Sashe 101
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai kuwa ko dubu zaka shiga yau sai dai ka shiga dan wlh ba zan kwana a hotel ba a gida na yi niyyar kwana tunda kuma ka kyautar mun da kayan gida ba tareda izini na ba sai ka kaini naka gidan ba wai matarka bata nan ba ko tana nan wlh ba abinda ya mun zafi a nan zan kwana dan dama da baka zo ba sai dai ka ganni a ƙofar gida kuma ko yanzu ka direni a nan ƙila sai na rigaka zuwa so baki alaikum ka wuce mu tafi dan ni a gajiye nake wanka nake so nayi na kwanta nayi bacci" ta bashi amsa itama.
Duk yanda ya so ya fahimtar da ita ta masa banza ƙarshe mayafinta taja ta rufe fuskarta kamar me bacci, ganin har ɗaya ta kusa suna gararanba akan titi bai kuma ga alamar zata canza ra'ayi ba ya saka kawai ya kama hanyar gida a ransa yana addu'ar Allah ya sa kowa yayi bacci har masu gadin layin. Ya da sauri ya kalli mirror jin ta ce
"Ga wata mota nan ma tun ɗazu take binka ƙila ma matar taka ce ko wani daya sanka" ta ƙarasa tana dariya. Kallon motar yayi dakyau, sai tayi masa kama da motar Suhaila matar Hafiz amma kuma number ta banbanta tata kamar ABJ wannan kuma ABC dukda dai bai tabbatar ba amma ya ƙarfafawa kansa hakan ne dan ba zai iya hasaso cewa Matar Hafiz ɗin ce ko kuma ma shine da kansa ba iya tashin hankalin da yake ciki yanzu ya ishe shi. Kamar me motar ya san me suke cewa kuwa yazo ya wuce su dama a junction suke ya ɗauki wata hanyar daban Bilal ya sauke ajiyar zuciya kafin ya balla mata harara ya cigaba da tuƙi.
Roƙonta ya ringayi akan ta rufe fuskarta sanda suka isa unguwar, duk wanda ya kalle shi dakyau sai ya fahimci bashi da gaskiya haka ya lallaɓa ya shige Allah ya taimake shi mutum ɗaya ne zaune sauran masu gadin duk sunyi bacci get ɗin kuma a buɗe yake dan haka bai ma taso ba tunda ya gane motar daga zaune ya masa sannu da zuwa ya wuce dama kuma windows ɗin motar tint ne ta gaba ne za'a iya ganin wanda yake ciki. Sai da ya shige da motar ya dawo ya kulle get kafin ya tsaya ya riƙe ƙugu yana sauke numfashi. Ta fashe da dariya bayan da ta fito daga motar tana cewa
"Wai yanzu duk tsoron kar yan unguwa su ganka ne yasa ka birkice haka amma baka tsoron Allah kake bajekolinka a hotel ko?"
"Dan Allah ki wuce ciki kum wlh tun kafin gari yayi haske zamu fita ba zaki zubar mun da mutunchi a unguwa ba dama duk sun tsaneni tunda Halima ta bar gidan nan" ya faɗa yana wucewa gaba bayan daya shiga ɗakin tsakar gida ya kunno Solar dan babu wuta tunda sha biyu ta wuce kuma ya san ba dawo da ita zasuyi ba. Bayan tafiyar Halima da aka fara rashin wuta ya haɗa ta babba har Ac take ɗauka. Kan kujera ta faɗa tana cewa
"Wash Allah, daɗi na da matar nan taka akwai tsafta ba wanda zaice falon me yara ne kamar na sabuwar amarya komai na nan da sabuntarsa"
"Basu daɗe ba ai bayan haihuwar Sharifa ta canza su" ya bata amsa yana ɗaukar remote ɗin Ac ya kunna. Ta miƙe tana ƙoƙarin cire doguwar rigar jikinta tace
"Dukda haka dai tana da tsafta gaskiya" sai ya wuce ɗaki yana cewa
"Ba laifi amma dai ni nake shara da mopping har wankin toilet duka" ta kuwa fashe da dariya tace
"Ashe boyi boyi ta mayar da kai sannu mijin tace".
Indomie ya dafa mata bayan tayi wanka ya ɗumama Shawarmar daya siyo ɗazu a microwave dama guda biyu ce ya dafa tea suka ci kafin ta kwanta a Asalin ɗakin Halima da tace gadon irin nata ne na gida dan haka nan zata kwanta kafin ma ya gama wanke kwanukan da suka ɓata ya tattare falon har tayi bacci. A falo ya kwanta bayan daya leƙa ta ya tarar tana bacci dan dama cike yake da taraddadin karta nemi suyi wani abu dan gaskiya ba zai iya ba gaba ɗaya yanzu haka ma a mugun tsorace yake ji yakeyi kamar wani zai iya shigowa ya tarar dasu yayi mamakin yanda yake ji ɗin dan ko kaɗan bayajin komai idan suka je can gidan ta ko da yake yan unguwar kallon ma'aurata suke musu irin kamar a wani garin suke zama sai hutu suke zuwa nan ɗin. Daƙyar bacci ya ɗauke shi yana yi yana farkawa gudun karsu makara gari yayi haske bai fita da ita daga unguwar ba.
HALIMA
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 43*
HALIMA
Yanda naga rana haka naga dare, sai naji ashe ma jiya baccin daɗi nayi yaune nake ganin asalin baƙin dare. Sai da aka idar da sallar asuba kafin na samu bacci ya fizgeni, sai dai ban wani yi nisa ba na farka sakamakon kiran suna na da nake ta ji anayi.
Na tashi zaune daƙyar ina matse ido haɗi da dafe gefen kaina da nake ji kamar zai faɗo saboda ciwo. Mama na tsaye ta ce
"Hala kin manta abinda Abbanku ya faɗa miki shiyasa kika shantake kina bacci har ƙarfe tara".
Gabana ya yanke ya faɗi, mai take nufi? Takardar ya turo ta karɓa ko me?
Muryata bata ko fita sosai saboda uban kukan da nasha jiya ga bacci da ciwon kan da suka mun rubdugu na ce
"Dan girman Allah Mama ki bashi haƙuri"
"Kin yafe ba zakiyi bautar ƙasar ba kenan in je na gaya masa?" Ta katse ni. Na tabbatar har kunnuwanta ƙarar ajiyar zuciyar da nayi ya isa jin ba abinda nake tunani bane, ta ja tsaki ta fice daga ɗakin tana cewa
"Ki tashi ki shirya tun ranki bai sakw ɓaci ba dan wlh a cike yake dake kin kuma san dai bai iya fushi ba".
Ina wanka ina hasaso ta inda zan samu mafita cikin wannan tsaka mai wuya da Abba yake ƙoƙarin jefa ni. Yanzu shi ba bu ruwansa a ringa cewa aure na ya mutu kenan? Na tafi tunani dangi na uwa da uba babu wata bazawara kamata, yawanci ma har manyan mutuwa ce ta rabasu da mazajensu ba sakin aure na shikenan ni zan zama abar buga misali a dangi da unguwa, fatan da aka ringa mun zai tabbata na san ƙila labari na babu inda ba zai kai ba har Facebook da Whatsapp groups.
Kan toilet na zauna na sha kuka na godewa Allah kafin na fito na sake zama kan gado na rafka tagumi. Allah ya sani ina son Bilal, rabuwa dashi abu ne da ban taɓa hasasowa a nan kusa ba duk da abinda ya faru yayi silar zabtarewar sama da kaso hamsin na yanda nake jin sa a zuciyata amma in ce na dena son sa wannan ƙarya kawai nakeyi.
Hannu biyu na saka ina goge sababbin hawayen da suka ɓalle mun, da kaina kuma na shiga tugumar kaina anya kuwa nayiwa kaina adalci idan na cigaba da son Bilal?
Babu wani abu da zan ɗorar a zamana dashi wanda zan dogara akansa har ya bani ƙwarin guiwar sake bashi dama a karo na biyu bayan abinda ya faru. Ya gwada mun halayen ni da kaina na yarda zuciyar dake cike da so ba zata aikata irin su ba abu mafi muni ya ci amanata a bayan ido na yana mu'amala da macen banza sannan ya tozartani akan hakan har mahaifiyata yayiwa zagi mafi muni kuma dukda haka nake jin zan iya yafe masa na cigaba da rayuwa dashi.
Ƙasa na durƙushe na sake fashewa da kuka ina nanata "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Tabbas ina cikin masifa ni kaina na sani ta yaya wanda ya aikata mun irin waɗannan zunuban zan cigaba da dakon soyayyar sa a raina?
Muryar Mama naji a kaina tana cewa
"Halima wai ba zaki ko duba ƙananun yayanki kiyi tunanin halin da zasu shiga idan babu ke ba kin dage lallai sai kin ja wa kanki ciwon da zai kashe ki ko?" Ta faɗa tana kallo na, ban ɗago ba sai kukan da na cigaba da yi, tayi ƙaramin tsaki ta ce
"Mu'azzam yana da uzuri kin zaka ya tsayar dashi ya ce ya kaiki idan ba zakije ba ki fita ki gayawa Abba ya sallame shi ya tafi sabgar sa dan Allah"
"Mama kin dena so na, kwata kwata yanzu kin dena damuwa da abinda ya shafe ni kenan idan ma na mutu yarana ne kaɗai suka rasa banda ke" na faɗa cikin kuka. Tayi ƙaramar dariya tana nufar ƙofa tace
"Mutum kuwa ya taɓa haifar ɗa a cikin sa yace ya dena sonsa Halima? Ke ɗin ce ai kin zama gomnati ba'a miki kutse yanda aka dama da nace yaranki kuma kinga ai su ke kaɗai gare su ni kuwa Alhamdulillahi ku huɗu Allah ya bani dama kuma daɗin haihuwar da yawa kenan idan wani bai faranta maka ba wani zai saka ka farinciki. Ni dai idan ba zakije ba kije ki faɗa masa dan Allah ya sallamar mun yaro ya tafi dan shi yana da abubuwan yi da zasu taimaki rayuwar sa".
Wato ni ce wadda bata da abinyi da zai taimaki rayuwata? Haka nan na haƙurtar da kaina na saka kaya ban ko nemi mai ba balle aje ga batun turare ko in yi kwalliya, sai sa na gama shiryawa kuma sannan na tuna ai Khaki ya kamata na saka kuma ban taho dasu ba suna can gidan Bilal.
Duk yanda ya so ya fahimtar da ita ta masa banza ƙarshe mayafinta taja ta rufe fuskarta kamar me bacci, ganin har ɗaya ta kusa suna gararanba akan titi bai kuma ga alamar zata canza ra'ayi ba ya saka kawai ya kama hanyar gida a ransa yana addu'ar Allah ya sa kowa yayi bacci har masu gadin layin. Ya da sauri ya kalli mirror jin ta ce
"Ga wata mota nan ma tun ɗazu take binka ƙila ma matar taka ce ko wani daya sanka" ta ƙarasa tana dariya. Kallon motar yayi dakyau, sai tayi masa kama da motar Suhaila matar Hafiz amma kuma number ta banbanta tata kamar ABJ wannan kuma ABC dukda dai bai tabbatar ba amma ya ƙarfafawa kansa hakan ne dan ba zai iya hasaso cewa Matar Hafiz ɗin ce ko kuma ma shine da kansa ba iya tashin hankalin da yake ciki yanzu ya ishe shi. Kamar me motar ya san me suke cewa kuwa yazo ya wuce su dama a junction suke ya ɗauki wata hanyar daban Bilal ya sauke ajiyar zuciya kafin ya balla mata harara ya cigaba da tuƙi.
Roƙonta ya ringayi akan ta rufe fuskarta sanda suka isa unguwar, duk wanda ya kalle shi dakyau sai ya fahimci bashi da gaskiya haka ya lallaɓa ya shige Allah ya taimake shi mutum ɗaya ne zaune sauran masu gadin duk sunyi bacci get ɗin kuma a buɗe yake dan haka bai ma taso ba tunda ya gane motar daga zaune ya masa sannu da zuwa ya wuce dama kuma windows ɗin motar tint ne ta gaba ne za'a iya ganin wanda yake ciki. Sai da ya shige da motar ya dawo ya kulle get kafin ya tsaya ya riƙe ƙugu yana sauke numfashi. Ta fashe da dariya bayan da ta fito daga motar tana cewa
"Wai yanzu duk tsoron kar yan unguwa su ganka ne yasa ka birkice haka amma baka tsoron Allah kake bajekolinka a hotel ko?"
"Dan Allah ki wuce ciki kum wlh tun kafin gari yayi haske zamu fita ba zaki zubar mun da mutunchi a unguwa ba dama duk sun tsaneni tunda Halima ta bar gidan nan" ya faɗa yana wucewa gaba bayan daya shiga ɗakin tsakar gida ya kunno Solar dan babu wuta tunda sha biyu ta wuce kuma ya san ba dawo da ita zasuyi ba. Bayan tafiyar Halima da aka fara rashin wuta ya haɗa ta babba har Ac take ɗauka. Kan kujera ta faɗa tana cewa
"Wash Allah, daɗi na da matar nan taka akwai tsafta ba wanda zaice falon me yara ne kamar na sabuwar amarya komai na nan da sabuntarsa"
"Basu daɗe ba ai bayan haihuwar Sharifa ta canza su" ya bata amsa yana ɗaukar remote ɗin Ac ya kunna. Ta miƙe tana ƙoƙarin cire doguwar rigar jikinta tace
"Dukda haka dai tana da tsafta gaskiya" sai ya wuce ɗaki yana cewa
"Ba laifi amma dai ni nake shara da mopping har wankin toilet duka" ta kuwa fashe da dariya tace
"Ashe boyi boyi ta mayar da kai sannu mijin tace".
Indomie ya dafa mata bayan tayi wanka ya ɗumama Shawarmar daya siyo ɗazu a microwave dama guda biyu ce ya dafa tea suka ci kafin ta kwanta a Asalin ɗakin Halima da tace gadon irin nata ne na gida dan haka nan zata kwanta kafin ma ya gama wanke kwanukan da suka ɓata ya tattare falon har tayi bacci. A falo ya kwanta bayan daya leƙa ta ya tarar tana bacci dan dama cike yake da taraddadin karta nemi suyi wani abu dan gaskiya ba zai iya ba gaba ɗaya yanzu haka ma a mugun tsorace yake ji yakeyi kamar wani zai iya shigowa ya tarar dasu yayi mamakin yanda yake ji ɗin dan ko kaɗan bayajin komai idan suka je can gidan ta ko da yake yan unguwar kallon ma'aurata suke musu irin kamar a wani garin suke zama sai hutu suke zuwa nan ɗin. Daƙyar bacci ya ɗauke shi yana yi yana farkawa gudun karsu makara gari yayi haske bai fita da ita daga unguwar ba.
HALIMA
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 43*
HALIMA
Yanda naga rana haka naga dare, sai naji ashe ma jiya baccin daɗi nayi yaune nake ganin asalin baƙin dare. Sai da aka idar da sallar asuba kafin na samu bacci ya fizgeni, sai dai ban wani yi nisa ba na farka sakamakon kiran suna na da nake ta ji anayi.
Na tashi zaune daƙyar ina matse ido haɗi da dafe gefen kaina da nake ji kamar zai faɗo saboda ciwo. Mama na tsaye ta ce
"Hala kin manta abinda Abbanku ya faɗa miki shiyasa kika shantake kina bacci har ƙarfe tara".
Gabana ya yanke ya faɗi, mai take nufi? Takardar ya turo ta karɓa ko me?
Muryata bata ko fita sosai saboda uban kukan da nasha jiya ga bacci da ciwon kan da suka mun rubdugu na ce
"Dan girman Allah Mama ki bashi haƙuri"
"Kin yafe ba zakiyi bautar ƙasar ba kenan in je na gaya masa?" Ta katse ni. Na tabbatar har kunnuwanta ƙarar ajiyar zuciyar da nayi ya isa jin ba abinda nake tunani bane, ta ja tsaki ta fice daga ɗakin tana cewa
"Ki tashi ki shirya tun ranki bai sakw ɓaci ba dan wlh a cike yake dake kin kuma san dai bai iya fushi ba".
Ina wanka ina hasaso ta inda zan samu mafita cikin wannan tsaka mai wuya da Abba yake ƙoƙarin jefa ni. Yanzu shi ba bu ruwansa a ringa cewa aure na ya mutu kenan? Na tafi tunani dangi na uwa da uba babu wata bazawara kamata, yawanci ma har manyan mutuwa ce ta rabasu da mazajensu ba sakin aure na shikenan ni zan zama abar buga misali a dangi da unguwa, fatan da aka ringa mun zai tabbata na san ƙila labari na babu inda ba zai kai ba har Facebook da Whatsapp groups.
Kan toilet na zauna na sha kuka na godewa Allah kafin na fito na sake zama kan gado na rafka tagumi. Allah ya sani ina son Bilal, rabuwa dashi abu ne da ban taɓa hasasowa a nan kusa ba duk da abinda ya faru yayi silar zabtarewar sama da kaso hamsin na yanda nake jin sa a zuciyata amma in ce na dena son sa wannan ƙarya kawai nakeyi.
Hannu biyu na saka ina goge sababbin hawayen da suka ɓalle mun, da kaina kuma na shiga tugumar kaina anya kuwa nayiwa kaina adalci idan na cigaba da son Bilal?
Babu wani abu da zan ɗorar a zamana dashi wanda zan dogara akansa har ya bani ƙwarin guiwar sake bashi dama a karo na biyu bayan abinda ya faru. Ya gwada mun halayen ni da kaina na yarda zuciyar dake cike da so ba zata aikata irin su ba abu mafi muni ya ci amanata a bayan ido na yana mu'amala da macen banza sannan ya tozartani akan hakan har mahaifiyata yayiwa zagi mafi muni kuma dukda haka nake jin zan iya yafe masa na cigaba da rayuwa dashi.
Ƙasa na durƙushe na sake fashewa da kuka ina nanata "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Tabbas ina cikin masifa ni kaina na sani ta yaya wanda ya aikata mun irin waɗannan zunuban zan cigaba da dakon soyayyar sa a raina?
Muryar Mama naji a kaina tana cewa
"Halima wai ba zaki ko duba ƙananun yayanki kiyi tunanin halin da zasu shiga idan babu ke ba kin dage lallai sai kin ja wa kanki ciwon da zai kashe ki ko?" Ta faɗa tana kallo na, ban ɗago ba sai kukan da na cigaba da yi, tayi ƙaramin tsaki ta ce
"Mu'azzam yana da uzuri kin zaka ya tsayar dashi ya ce ya kaiki idan ba zakije ba ki fita ki gayawa Abba ya sallame shi ya tafi sabgar sa dan Allah"
"Mama kin dena so na, kwata kwata yanzu kin dena damuwa da abinda ya shafe ni kenan idan ma na mutu yarana ne kaɗai suka rasa banda ke" na faɗa cikin kuka. Tayi ƙaramar dariya tana nufar ƙofa tace
"Mutum kuwa ya taɓa haifar ɗa a cikin sa yace ya dena sonsa Halima? Ke ɗin ce ai kin zama gomnati ba'a miki kutse yanda aka dama da nace yaranki kuma kinga ai su ke kaɗai gare su ni kuwa Alhamdulillahi ku huɗu Allah ya bani dama kuma daɗin haihuwar da yawa kenan idan wani bai faranta maka ba wani zai saka ka farinciki. Ni dai idan ba zakije ba kije ki faɗa masa dan Allah ya sallamar mun yaro ya tafi dan shi yana da abubuwan yi da zasu taimaki rayuwar sa".
Wato ni ce wadda bata da abinyi da zai taimaki rayuwata? Haka nan na haƙurtar da kaina na saka kaya ban ko nemi mai ba balle aje ga batun turare ko in yi kwalliya, sai sa na gama shiryawa kuma sannan na tuna ai Khaki ya kamata na saka kuma ban taho dasu ba suna can gidan Bilal.