← Book details Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 158

Sashe 68

Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ungo ɗanki mun gaji" na karɓe shi na koma ciki. Ina tsaka da shayar da shi Mama ta shigo ɗakin da tafasasshen ruwa a bokiti ta ajiye ta sake fita ta dawo da baho. Wanka ta masa da ruwa masu ɗan banzan zafi ya ringa canyara kuka fatar jikin za ta yi jajir har ƙwalla na yi ita kuwa ko a jikin ta, kafin ta gama shirya shi ya yi bacci. Ta kwantar da shi tana cewa
"Yanzu Fauziyya ta kira waya ta ji kukan sa shine Baba Jummai ta ce duk yanda aka yi wanka ne ba'a masa ba ko kuma ruwan babu zafi yanda ya saba ji"

"Amma fa Mama likitoci sun ce a dena saka musu ruwa me zafi sosai wankan yammar ma su suka ce a dena masa ai" na faɗa ba tare da na kalle ta ba. Ta harare ni ta ce
"Da ruwan zafin na kisa da baki girma kin kawo yanzu har kin haife shi ba, ni tun jiyan ma sha'afa na yi kema haka kika ringa mana wannan kukan sai da Goggo Habi ta zo ta fara gasa ki haka sannan muka samu lafiya to irin ƙashin ki ya gado, kuma na ga har yanzu idan kika gaji in ba kinyi wankan da ruwa mai zafi ba bakya iya bacci".

Shiru na yi dan gaskiya ta faɗa, da na taho na ce na yada wanka amma tun jiyan da jikina ya fara gaya mun babu wanda ya tuna mun na saka Zainab ta ɗora mun ruwa a gas ɗin waje na girkin sallah yana tafasa na cewa Mama ruwa ya tafasa ta saka aka tsinko ganye a waje ta mun wankan sannan na ji daidai a jiki na.

Cikin bacci na ji kamar waya ta tana ƙara, ido a rufe na laluba na janyo ta daga ƙasan pillow da nake kai. 'My world' da na gani ya saka na wartsake ba shiri na tashi zaune. Sai da ta katse ya sake kira, wani ɓangare na zuciya ta na hanani da in amsa wayar amma gefen dake cike da bege da kewar sa ta ingizani na danna.

"Fushi dai har yanzu My Halims" ya faɗa cikin wani sauti da ya sakani sakin ajiyar zuciya ba tare da na shirya ba, ban amsa shi ba na yi shiru. Ya yi murmushi mai sauti da na ji har ƙasan zuciya ta kafin ya ce
"Allah ya huci zuciyar Hali dubu fitila mai haska duniyar Bilal".

Da sauri na toshe baki na saboda murmushin da ke shirin kufce mun, kamar ya ji ya ce
"Nasan dariya kike yi, ni dama na sani ba zaki iya dogon fushi da ni ba".

"Oh, haka ma ka ce?" Na faɗa a shagwaɓe, ya ce
"Yes, na shaida kina So na, masoyi kuma baya fushi da abin ƙaunar sa ai".
"Hmmm, da wannan kake fakewa kenan kana mun duk abinda kaga dama tunda ka san ina son ka" na faɗa cikin karyewar sauti, so na ke ya ce mun ba haka ba ne, ya bani amsar da zata shafe maganganun Anty Labiba amma maimakon haka sai ya canza maganar da cewa

"Tun jiya baki kira kin ji ya na sauka ba, ina Al'amin? Ya ji daɗin gadon Mama ya dena kukan banza ko?"

Kasa ce masa komai na yi shima bai damu ba ya sake cewa
"Ɗazu Oga Hafiz ya ke ce mun sun zo tare da Madam sun kawo muku tsarabar Finland, Al'amin ya sha kaya na sa ni" ya faɗi ainihin dalilin kiran wayar, sai na saki murmushin takaici na cije leɓe na na ce
"Ai kuwa dai, sun zo, sun kawo masa kaya ya kuma gode dama abin da ka kira ka tambaya kenan?"

"Kamar ya ya abinda na kira na tambaya kenan haka na ce miki? Ai ke ya kamata ma ki kira ni tun sanda suka zo ɗin ki gaya mun ba wai ki jira sai ni na kira ki ba. Kuma ni ba dalilin da ya saka na kira ki ba kenan saboda ina so naji muryar ki ne tunda kin fara ɗaukar zugar mutane kin canza hali".

"Bacci na ke ji zamu yi magana da safe idan Allah ya kaimu" na faɗa saboda wani yanayi da naji yana taso mun na san a kowanne lokaci zan iya fashewa da kuka. Yayi shiru kafin ya ce
"Shikenan, Allah ya tashe mu lafiya" ya katse wayar ba tareda ya tsaya ya tambaye ni me yake damuna ko ya lallashe ni ba. Kife kaina nayi a pillow na fashe da kukan da takamimai ban san dalilin yin sa ba.

[2/21, 3:13 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*

*PAGE 28*

Washe gari da wuri na fara haɗa kayan mu dan komawa gidan Anty Labiba duk da jirgin dare su Mama zasu bi amma da wuri nake so na tafi can ɗin dan ko rakiya ba zan tsaya yi musu ba. Gaba ɗaya raina babu daɗi na tashi, na ɗauka Bilal zai sake kira na daga baya ko kuma da asuba amma shiru. Ina zuge akwatin kaya na Zainab ta shigo ta ce mun na zo na yi baƙi, na ɗora mayafin doguwar rigar yadin jiki na ina ƙoƙarin kawar da ɓacin ran dake kwance akan fuskata na fita falon.

Turus na yi a bakin ƙofa ganin Fadila da wata mata da na ga suna yanayin kama sai kuma wata tsohuwa da ita ma ban gama tantance fuskarta ba. Sake tattaro fushin dana ɗauke a kan fuskata na yi na maido da shi na ƙarasa da sallama ciki ciki. Da "ina kwana" na gaishe su baki ɗaya matar ta amsa fuskar ta ɗauke da fara'a Fadila kuma ta gaishe ni baki a kumbure kamar an mata dole. Sai bayan na zauna na gane tsohuwar Lanti ce wacce suka je gida na tare da Hajja har suka yi faɗa da Baba Jummai.

Kamar dole Fadilan ta ce
"Dama Anty Sa'adatu ce ta zo shine Hajja ta ce a rakota ta ga Aminu". Na watsa mata wani kallo jin yanda ta ambaci Aminun garangatsau kana ji kasan da rashin mutunchi ta yi abun dama, matar ta harare ta ta ce
"Haka ake kiran sa dama?"
"Sunan sa kenan ai Anty" ta bata amsa tana ƙoƙarin sakko yaron ta daga baya. Girgiza kai kawai na yi a raina ina takaicin sakewa yarinyar tun farko, da nasan haka take bata da mutunchi da wlh bata isa na mata abubuwan da na mata a baya ba. Mayafin da ke jikin ta ma nawa ne daga aro na ma manta da shi sai yanzun tun da mukayi aure hatta da plates da cups sai da na ƙara mata a cikin nawa da muka je gidan ta naga duk tarkace ne natan ba wasu na ƙwarai ba ni a ganina an zama ɗaya ina da su har sun mun yawa na ɗibar mata amma tun daga zuwan da ta mana ta tafi ta ƙulla mun sharri ta fita a kaina ita ma kuma ta dena ɓoye ɓoye ta fito mun a asalin halin ta yanzu.

"Ina maigidan nawa ne ko bacci ya ke yi?" Matar ta katse mun tunani, na ji kamar na ce mata Eh baccin yake kuma ba za'a ɗakko shi ba amma hakan sai ta mun kwarjini dan haka na miƙe na wuce falon Abba bayan na ce mata bari na karɓo shi.

Sai bayan da Mama ta fito kafin Fadila da Lanti suka gabatar mata da matar da suka zo tare a matsayin ƙanwar Hajja ta Jos, dama ni ɗaki kom na cigaba da abinda nake yi. A ɗakin Fadila ta tarar dani, ban ko ɗaga kai na kalle ta daga danna wayar da nake yi ba. Ta gama kalle kallenta kamar tayi ajiyar wani abu kafin ta ceygg
"Hajja ta ce idan mun zo ki nuna mun kayan da Yaya Hafiz ya kawo muku".

Ban ko yi motsin da zai nuna mata alamar na ji me ta faɗa ba, a raina kuwa juya maganar na ringayi. Hajja tace na nuna mata kayan da Hafiz ya kawo, to ya akayi ta sani? Sai dai idan Bilal ne ya gaya mata shine zata turo ta tunda shi bai gani ba su suzo su gani ko?
Wane ɓangare na zuciya ta ya shiga ƙoƙarin kare Bilal ta hanyar gwada mun ba shi ya turo su ba amma kuma tunani mafi rinjaye shi ɗin ne tunda ina da tabbacin Hafiz dai ba zai je ko ya kira su ya faɗa musu ba.
"Zan je na faɗa mata kin ce na ƙarfi ne idan muna da gado a ciki mu taru mu ƙwata" ta sake faɗa kamar wata yarinya ƙarama.

Sai lokacin na kalle ta, murmushin takaici ya ƙwace mun na girgiza kai na ce
"Ai ba yau zan fara sanin ke ɗin maƙaryaciya bace kuma masharranciya, kije ki faɗi hakan ni yanzu bani da lokacin ki" na kwanta haɗi da juya mata baya. Ina ji ta ja ƙwafa kafin ta fita ta bugo mun ƙofa, da Zainab ta sake zuwa akan nazo muyi sallama zasu tafi ce mata nayi ta ce ina banɗaki kawai. Sai da na tabbatar sun bar gidan kafin na fito falo Mama ta bani dubu goma da turmin Atamfa Holland sai riguna masu kyau guda uku in ji Hajiya Sa'adatu.
Chapter 68 · 0% Book details