulla alaƙa ba kuma tayi musu ba ta biye masa, irin yanda kuma yake tafi da ita da jin daɗin da yake bata ya saka bata ƙyashi yi masa komai dashi da mahaifiyarsa da tun haɗuwar farko ta fahimci ƙwadayyace kuma a gurinta Bilal ɗin yayi gadon ƙwadayi.
Sau tari zuciyarta ta kan raya mata tarayyarsu bata gaskiya bace yana binta ne domin cikar buri tamkar yanda ya yiwa matarsa Halima har wasu lokutan ta kan yi yunƙurin datse alaƙar amma sai ta kasa, daga ƙarshe ta yaƙi kanta ta kuma tilastawa kanta yarda dashi da amincewa da duk zancen daya zo mata dashi wanda sau da yawa ta kan tuhumin kanta akan hakan, abinda ta yarda dashi Bilal ɗin yana da wata baiwa ta iya yaudara da asirce zuciyar mace shiyasa ko da ace tayi niyyar yaƙar zuciyarta ta rabu dashi sai ta kasa.
A karo na biyu ta sake bijiro masa da maganar aure wanda wani babban dalili ya janyo hakan ta kuma bashi sharaɗin idan har zai aureta toh fa sai dai ya rabu da matarsa wanda bai musa hakan ba kuma ya amince har suka fara shirye-shirye.
Ta siyi gida wanda tayi niyyar mallaka masa ya sakata a ciki idan sunyi aure, shagunan da Mamanta ta siya mata su kansu shi taso ta mallakawa domin tana so ya tsaya da ƙafarsa idan sunyi aure bata so ya zamana ita zata cigaba da ɗaukar ɗawainiyarsa.
A hannun Hafiz ta siyi gidan kuma a lokacin ta faɗa masa alaƙar da take tsakaninta da Bilal harda matsayin da suke kai a lokacin, batayi mamaki yanda Hafiz ɗin yace mata ya sani ba domin alaƙarta da Bilal a bayyane take. A lokacin ya ce mata
"Ki kula dai domin KURA A RUMBU, ABAR TSORO CE" bata damu ba dan bata ma san ma'anar karin maganar ba, sanda ya bata takardun gidan data shaida masa Bilal ta siyawa, a lokacin ne ya ce mata
"Yanzu bakya tsoron duk bayan kin gama kyautata masa ya guje ki tamkar yanda yayiwa matarsa? Jalilah Bilal ba mutumin kirki bane na shaida hakan, ta silata kika sanshi, daga sanda kika buɗe masa ido da kuɗi na zama mara amfani a gurinsa kamar yanda ya wulaƙanta matarsa, ina baki tabbacin kema haka zai watsar da ke da zarar ya samu wadda ta fiki dan haka kiyiwa kanki tunani. Bance mutum baya canzawa ba, ta yuwu dagaske yake sonki kuma ba zai butulce miki ba amma kada ki zura jiki domin duk alkhairin da kikayi masa ba zai kai wanda matarsa tayi masa ba kuma daga ƙarshe ya saka ƙafa ya tankwaɓe"
Ganin da Halima tayi musu a gidansa ya sakw tabbatar mata da tabbas Bilal ɗin ba mutum bane domin bata tsammaci bayan hakan kunya da nauyin matarsa zai bari ya cigaba da wata alaƙa da ita ba sai gashi a daren ranar ma sai da yaje gurinta, ta ringa hasaso ace ita ce Haliman a lokacin tabbas babu abinda zai hana ta kulle ƙofa ta kunna musu wuta sai dai duk abinda zai faru ya faru amma a maimakon haka sai kawai ta juya ta fita tana kuka wannan al'amarin ya saka ta canza niyyarta ta aurensa domin kuwa ta tabbatarwa da kanta Bilal ɗin ba miji bane kamar kuma yanda Hafiz ya sha faɗa zai iya aikata komai akan kuɗi.
Da wannan ta wuce Dubai a lokacin kuma har ranta ta yanke rabuwa dashi ta gaske. Ita sam bata ma ankare da yayi blocking ɗinta ba dan bata nemeshi ba sai da aka kwana biyu kawai Hafiz ya kirata yana gaya mata wai Bilal ya siyar da gida. A lokacin ta sake tsinkewa da lamarinsa, dukda kafin ta taho dama ta fara zargin wani abu akan zancen renovation data bashi kuɗi ayi amma da yake ta mata hanya-hanya tunaninta sai ya tafi akan ya kashe kuɗin ne kawai ba'ayi aikin ba ashe shi mai ɗungurungun yayi ya siyar da gidan.
Ta jinjinawa basirar Hafiz daya shaida mata takardun hannun Bilal fake ne, yayi zargin haka kuma ya sani idan ya gaya mata ba zata yarda ba shiyasa yayi shiru ya barta taga abinda yake haska mata da kanta.
A lokacin dukda Hafiz ya ce karta nuna masa komai amma ta kasa, ta ringa nemansa ta duk wata kafa amma ta gagara samunsa, ya rufe layinta kuma idan ta kira da wata number suma basa shiga alamar nan ma ya toshe kira ba zai shiga wayarsa da lambar da bai yi saving ba.
A haka labarin sakin Halima da auren da yayi tun tana Nigeria ya sake riskarta. Da kuɗinta ya auro wata ya siyi gida da kuɗin gidanta zai sakata a ciki, bata gama warkewa daga wannan shock ɗin ba Hafiz ya sake kiranta wai Bilal ya kai masa tallan shagunanta, ta shiga tambayar kanta a ina ya samu takardun shagunan? Domin dai bata bashi ba. Ta birkice ƙaramar akwatinta wacce takaddun suke ciki nan suka ce ta ɗauke su in da ta ajiye hakan kuma ya ankarar da ita tabbas ɗauka yayi, yanzu da ba Hafiz ɗin ya kaiwa ba shikenan ya dirata da ka bata ci ba bata sha ba.
Ta daɗe tana lissafa ta inda ya kamata ta rama, yana ɗaukar kansa mai wayau ya kamata ta koya masa hankali ta muna masa wayon banza gareshi lissafinsa kuma ba daidai yake tafiya ba. Akan haka ta shirya dawowa, ta hillaceshi da abinda ta san ba zai kaucewa ba wato kuɗi sai gashi kuwa yayi unblocking ɗinta da kansa.
Abu na farko data farayi shine siyar da gidan daya rigada ya ci kuɗinsa ga tsohon abokin harkarta Ahlan. Abinda ya rabasu shi ɗin ya fiya tsalle-tsalle sannan kuma yana shan giya, ita kuma duk namijin da zata kula ta fi so ya zama ita take da iko dashi shiyasa tafi harka da waɗanda tafi kuɗi a yanda zata ringa juyasu yanda take so. Ahlan matashi ne da yake cikin late thirties ɗin sa, yana da kuɗi sosai yana kuma kashewa mata su tamkar a bishiya yake tsinkosu. Tantiri ne na gaske, ko bunsuru albarka a neman mata.
A hanyar dawowa suka haɗu a jirgi hira tayi hira yake bata labarin wata yarinya mai shegen taurin kai daya haɗu da ita yayi yayi taƙi bashi haɗin kai shi kuma ya rantse tunda yawunsa ya tsinke sai ya ɗanɗana dan haka yanzu ya yanke shawara zai aureta daya samu biyan buƙatarsa ya saita mata hanya. Tana jin haka tace masa ai kuwa tana da gida na siyarwa, da farko ya ce mata Aa, auren da ba zai wuce na kwana ɗaya ba da an ɗaura zai fanshe kuɗinsa ya saita mata hanya sai kuma bayan kwana biyu da yin haka ya kira wai yana son gidan ba wani ja in ja ya tura mata kuɗinta ya karɓi Original takardu a hannun Hafiz.
Wani abin al'ajabi kuma bayan sun bar gidan Bilal ɗin tana duba status taci karo dana ɗaurin auren Ahlan, kawai ta fashe da dariya ba shiri ganin wacece Amaryar, Fadila fa ƙanwar Bilal lallai sata ta saci sata.
[5/28, 11:06 PM] Hauwa Galadima: ❤️ *ƊANLARABAWA INVESTMENT! Kyau Da Ƙima A Hannunku!* ❤️
*Ku sauka lafiya zuwa masarautar ƙayatarwa!* 👑
*ƊANLARABAWA INVESTMENT* na kawo muku:
*Atamfofi masu kyau na zamani*
*Shaddodi da Laces masu ɗaukar ido*
*Takalma & Jakunkuna masu ladabi da ƙima*
*Hijabai, mayafai da dogwayen riguna masu salon zamani*
*Yari da sarƙa da kayan ado masu ban sha’awa*
*Akwatuna masu kyau don tafiya ko haɗa lefe*
*Turaruka masu ƙamshi da kayan kwalliya na garari*
*Nau'in kayan kicin na alfarma da kayan ɗaki*
*Zannuwan gado da labulaye na kashe kala*
*Da dai sauran su*
*Muna tura kayanmu ko'ina a fadin Nijeriya da ƙasashen ƙetare. Cikin mutuntaka da cika alƙawari in sha Allah*
*Location: Kano, Ƙofar Waika, Layin Malam Sani Shawus.*
*Lambar waya domin tuntuɓa*: 08080049548
*Ko ku shiga zaurenmu na manhajar WatsApp ta wannan link kamar haka:*
https://chat.whatsapp.com/Loht5sGuLJO3LXYE9OkqNs
*Za ku more da kallon kayayyaki na ƙawa bisa ingantaccen farashi da rahusa mai kama da kyauta. Sayen nagari, mayar da kuɗi gida.*
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 57*
BILAL
Yana kwance a gida Hajja ta kirashi wai ya kawo musu kayan miyan da za'ayi tuwon ɗaurin auren Fadila da za'a ɗaura a gobe Juma'a. Da yake a tsini suke yayi mata laifi shiyasa bai musa ba ya tashi ya tafi kasuwar Yankaba ya yiwo musu cefanen ya tafi ya kai. Zagayewa yayi yaje ya samu Kawu Ɗayyabu, Yayan Hajja ne da suke uba ɗaya da yake mutum ne mara ɗaukar raini shiyasa duk rashin mutunchin Hajjan take shakkarsa ko da wasa kuma bata bari wani abu ya gilma a tsakaninsu shi Bilal ɗin yaje ya samu ya gaya masa zancen auren Fadilan da yanda ita da Hajja suke shirya komai basu saka kowa a ciki ba.
Tabbas Bilal shi ya fara nemar su ƙulla alaƙa ba kuma tayi musu ba ta biye masa, irin yanda kuma yake tafi da ita da jin daɗin da yake bata ya saka bata ƙyashi yi masa komai dashi da mahaifiyarsa da tun haɗuwar farko ta fahimci ƙwadayyace kuma a gurinta Bilal ɗin yayi gadon ƙwadayi.
Sau tari zuciyarta ta kan raya mata tarayyarsu bata gaskiya bace yana binta ne domin cikar buri tamkar yanda ya yiwa matarsa Halima har wasu lokutan ta kan yi yunƙurin datse alaƙar amma sai ta kasa, daga ƙarshe ta yaƙi kanta ta kuma tilastawa kanta yarda dashi da amincewa da duk zancen daya zo mata dashi wanda sau da yawa ta kan tuhumin kanta akan hakan, abinda ta yarda dashi Bilal ɗin yana da wata baiwa ta iya yaudara da asirce zuciyar mace shiyasa ko da ace tayi niyyar yaƙar zuciyarta ta rabu dashi sai ta kasa.
A karo na biyu ta sake bijiro masa da maganar aure wanda wani babban dalili ya janyo hakan ta kuma bashi sharaɗin idan har zai aureta toh fa sai dai ya rabu da matarsa wanda bai musa hakan ba kuma ya amince har suka fara shirye-shirye.
Ta siyi gida wanda tayi niyyar mallaka masa ya sakata a ciki idan sunyi aure, shagunan da Mamanta ta siya mata su kansu shi taso ta mallakawa domin tana so ya tsaya da ƙafarsa idan sunyi aure bata so ya zamana ita zata cigaba da ɗaukar ɗawainiyarsa.
A hannun Hafiz ta siyi gidan kuma a lokacin ta faɗa masa alaƙar da take tsakaninta da Bilal harda matsayin da suke kai a lokacin, batayi mamaki yanda Hafiz ɗin yace mata ya sani ba domin alaƙarta da Bilal a bayyane take. A lokacin ya ce mata
"Ki kula dai domin KURA A RUMBU, ABAR TSORO CE" bata damu ba dan bata ma san ma'anar karin maganar ba, sanda ya bata takardun gidan data shaida masa Bilal ta siyawa, a lokacin ne ya ce mata
"Yanzu bakya tsoron duk bayan kin gama kyautata masa ya guje ki tamkar yanda yayiwa matarsa? Jalilah Bilal ba mutumin kirki bane na shaida hakan, ta silata kika sanshi, daga sanda kika buɗe masa ido da kuɗi na zama mara amfani a gurinsa kamar yanda ya wulaƙanta matarsa, ina baki tabbacin kema haka zai watsar da ke da zarar ya samu wadda ta fiki dan haka kiyiwa kanki tunani. Bance mutum baya canzawa ba, ta yuwu dagaske yake sonki kuma ba zai butulce miki ba amma kada ki zura jiki domin duk alkhairin da kikayi masa ba zai kai wanda matarsa tayi masa ba kuma daga ƙarshe ya saka ƙafa ya tankwaɓe"
Ganin da Halima tayi musu a gidansa ya sakw tabbatar mata da tabbas Bilal ɗin ba mutum bane domin bata tsammaci bayan hakan kunya da nauyin matarsa zai bari ya cigaba da wata alaƙa da ita ba sai gashi a daren ranar ma sai da yaje gurinta, ta ringa hasaso ace ita ce Haliman a lokacin tabbas babu abinda zai hana ta kulle ƙofa ta kunna musu wuta sai dai duk abinda zai faru ya faru amma a maimakon haka sai kawai ta juya ta fita tana kuka wannan al'amarin ya saka ta canza niyyarta ta aurensa domin kuwa ta tabbatarwa da kanta Bilal ɗin ba miji bane kamar kuma yanda Hafiz ya sha faɗa zai iya aikata komai akan kuɗi.
Da wannan ta wuce Dubai a lokacin kuma har ranta ta yanke rabuwa dashi ta gaske. Ita sam bata ma ankare da yayi blocking ɗinta ba dan bata nemeshi ba sai da aka kwana biyu kawai Hafiz ya kirata yana gaya mata wai Bilal ya siyar da gida. A lokacin ta sake tsinkewa da lamarinsa, dukda kafin ta taho dama ta fara zargin wani abu akan zancen renovation data bashi kuɗi ayi amma da yake ta mata hanya-hanya tunaninta sai ya tafi akan ya kashe kuɗin ne kawai ba'ayi aikin ba ashe shi mai ɗungurungun yayi ya siyar da gidan.
Ta jinjinawa basirar Hafiz daya shaida mata takardun hannun Bilal fake ne, yayi zargin haka kuma ya sani idan ya gaya mata ba zata yarda ba shiyasa yayi shiru ya barta taga abinda yake haska mata da kanta.
A lokacin dukda Hafiz ya ce karta nuna masa komai amma ta kasa, ta ringa nemansa ta duk wata kafa amma ta gagara samunsa, ya rufe layinta kuma idan ta kira da wata number suma basa shiga alamar nan ma ya toshe kira ba zai shiga wayarsa da lambar da bai yi saving ba.
A haka labarin sakin Halima da auren da yayi tun tana Nigeria ya sake riskarta. Da kuɗinta ya auro wata ya siyi gida da kuɗin gidanta zai sakata a ciki, bata gama warkewa daga wannan shock ɗin ba Hafiz ya sake kiranta wai Bilal ya kai masa tallan shagunanta, ta shiga tambayar kanta a ina ya samu takardun shagunan? Domin dai bata bashi ba. Ta birkice ƙaramar akwatinta wacce takaddun suke ciki nan suka ce ta ɗauke su in da ta ajiye hakan kuma ya ankarar da ita tabbas ɗauka yayi, yanzu da ba Hafiz ɗin ya kaiwa ba shikenan ya dirata da ka bata ci ba bata sha ba.
Ta daɗe tana lissafa ta inda ya kamata ta rama, yana ɗaukar kansa mai wayau ya kamata ta koya masa hankali ta muna masa wayon banza gareshi lissafinsa kuma ba daidai yake tafiya ba. Akan haka ta shirya dawowa, ta hillaceshi da abinda ta san ba zai kaucewa ba wato kuɗi sai gashi kuwa yayi unblocking ɗinta da kansa.
Abu na farko data farayi shine siyar da gidan daya rigada ya ci kuɗinsa ga tsohon abokin harkarta Ahlan. Abinda ya rabasu shi ɗin ya fiya tsalle-tsalle sannan kuma yana shan giya, ita kuma duk namijin da zata kula ta fi so ya zama ita take da iko dashi shiyasa tafi harka da waɗanda tafi kuɗi a yanda zata ringa juyasu yanda take so. Ahlan matashi ne da yake cikin late thirties ɗin sa, yana da kuɗi sosai yana kuma kashewa mata su tamkar a bishiya yake tsinkosu. Tantiri ne na gaske, ko bunsuru albarka a neman mata.
A hanyar dawowa suka haɗu a jirgi hira tayi hira yake bata labarin wata yarinya mai shegen taurin kai daya haɗu da ita yayi yayi taƙi bashi haɗin kai shi kuma ya rantse tunda yawunsa ya tsinke sai ya ɗanɗana dan haka yanzu ya yanke shawara zai aureta daya samu biyan buƙatarsa ya saita mata hanya. Tana jin haka tace masa ai kuwa tana da gida na siyarwa, da farko ya ce mata Aa, auren da ba zai wuce na kwana ɗaya ba da an ɗaura zai fanshe kuɗinsa ya saita mata hanya sai kuma bayan kwana biyu da yin haka ya kira wai yana son gidan ba wani ja in ja ya tura mata kuɗinta ya karɓi Original takardu a hannun Hafiz.
Wani abin al'ajabi kuma bayan sun bar gidan Bilal ɗin tana duba status taci karo dana ɗaurin auren Ahlan, kawai ta fashe da dariya ba shiri ganin wacece Amaryar, Fadila fa ƙanwar Bilal lallai sata ta saci sata.
[5/28, 11:06 PM] Hauwa Galadima: ❤️ *ƊANLARABAWA INVESTMENT! Kyau Da Ƙima A Hannunku!* ❤️
*Ku sauka lafiya zuwa masarautar ƙayatarwa!* 👑
*ƊANLARABAWA INVESTMENT* na kawo muku:
*Atamfofi masu kyau na zamani*
*Shaddodi da Laces masu ɗaukar ido*
*Takalma & Jakunkuna masu ladabi da ƙima*
*Hijabai, mayafai da dogwayen riguna masu salon zamani*
*Yari da sarƙa da kayan ado masu ban sha’awa*
*Akwatuna masu kyau don tafiya ko haɗa lefe*
*Turaruka masu ƙamshi da kayan kwalliya na garari*
*Nau'in kayan kicin na alfarma da kayan ɗaki*
*Zannuwan gado da labulaye na kashe kala*
*Da dai sauran su*
*Muna tura kayanmu ko'ina a fadin Nijeriya da ƙasashen ƙetare. Cikin mutuntaka da cika alƙawari in sha Allah*
*Location: Kano, Ƙofar Waika, Layin Malam Sani Shawus.*
*Lambar waya domin tuntuɓa*: 08080049548
*Ko ku shiga zaurenmu na manhajar WatsApp ta wannan link kamar haka:*
https://chat.whatsapp.com/Loht5sGuLJO3LXYE9OkqNs
*Za ku more da kallon kayayyaki na ƙawa bisa ingantaccen farashi da rahusa mai kama da kyauta. Sayen nagari, mayar da kuɗi gida.*
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 57*
BILAL
Yana kwance a gida Hajja ta kirashi wai ya kawo musu kayan miyan da za'ayi tuwon ɗaurin auren Fadila da za'a ɗaura a gobe Juma'a. Da yake a tsini suke yayi mata laifi shiyasa bai musa ba ya tashi ya tafi kasuwar Yankaba ya yiwo musu cefanen ya tafi ya kai. Zagayewa yayi yaje ya samu Kawu Ɗayyabu, Yayan Hajja ne da suke uba ɗaya da yake mutum ne mara ɗaukar raini shiyasa duk rashin mutunchin Hajjan take shakkarsa ko da wasa kuma bata bari wani abu ya gilma a tsakaninsu shi Bilal ɗin yaje ya samu ya gaya masa zancen auren Fadilan da yanda ita da Hajja suke shirya komai basu saka kowa a ciki ba.