Sashe 155
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ɗakin na nan yanda yake Katifa ce Gado huta a ciki sai ƙaramin carpet a tsakiyar ɗakin daga gefe kuma ga alwatuna da yake zaton kayansa ne dana Zulaihan a ciki. Towel ɗin data fitar ta bashi ya cire kaya ya ɗaura ya yafa wani ƙarami kafin ya fita yana sunkuyar da kai ya shiga wankan. Bokiti uku ta ajiye masa sai da ya gamsu dan kansa da wankan da yayi kafin ya fito yana jinsa kamar wanda aka sake haihuwa. Bai san inda zai tsoma ransa ba da ta tabbata zai yi zaman kurkuku na shekarun da yaji ana ambatowa. Ko a ina aka samu kuɗaɗen da aka ce an biya masa bashin ma sai Allah domin dai bashi da su bai kuma bawa wani ajiya ba.
Kaɗan ya ci abincin da Zulaiha ta shirya masa bayan yayi sallar magriba da aka kira yana wanka. Yana jingine da bango yayi shiru Abubakar ya ƙwanƙwasa ƙofa ya bashi izinin shiga dan Zulaiha bata ɗakin. Ledar Rufaida yoghurt ya ajiye masa da magunguna yana masa sannu.
"Na san dai da takura amma ba yanda za'ayi da nayi tunanin ko nemi haya toh ga wani sabon lissafin kuma ya sake tasowa. A haka ma Allah ya rufa asiri kaga gidajen da aka siyar duka sunyi daraja sosai shiyasa har aka samu aka rage kuɗaɗen" Abubakar ya faɗa. Bilal dake kallonsa ya ce
"Wai a ina aka samu kuɗaɗen da aka biyasu kuwa?"
"Shine maganar da nake yi maka, an siyar da gidanka na Goran dutse da kuma wancan na Rijiyar Zaki sai filaye guda biyu, takardun uku na gani amma biyu ne suka siyu ɗayan dillalan sunce hanya ce kaima kayi ganganci daka siya".
Shiru yayi kafin a hankali abin tausayi yace
"Toh yanzu saura nawa a gama biyanta ita?"
"Miliyan goma aka bata" ya bashi amsa, ya ɗago kamar a firgice ya zaro ido ya ce
"Goma? Saura Ashirin fa kenan, a ina zan nemo miliyan ashirin banda yanzu waccen tarar? Na shiga uku da wahala dai idan ban yi zaman kurkuku ba dan ban san in da zan samo kuɗin nan ba" ya faɗa gwanin tausayi kamar zai fashe da kuka.
Abubakar ya kalle shi cike da tausayawa ya ce
"Alhaji Hafiz ya biya duka tarar, yanzu ina hanya Barr Sajid ya kirani yake cewa ya kirashi yace ya tura da account number da za'a saka kuɗin, ya tura masa na san kuma ya saka dukda bai sake kirana ba".
Cike da rashin yarda Bilal ya ce
"Hafiz? Hafiz dai dana sani ko wani daban?"
"Shi dai Hafiz abokinka. Badan shi ba ai da wahala wannan yarinyar ta haƙura. Na fahimci ba wai kuɗin ne a gabanta ba burinta ta wulaƙanta ka dan shi kansa Alhaji Lawan ɗin ita ta ringa zugashi sai da Hafiz ɗin ya shiga maganar kafin suka haƙura."
Shiru sukayi na kusan minti biyar kafin a hankali Bilal ya ce
" Ɗazu naga Halima amma kafin mu fito ta tafi ita da wani Namiji"
"Eh taje nima bamuyi sallama ba gaskiya ta wuce" Abubakar daya miƙe ya bashi amsa. Sai ya sake karyar da murya ya ce
"Shi wanene wanda na gansu tare toh?"
"Wanda zata aura ne" ya bashi amsa cikin halin ko in kula. Yanda ka san dirar mashi haka yaji maganar, ya gwale ido yana kallon Abubakar ya ce
"Wanda zata aura?"
"Haka tace mun" Abubakar ya sake bashi amsa. Sai ya koma laƙwas ba tareda ya sake cewa komai ba Abubakar kuma ya fice daga ɗakin.
Kwana yayi a zaune, dukda ya tsammaci rasa sauran abubuwan daya mallaka domin dai babu mai biya masa bashin daya ci wa kansa amma kuma bai zaci abin zai dame shi haka ba. Shikenan yanzu ko gidan da zai zauna bashi da shi ya dawo ɗakin ƙaninsa da zama dan asalin nasa ɗakin samartaka a soro yake shi aka shigowa Hajja dashi aka ƙara mata a falo bayan da aka raba asalin ɗakin ya koma ciki da rumfa sannan aka mata banɗaki da sauran a cikin ɗaki. Shi gashi yanzu ɗakin ma falle ɗaya suka samu banɗaki sai sun fita tsakar gida, hatta da kayan gadon sa da na Zulaihan duka dasu akayi gwanjon gidan kayan kitchen ɗinta da sauran abubuwanta kawai ta fita dasu.
Abu ɗaya da ya saka ya ɗan ji dama-dama yanda bai ga damuwa sosai akan canjin muhallin a tattare da Zulaiha ba. Ba yabo ba fallasa take sabgoginta, daya gama cin abinci ta tattare kwanuka ta fita dasu ta dawo ta tambaye shi ko akwai abinda yake buƙata yace babu shikenan tayi kwanciyarta.
A haka ya kwashe kwana uku yana jinyar malaria daya kwaso a prison, ba inda yake fita yana ɗaki ko falon Hajja sai ta fito tana ta ƙwala masa kira musamman idan yan jaje da yace munafunci suke zuwa suka zo kafin zai shiga yafi ganewa ya zauna a ɗaki kawai yayi shiru yana Istigfari da tunanin duniya.
Ranar daya kwana huɗu da yamma yana kwance a ɗaki ranar an samu sauƙin yan jaje dan tun safe babu wanda yayi sallama, yana kwancen yana jiyo Hajja nata sababi wanda kuma ya san ba zai wuce da Zulaiha take ba. Tun washe garin daya dawo ya fahimci za'a samu gagarunar matsala tsakanin Hajja da Zulaihan a zamansu.
Hajja tamkar shi take, gurinta ya gado shegiyar tsafta da rashin son ganin shirgi a guri. Idan ka shiga gidanta kamar ba na tsohuwa ba shiyasa sanda Fadila take zawarci Hajjan take gwammace ta tafi gidan Anty Habiba saboda tace ɓata mata gida takeyi, da ciwon ƙafar da komai haka zatayi shara ta wuni tana kaye-kaye ko leda iska ta kwaso mata idan bata ɗauke ba bata jin daɗi toh yanzu ga Zulaiha kuma da shegiyar ƙazanta.
Bata mata aikin komai, dai-dai da kwanukan abinci idan aka kai masa dan ita bata wani ci sai kayan kwaɗayi yanayinta ma sai yake ganin kamar tana da shigar ciki dukda bai tabbatar ba amma haka zata haɗo na rana da dare ta fito dasu ƙofar ɗaki da safe sai dai Safiyya yar Anty Ladidi ta ɗauke ta wanke. Tun bayan da aka sallamo Hajjan daga Asibiti ta dawo gidan da zama saboda yanzu ko tafiya sai da sanduna biyu take yinta Safiyyan ce take mata komai haka su ma hatta sharar cikin ɗakin ita take shiga ta musu.
Yau ɗin Safiyyar ta tafi rubuya Jamb tun safe kafin ta fita kuma sai da ta yiwa Hajjan komai har abin karyawa, tun sha ɗaya yana ji tana kiran Zulaiha ta fito ta ɗora abincin rana tunda Safiyya bata dawo ba amma tayi kunnen uwar shegu tana danna waya shima ya maimaita mata amma bata ko kalle shi ba yayi shiru ya zura mata ido ana kiran Azahar ta ɗaura zani ta fita ta juye ruwan zafin da Hajjan ta ɗora a kurfoti ta shige wanka shine yanzu ta fito ta gani take sababi.
Tashi yayi ya saka riga saboda jiyo tashin muryar Zulaihan da yayi kamar tana amsawa Hajja maganar da takeyi, yana fita kuwa ya jita tana cewa
"Ai na faɗa miki ni ba yar aiki bace zaman aure nakeyi idan ma zan girkawa wani abinci toh mijina ne tunda kuma kince ke zaki ringa bashi abinci sai kiyi tayi ku dafa ko karku dafa matsalarku ce ko kinga ina cin abincinku ne?"
"Ni kike faɗawa haka" Hajja ta faɗa tana kallonta, Zulaiha ta ɗauke kai gefe ganin Bilal ɗin ya fito ba tareda tace komai ba shirun da sukayi kuma ya saka suka ji sallamar da ake ta dokawa tun farkon fara muhawarar tasu. Duka su ukun suka kalli ƙofa, Halima dake tsaye riƙe da hannun Sharifa Al'amin da Inaayah na tsaye kusa da ita hannayensu riƙe da ledoji ta sake maimaita sallama.
Ba Bilal da Hajja ba hatta Zulaiha sai da taji wani iri da zuwan Haliman da sauri ta shige ɗaki ta bar Bilal da Hajja da suka ƙame a tsaye aka rasa wanda zai amsa musu.
HALIMA
Ganin duk suna kallonmu sun kasa magana ya saka na shiga ina faɗaɗa fuskata, tabarmar da na gani shimfiɗe kan barandar ɗakin Hajja muka zauna tareda yaran sai lokacin sukayi firgigit kamar waɗanda aka watsawa ruwan sanyi Hajja cikin murmushin da kana gani kasan na yaƙe ne haɗi da kunya mai tsanani ta shiga yi mana sannu da zuwa tana cewa mu tashi mu shiga ciki.
"Nan ma yayi Hajja" na faɗa ta ce
"Aa ku tashi dan Allah" ta kamo Al'amin tana cewa
"Ku tashi ku shiga ciki kunji kai da ɗakin matarka ace ku zauna a tabarma".
A raina nace "ikon Allah" kafin na miƙe nabi bayanta. Kallon falon na ringayi, tunda naje gidan Bilal nake masa nacin ya kamata ya gyarawa Hajja ɗakinta ƙarshe cewa yayi nima idan nayi mata ai ba laifi bane shi in rabu dashi a lokacin har na niyyata zanyi ɗin da surutu na faɗawa Mama tace kar taji karta gani na fishi sanin ya kamata ne ko kuwa da zance zan gyarawa Babarsa ɗaki gashi yanzu Allah ya nufa an mata shi ɗin ne ko Abubakar ne sai Allah.
Al'amin ta cewa ya buɗe fridge ya ɗebo mana ruwa da lemo nace mata a barshi daga gida muke ma mungode"
"Kai tashi ka ɗebo, rashin ƙafa ya saka har aka fara ganin damata ana maida mun magana" Hajjan ta faɗa sai na kama bakina nayi shiru kawai ina duba wayata da tayi ƙara dai-dai nan Bilal ya shigo falon da ƙaramar sallama kamar Almajirin dake jin yunwa.
A kujerar dake bakin ƙofa ya zauna, sai da na kalli Inaayah da Al'amin da suke kallonsa kamar sunga wani baƙo kafin suka gaishe shi, ya miƙawa Sharifa hannu ta sake lafewa a jikina dan tunda Hajja tace taje da a zaune take a kujerar ta tashi ta haye jikina.
"Au kaima ubanta kenan, toh bari na shafawa kaina lafiya" Hajja ta faɗa, na kalleshi kafin na gaishe shi haɗi dayi masa jaje ya amsa yana mun kallon ƙurilla kamar wanda ke neman wani abu a jikina. Falon yayi shiru, ƙarar da wayata tayi ya saka na miƙe ina cewa
"Dama kawo su nayi su dubaku bari muje ana jiranmu a waje"
Kaɗan ya ci abincin da Zulaiha ta shirya masa bayan yayi sallar magriba da aka kira yana wanka. Yana jingine da bango yayi shiru Abubakar ya ƙwanƙwasa ƙofa ya bashi izinin shiga dan Zulaiha bata ɗakin. Ledar Rufaida yoghurt ya ajiye masa da magunguna yana masa sannu.
"Na san dai da takura amma ba yanda za'ayi da nayi tunanin ko nemi haya toh ga wani sabon lissafin kuma ya sake tasowa. A haka ma Allah ya rufa asiri kaga gidajen da aka siyar duka sunyi daraja sosai shiyasa har aka samu aka rage kuɗaɗen" Abubakar ya faɗa. Bilal dake kallonsa ya ce
"Wai a ina aka samu kuɗaɗen da aka biyasu kuwa?"
"Shine maganar da nake yi maka, an siyar da gidanka na Goran dutse da kuma wancan na Rijiyar Zaki sai filaye guda biyu, takardun uku na gani amma biyu ne suka siyu ɗayan dillalan sunce hanya ce kaima kayi ganganci daka siya".
Shiru yayi kafin a hankali abin tausayi yace
"Toh yanzu saura nawa a gama biyanta ita?"
"Miliyan goma aka bata" ya bashi amsa, ya ɗago kamar a firgice ya zaro ido ya ce
"Goma? Saura Ashirin fa kenan, a ina zan nemo miliyan ashirin banda yanzu waccen tarar? Na shiga uku da wahala dai idan ban yi zaman kurkuku ba dan ban san in da zan samo kuɗin nan ba" ya faɗa gwanin tausayi kamar zai fashe da kuka.
Abubakar ya kalle shi cike da tausayawa ya ce
"Alhaji Hafiz ya biya duka tarar, yanzu ina hanya Barr Sajid ya kirani yake cewa ya kirashi yace ya tura da account number da za'a saka kuɗin, ya tura masa na san kuma ya saka dukda bai sake kirana ba".
Cike da rashin yarda Bilal ya ce
"Hafiz? Hafiz dai dana sani ko wani daban?"
"Shi dai Hafiz abokinka. Badan shi ba ai da wahala wannan yarinyar ta haƙura. Na fahimci ba wai kuɗin ne a gabanta ba burinta ta wulaƙanta ka dan shi kansa Alhaji Lawan ɗin ita ta ringa zugashi sai da Hafiz ɗin ya shiga maganar kafin suka haƙura."
Shiru sukayi na kusan minti biyar kafin a hankali Bilal ya ce
" Ɗazu naga Halima amma kafin mu fito ta tafi ita da wani Namiji"
"Eh taje nima bamuyi sallama ba gaskiya ta wuce" Abubakar daya miƙe ya bashi amsa. Sai ya sake karyar da murya ya ce
"Shi wanene wanda na gansu tare toh?"
"Wanda zata aura ne" ya bashi amsa cikin halin ko in kula. Yanda ka san dirar mashi haka yaji maganar, ya gwale ido yana kallon Abubakar ya ce
"Wanda zata aura?"
"Haka tace mun" Abubakar ya sake bashi amsa. Sai ya koma laƙwas ba tareda ya sake cewa komai ba Abubakar kuma ya fice daga ɗakin.
Kwana yayi a zaune, dukda ya tsammaci rasa sauran abubuwan daya mallaka domin dai babu mai biya masa bashin daya ci wa kansa amma kuma bai zaci abin zai dame shi haka ba. Shikenan yanzu ko gidan da zai zauna bashi da shi ya dawo ɗakin ƙaninsa da zama dan asalin nasa ɗakin samartaka a soro yake shi aka shigowa Hajja dashi aka ƙara mata a falo bayan da aka raba asalin ɗakin ya koma ciki da rumfa sannan aka mata banɗaki da sauran a cikin ɗaki. Shi gashi yanzu ɗakin ma falle ɗaya suka samu banɗaki sai sun fita tsakar gida, hatta da kayan gadon sa da na Zulaihan duka dasu akayi gwanjon gidan kayan kitchen ɗinta da sauran abubuwanta kawai ta fita dasu.
Abu ɗaya da ya saka ya ɗan ji dama-dama yanda bai ga damuwa sosai akan canjin muhallin a tattare da Zulaiha ba. Ba yabo ba fallasa take sabgoginta, daya gama cin abinci ta tattare kwanuka ta fita dasu ta dawo ta tambaye shi ko akwai abinda yake buƙata yace babu shikenan tayi kwanciyarta.
A haka ya kwashe kwana uku yana jinyar malaria daya kwaso a prison, ba inda yake fita yana ɗaki ko falon Hajja sai ta fito tana ta ƙwala masa kira musamman idan yan jaje da yace munafunci suke zuwa suka zo kafin zai shiga yafi ganewa ya zauna a ɗaki kawai yayi shiru yana Istigfari da tunanin duniya.
Ranar daya kwana huɗu da yamma yana kwance a ɗaki ranar an samu sauƙin yan jaje dan tun safe babu wanda yayi sallama, yana kwancen yana jiyo Hajja nata sababi wanda kuma ya san ba zai wuce da Zulaiha take ba. Tun washe garin daya dawo ya fahimci za'a samu gagarunar matsala tsakanin Hajja da Zulaihan a zamansu.
Hajja tamkar shi take, gurinta ya gado shegiyar tsafta da rashin son ganin shirgi a guri. Idan ka shiga gidanta kamar ba na tsohuwa ba shiyasa sanda Fadila take zawarci Hajjan take gwammace ta tafi gidan Anty Habiba saboda tace ɓata mata gida takeyi, da ciwon ƙafar da komai haka zatayi shara ta wuni tana kaye-kaye ko leda iska ta kwaso mata idan bata ɗauke ba bata jin daɗi toh yanzu ga Zulaiha kuma da shegiyar ƙazanta.
Bata mata aikin komai, dai-dai da kwanukan abinci idan aka kai masa dan ita bata wani ci sai kayan kwaɗayi yanayinta ma sai yake ganin kamar tana da shigar ciki dukda bai tabbatar ba amma haka zata haɗo na rana da dare ta fito dasu ƙofar ɗaki da safe sai dai Safiyya yar Anty Ladidi ta ɗauke ta wanke. Tun bayan da aka sallamo Hajjan daga Asibiti ta dawo gidan da zama saboda yanzu ko tafiya sai da sanduna biyu take yinta Safiyyan ce take mata komai haka su ma hatta sharar cikin ɗakin ita take shiga ta musu.
Yau ɗin Safiyyar ta tafi rubuya Jamb tun safe kafin ta fita kuma sai da ta yiwa Hajjan komai har abin karyawa, tun sha ɗaya yana ji tana kiran Zulaiha ta fito ta ɗora abincin rana tunda Safiyya bata dawo ba amma tayi kunnen uwar shegu tana danna waya shima ya maimaita mata amma bata ko kalle shi ba yayi shiru ya zura mata ido ana kiran Azahar ta ɗaura zani ta fita ta juye ruwan zafin da Hajjan ta ɗora a kurfoti ta shige wanka shine yanzu ta fito ta gani take sababi.
Tashi yayi ya saka riga saboda jiyo tashin muryar Zulaihan da yayi kamar tana amsawa Hajja maganar da takeyi, yana fita kuwa ya jita tana cewa
"Ai na faɗa miki ni ba yar aiki bace zaman aure nakeyi idan ma zan girkawa wani abinci toh mijina ne tunda kuma kince ke zaki ringa bashi abinci sai kiyi tayi ku dafa ko karku dafa matsalarku ce ko kinga ina cin abincinku ne?"
"Ni kike faɗawa haka" Hajja ta faɗa tana kallonta, Zulaiha ta ɗauke kai gefe ganin Bilal ɗin ya fito ba tareda tace komai ba shirun da sukayi kuma ya saka suka ji sallamar da ake ta dokawa tun farkon fara muhawarar tasu. Duka su ukun suka kalli ƙofa, Halima dake tsaye riƙe da hannun Sharifa Al'amin da Inaayah na tsaye kusa da ita hannayensu riƙe da ledoji ta sake maimaita sallama.
Ba Bilal da Hajja ba hatta Zulaiha sai da taji wani iri da zuwan Haliman da sauri ta shige ɗaki ta bar Bilal da Hajja da suka ƙame a tsaye aka rasa wanda zai amsa musu.
HALIMA
Ganin duk suna kallonmu sun kasa magana ya saka na shiga ina faɗaɗa fuskata, tabarmar da na gani shimfiɗe kan barandar ɗakin Hajja muka zauna tareda yaran sai lokacin sukayi firgigit kamar waɗanda aka watsawa ruwan sanyi Hajja cikin murmushin da kana gani kasan na yaƙe ne haɗi da kunya mai tsanani ta shiga yi mana sannu da zuwa tana cewa mu tashi mu shiga ciki.
"Nan ma yayi Hajja" na faɗa ta ce
"Aa ku tashi dan Allah" ta kamo Al'amin tana cewa
"Ku tashi ku shiga ciki kunji kai da ɗakin matarka ace ku zauna a tabarma".
A raina nace "ikon Allah" kafin na miƙe nabi bayanta. Kallon falon na ringayi, tunda naje gidan Bilal nake masa nacin ya kamata ya gyarawa Hajja ɗakinta ƙarshe cewa yayi nima idan nayi mata ai ba laifi bane shi in rabu dashi a lokacin har na niyyata zanyi ɗin da surutu na faɗawa Mama tace kar taji karta gani na fishi sanin ya kamata ne ko kuwa da zance zan gyarawa Babarsa ɗaki gashi yanzu Allah ya nufa an mata shi ɗin ne ko Abubakar ne sai Allah.
Al'amin ta cewa ya buɗe fridge ya ɗebo mana ruwa da lemo nace mata a barshi daga gida muke ma mungode"
"Kai tashi ka ɗebo, rashin ƙafa ya saka har aka fara ganin damata ana maida mun magana" Hajjan ta faɗa sai na kama bakina nayi shiru kawai ina duba wayata da tayi ƙara dai-dai nan Bilal ya shigo falon da ƙaramar sallama kamar Almajirin dake jin yunwa.
A kujerar dake bakin ƙofa ya zauna, sai da na kalli Inaayah da Al'amin da suke kallonsa kamar sunga wani baƙo kafin suka gaishe shi, ya miƙawa Sharifa hannu ta sake lafewa a jikina dan tunda Hajja tace taje da a zaune take a kujerar ta tashi ta haye jikina.
"Au kaima ubanta kenan, toh bari na shafawa kaina lafiya" Hajja ta faɗa, na kalleshi kafin na gaishe shi haɗi dayi masa jaje ya amsa yana mun kallon ƙurilla kamar wanda ke neman wani abu a jikina. Falon yayi shiru, ƙarar da wayata tayi ya saka na miƙe ina cewa
"Dama kawo su nayi su dubaku bari muje ana jiranmu a waje"