Sashe 74
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dama akan saka shi a makaranta ma sai da raina ya ɓaci cewa ya yi bashi da kuɗi yanzu sai dai a jira zuwa second term.
"Kawai tsurfa ce irin taki, shekara uku ne zaki wani damu a saka shi a makaranta ni banyi lissafi da kuɗin makaranta ba gaskiya a watannan watan da na gaba, sai dai ki jira second term se a kaishi idan kuma na zaki iya jira ba ki saka shi tunda ke kike so" amsar da ya bani a lokacin har kuma aka cinye first term aka shiga hutu bai tayar da maganar ba ƙarshe ni ɗin da na damu ni na nemi kuɗi na kaishi makaranta kuma ya dawo zai yi mun haukan ƙarya akan me zan kaishi ko ce mun ya yi ba zai saka shi? Kuma shi ba wacce na kai shi ya yi niyya ba sai a cire shi a mayar da shi wacce yake so.
Peak ya siyo leda biyu, na haɗa kunun na bata tana gama sha kuma ta koma bacci bayan na bata magungunan ta na zuƙe mata majinar da hanata sukuni lokacin Al'amin ya tashi na masa wanka sannan na zuba masa abinci. Ina zaune ina kallon sa yana cin abincin, a zahiri kallon sa nake yi amma a baɗini nayi nisa cikin tunanin neman hanyar da zan ringa samun kuɗi tunda sune tikitin farin ciki na a cikin gidan. Na sauke ajiyar zuciya jin Al'amin yana girgiza ni, ya gama cin abincin muka tafi kitchen na wanke masa hannu sannan na bashi ruwa ya sha muna fitowa Ummi yarinyar Maman Yusuf da suke tafiya Islamiyya tare ta shigo da suka fita.
Sai lokacin nima na ɗebi abinci kaɗan na ci. A mudubin banɗaki da na shiga alwala na tsaya na ƙarewa kaina kallo, ni dama jiki ba auki ba damuwa duk ta sake tsotseni nayi baƙi kamar mara lafiya. Na ɗauro alwala ina fitowa na ji Bilal yana kirana. Hijab na saka na fita ina ɓata rai ganin Abubakar da wani da ban sani ba ya saka na ɗan saki fuska na zauna kan hannun kujera muka gaisa a gurguje suka tafi.
Ledar dake kan center table ya nuna mun ya ce
"Ga magungunan nan".
"Kai da ka ce baka da kuɗi?" Na faɗa ina tsareshi da ido.
Tsareni yayi da ido shima yana wani murmushi dana tabbatar akwai wata manufa a ƙasan zuciyar sa, na ɗauke kaina gefe saboda bana fatan nan kusa ya ci galaba akaina na sakko, ina fatan ya fahimci fushi na kuma canza zuwa yanda nake fatan ya kasance.
"Na samu na siyo toh. Kina ta fushi wai kina zaton da gangan zan ƙi siya mata magani ne ahalin ina da kuɗin siyan?" Ya faɗa yana wani karya harshe. Tsakin da ban zata ba ya ƙwace mun na miƙe tsaye ina cewa
"Na tabbata ko maganin dubu ɗari ne Nasir ba zai ƙi yi maka lamuni ba, amma saboda baka damu da ta rayu ko ta mutu ba faɗa kayi akan me zan kaita asibitin kuɗi a rubuta mata magani mai tsada. Ni da na haifeta ina son abata kuma na nemi kuɗi tuntuni na siya mata magani dan haka ka mayar ka karɓo kuɗin ka mungode" na wuce ɗaki saboda kukan da ya taho mun. Ina shiga na mayar da ƙofa na rufe na jingina a jiki na fashe da kuka.
Bayan na idar da sallar la'asar ina lazumi na tuna da Oil ɗin da nake mata sirace da shi ya ƙare, goyata na yi na ɗakko jakar da na zuba sauran kuɗin suka ce na ɗauke su in da na ajiye. Sai da na duba duk jakunkunana da inda nake ajiyar kuɗi amma ban gansu ba, na koma na zauna gefen gado na zabga tagumi hawaye suka fara tarar mun a kwarmin ido na. Waye ze ɗauka kuɗin gida daga ni sai yara.
Zuciya ta ta ringa raya mun Bilal ne kawai zai ɗauki kuɗin amma da wacce shaida zan kama shi? Tunda muke bai taɓa ɗaukar mun kuɗi ba ba tare da sanina ba sai dai na ɗauka da hannu na na bashi amma kuma idan ba shi ba waye ya ɗauki kuɗin??
Kuka na zauna na sha na godewa Allah. Yanzu idan na masa magana ko da ace shi ya ɗauka na san tashin hankali zan janyowa kaina da sai na gwammace ban yi maganar ba idan kuma nayi shiru zan cutu dan su kaɗai ne kuɗin da suka rage mun su nake so na lallaɓa a hannu na zuwa wani lokacin.
Kwanciya nayi na cigaba da saƙa da warwarar yanda zan ɓullowa al'amari na, Abban dai bani da kamar sa shi kaɗai ya fahimce ni shi ne kuma ba zai gajiya da ni ba. Tashi nayi na ciro wayata daga caji, sau uku ina danna layin Abba sai na katse dan ban san me zance masa ba.
A tsakanin shekara ɗaya sau biyu ya bani jari wanda da ace da gaske kasuwancin na yi da yanzu sun haɓaka amma muka taru da ni da Bilal muka cinye su. Miliyan ɗaya ya bani da farko akan na je na kama wani abun idan ya ga kamun ludayin sana'ar sai ya ƙara mun wani abu. A raina a lokacin Anty Labiba nayi niyyar bawa kuɗin, tana siyar da kayan kitchen da kayan irin PAT PAT ɗin nan, na san ko a cikin unguwar da nake zanyi cinikin su tunda kusan kowanne gida akwai yara ƙanana tsautsayi farin ciki ya saka na bawa Bilal labari shi kuma ya kawo mun shawarar gwada Exportation.
Kamar yanda ya ce shima yanzu abinda yake so yayi kenan wani abokin sa yana harkar fitar da riɗi da citta. Lissafin da ya mun dukda kuɗin basu da yawa acewar sa a zuwa ɗaya za'a iya samun ribar dubu ɗari biyu zuwa sama kuma a ƙalla duk wata suna tura kaya sau biyu dan haka na bayar da kuɗin ya haɗa da nasa sai mu ringa raba ribar haka na bashi ba tareda nayi shawara da kowa ba har yau kuma babu kuɗin babu riba, da na masa magana bayan an shafe wata biyu bai ce mun komai ba sai cewa yayi wai motar da ta ɗakko kayan daga ƙauyen da aka siyo su yan kidnapping sun ƙwace ta shikenan maganar ta wuce.
Haka na sake komawa a karo na biyu akan a ƙara mun jarin sai Abba ya bani zaɓi saboda ya ce kuɗin da ya ware a lokacin wanda zai biya mun aikin Hajji ne. Idan na yarda ya bani rance a ciki tunda akwai sauran lokaci da Sharaɗin zan maido da su kuma na karɓa tunda na san zance ne kawai yake yi in dai Allah ya nufa tunda yayi niyya zai biya mun na je na san kuma ko da na mayar da kuɗin ba zai karɓa ba. Wannan karon Anty Labiban na bawa aka kawo mun kayan yaran kuma Allah ya buɗa mun kasuwar kafin kace me suka ƙare sai dai kafin na haɗa kuɗin na sake bata a kawo wasu na cinye rabi, da aka sake kawowa dab da sallah ƙarshe ya saka na bawa yaran yayyen sa akan zai siya har yau kuma bai bani kuɗin ba shikenan jarin ya karye ido da kunya kuma na sake komawa.
Sai da Abba ya kira sau biyu kafin nayi ƙarfin halin ɗagawa. Muak gaisa kafin ya ce
"Ina kan hanya ne sai da ma sauka yanzu naga kiran ki, kuma ɗazu na shigo unguwar taku wata gaisuwa kamar na leƙo naga wannan maƙuyaciyar matar tawa da ake mun rowar ta sai kuma na wuce"
"Lah Abba da ka zo ai bata da lafiya ma shiyasa kwana biyu kuka ji mu shiru" na faɗa. Ya tambaye ni mai ya sameta na gaya masa harda sunan magungunan da aka rubuta mata kafin ya mata addu'ar samun sauƙi. Jin yana ƙoƙarin kashe wayar ya saka na ce
"Dama Abba likitan ya rubuta mana wani test ne yace idan ta sha maganin na kwana uku bata samu sauƙi ba muyi kuma yau kwana ukun da sauƙi jikin amma ba yanda na zata ba shine nake tunanin ko zan mayar da ita ayi"
"Ya kamata dai ayi test ɗin na ɗauka ma ai sai da sukayi kafin aka bata maganin, amma dai ba Dr Bashir kuka gani ba dan na san shi baya rubuta magani kai tsaye in dai symptoms yana buƙatar ayi test sai ya tabbatar da abunda yake damun mutum kafin nan" cewar Abba. Shiru nayi ya sake cewa
"Ki tabbata gobe kun koma anyi test ɗin Allah ya sa ba Pneumonia ba ce ba"
"Ai kuɗi ne bani da shi ma shiyasa da yau ɗin zan mayar da ita" nayi ƙarfin halin faɗa. Ya ɗan yi shiru kafin ya ce
"Babanta baya nan ne?"
"Aa yana nan Abba, cewa yayi na bari cikin wanin satin ayi salary tukunna"
"Wace irin magana ce ita rashin lafiyar yarinyar za'a ce a jira har wani lokaci? Zan tura miki kuɗi yanzu ki kama hanya ki mayar da ita Asibiti duk kuma yanda akayi ki sanar da ni" Abban ya faɗa kamar cikin fushi dai dai lokacin Bilal ya shigo ɗakin nayi masa kallo ɗaya na cigaba da yiwa Abba godiya.
"Halimatu" Abba ya sake kira sunana, kafin na amsa ya cigaba da cewa
"Ya kamata kiyi ƙoƙari ki samu certificate ɗin NYSC a nema miki aiki idan ya so ki haɗa da business ɗin gaba daya zai fi, duk da dai na ce ba zan sake magana akan hakan ba amma hakan ya kamata ayi".
"Shikenan Abba zan masa magana duk shawarar da ya yanke sai na faɗa maka" na faɗa murya ta na karyewa, ya ce
"Ba zancen shawara bane Halima umarni nake baki, ya isa haka ya kamata ki san in da kika dosa a rayuwa zuwa yanzu". Haka nan naji zuciya ta ta karye kuka ya taho mun amma na daure na ce
"In sha Allah Abba".
"Kawai tsurfa ce irin taki, shekara uku ne zaki wani damu a saka shi a makaranta ni banyi lissafi da kuɗin makaranta ba gaskiya a watannan watan da na gaba, sai dai ki jira second term se a kaishi idan kuma na zaki iya jira ba ki saka shi tunda ke kike so" amsar da ya bani a lokacin har kuma aka cinye first term aka shiga hutu bai tayar da maganar ba ƙarshe ni ɗin da na damu ni na nemi kuɗi na kaishi makaranta kuma ya dawo zai yi mun haukan ƙarya akan me zan kaishi ko ce mun ya yi ba zai saka shi? Kuma shi ba wacce na kai shi ya yi niyya ba sai a cire shi a mayar da shi wacce yake so.
Peak ya siyo leda biyu, na haɗa kunun na bata tana gama sha kuma ta koma bacci bayan na bata magungunan ta na zuƙe mata majinar da hanata sukuni lokacin Al'amin ya tashi na masa wanka sannan na zuba masa abinci. Ina zaune ina kallon sa yana cin abincin, a zahiri kallon sa nake yi amma a baɗini nayi nisa cikin tunanin neman hanyar da zan ringa samun kuɗi tunda sune tikitin farin ciki na a cikin gidan. Na sauke ajiyar zuciya jin Al'amin yana girgiza ni, ya gama cin abincin muka tafi kitchen na wanke masa hannu sannan na bashi ruwa ya sha muna fitowa Ummi yarinyar Maman Yusuf da suke tafiya Islamiyya tare ta shigo da suka fita.
Sai lokacin nima na ɗebi abinci kaɗan na ci. A mudubin banɗaki da na shiga alwala na tsaya na ƙarewa kaina kallo, ni dama jiki ba auki ba damuwa duk ta sake tsotseni nayi baƙi kamar mara lafiya. Na ɗauro alwala ina fitowa na ji Bilal yana kirana. Hijab na saka na fita ina ɓata rai ganin Abubakar da wani da ban sani ba ya saka na ɗan saki fuska na zauna kan hannun kujera muka gaisa a gurguje suka tafi.
Ledar dake kan center table ya nuna mun ya ce
"Ga magungunan nan".
"Kai da ka ce baka da kuɗi?" Na faɗa ina tsareshi da ido.
Tsareni yayi da ido shima yana wani murmushi dana tabbatar akwai wata manufa a ƙasan zuciyar sa, na ɗauke kaina gefe saboda bana fatan nan kusa ya ci galaba akaina na sakko, ina fatan ya fahimci fushi na kuma canza zuwa yanda nake fatan ya kasance.
"Na samu na siyo toh. Kina ta fushi wai kina zaton da gangan zan ƙi siya mata magani ne ahalin ina da kuɗin siyan?" Ya faɗa yana wani karya harshe. Tsakin da ban zata ba ya ƙwace mun na miƙe tsaye ina cewa
"Na tabbata ko maganin dubu ɗari ne Nasir ba zai ƙi yi maka lamuni ba, amma saboda baka damu da ta rayu ko ta mutu ba faɗa kayi akan me zan kaita asibitin kuɗi a rubuta mata magani mai tsada. Ni da na haifeta ina son abata kuma na nemi kuɗi tuntuni na siya mata magani dan haka ka mayar ka karɓo kuɗin ka mungode" na wuce ɗaki saboda kukan da ya taho mun. Ina shiga na mayar da ƙofa na rufe na jingina a jiki na fashe da kuka.
Bayan na idar da sallar la'asar ina lazumi na tuna da Oil ɗin da nake mata sirace da shi ya ƙare, goyata na yi na ɗakko jakar da na zuba sauran kuɗin suka ce na ɗauke su in da na ajiye. Sai da na duba duk jakunkunana da inda nake ajiyar kuɗi amma ban gansu ba, na koma na zauna gefen gado na zabga tagumi hawaye suka fara tarar mun a kwarmin ido na. Waye ze ɗauka kuɗin gida daga ni sai yara.
Zuciya ta ta ringa raya mun Bilal ne kawai zai ɗauki kuɗin amma da wacce shaida zan kama shi? Tunda muke bai taɓa ɗaukar mun kuɗi ba ba tare da sanina ba sai dai na ɗauka da hannu na na bashi amma kuma idan ba shi ba waye ya ɗauki kuɗin??
Kuka na zauna na sha na godewa Allah. Yanzu idan na masa magana ko da ace shi ya ɗauka na san tashin hankali zan janyowa kaina da sai na gwammace ban yi maganar ba idan kuma nayi shiru zan cutu dan su kaɗai ne kuɗin da suka rage mun su nake so na lallaɓa a hannu na zuwa wani lokacin.
Kwanciya nayi na cigaba da saƙa da warwarar yanda zan ɓullowa al'amari na, Abban dai bani da kamar sa shi kaɗai ya fahimce ni shi ne kuma ba zai gajiya da ni ba. Tashi nayi na ciro wayata daga caji, sau uku ina danna layin Abba sai na katse dan ban san me zance masa ba.
A tsakanin shekara ɗaya sau biyu ya bani jari wanda da ace da gaske kasuwancin na yi da yanzu sun haɓaka amma muka taru da ni da Bilal muka cinye su. Miliyan ɗaya ya bani da farko akan na je na kama wani abun idan ya ga kamun ludayin sana'ar sai ya ƙara mun wani abu. A raina a lokacin Anty Labiba nayi niyyar bawa kuɗin, tana siyar da kayan kitchen da kayan irin PAT PAT ɗin nan, na san ko a cikin unguwar da nake zanyi cinikin su tunda kusan kowanne gida akwai yara ƙanana tsautsayi farin ciki ya saka na bawa Bilal labari shi kuma ya kawo mun shawarar gwada Exportation.
Kamar yanda ya ce shima yanzu abinda yake so yayi kenan wani abokin sa yana harkar fitar da riɗi da citta. Lissafin da ya mun dukda kuɗin basu da yawa acewar sa a zuwa ɗaya za'a iya samun ribar dubu ɗari biyu zuwa sama kuma a ƙalla duk wata suna tura kaya sau biyu dan haka na bayar da kuɗin ya haɗa da nasa sai mu ringa raba ribar haka na bashi ba tareda nayi shawara da kowa ba har yau kuma babu kuɗin babu riba, da na masa magana bayan an shafe wata biyu bai ce mun komai ba sai cewa yayi wai motar da ta ɗakko kayan daga ƙauyen da aka siyo su yan kidnapping sun ƙwace ta shikenan maganar ta wuce.
Haka na sake komawa a karo na biyu akan a ƙara mun jarin sai Abba ya bani zaɓi saboda ya ce kuɗin da ya ware a lokacin wanda zai biya mun aikin Hajji ne. Idan na yarda ya bani rance a ciki tunda akwai sauran lokaci da Sharaɗin zan maido da su kuma na karɓa tunda na san zance ne kawai yake yi in dai Allah ya nufa tunda yayi niyya zai biya mun na je na san kuma ko da na mayar da kuɗin ba zai karɓa ba. Wannan karon Anty Labiban na bawa aka kawo mun kayan yaran kuma Allah ya buɗa mun kasuwar kafin kace me suka ƙare sai dai kafin na haɗa kuɗin na sake bata a kawo wasu na cinye rabi, da aka sake kawowa dab da sallah ƙarshe ya saka na bawa yaran yayyen sa akan zai siya har yau kuma bai bani kuɗin ba shikenan jarin ya karye ido da kunya kuma na sake komawa.
Sai da Abba ya kira sau biyu kafin nayi ƙarfin halin ɗagawa. Muak gaisa kafin ya ce
"Ina kan hanya ne sai da ma sauka yanzu naga kiran ki, kuma ɗazu na shigo unguwar taku wata gaisuwa kamar na leƙo naga wannan maƙuyaciyar matar tawa da ake mun rowar ta sai kuma na wuce"
"Lah Abba da ka zo ai bata da lafiya ma shiyasa kwana biyu kuka ji mu shiru" na faɗa. Ya tambaye ni mai ya sameta na gaya masa harda sunan magungunan da aka rubuta mata kafin ya mata addu'ar samun sauƙi. Jin yana ƙoƙarin kashe wayar ya saka na ce
"Dama Abba likitan ya rubuta mana wani test ne yace idan ta sha maganin na kwana uku bata samu sauƙi ba muyi kuma yau kwana ukun da sauƙi jikin amma ba yanda na zata ba shine nake tunanin ko zan mayar da ita ayi"
"Ya kamata dai ayi test ɗin na ɗauka ma ai sai da sukayi kafin aka bata maganin, amma dai ba Dr Bashir kuka gani ba dan na san shi baya rubuta magani kai tsaye in dai symptoms yana buƙatar ayi test sai ya tabbatar da abunda yake damun mutum kafin nan" cewar Abba. Shiru nayi ya sake cewa
"Ki tabbata gobe kun koma anyi test ɗin Allah ya sa ba Pneumonia ba ce ba"
"Ai kuɗi ne bani da shi ma shiyasa da yau ɗin zan mayar da ita" nayi ƙarfin halin faɗa. Ya ɗan yi shiru kafin ya ce
"Babanta baya nan ne?"
"Aa yana nan Abba, cewa yayi na bari cikin wanin satin ayi salary tukunna"
"Wace irin magana ce ita rashin lafiyar yarinyar za'a ce a jira har wani lokaci? Zan tura miki kuɗi yanzu ki kama hanya ki mayar da ita Asibiti duk kuma yanda akayi ki sanar da ni" Abban ya faɗa kamar cikin fushi dai dai lokacin Bilal ya shigo ɗakin nayi masa kallo ɗaya na cigaba da yiwa Abba godiya.
"Halimatu" Abba ya sake kira sunana, kafin na amsa ya cigaba da cewa
"Ya kamata kiyi ƙoƙari ki samu certificate ɗin NYSC a nema miki aiki idan ya so ki haɗa da business ɗin gaba daya zai fi, duk da dai na ce ba zan sake magana akan hakan ba amma hakan ya kamata ayi".
"Shikenan Abba zan masa magana duk shawarar da ya yanke sai na faɗa maka" na faɗa murya ta na karyewa, ya ce
"Ba zancen shawara bane Halima umarni nake baki, ya isa haka ya kamata ki san in da kika dosa a rayuwa zuwa yanzu". Haka nan naji zuciya ta ta karye kuka ya taho mun amma na daure na ce
"In sha Allah Abba".