Sashe 34
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ke bafa zama zanyi ba. Nan bayan ku zamu je gaisuwa gidan wani abokin sa maman sa ta rasu a UK suke to sunyi waya yace yazo Kano amma gobe ze wuce Abuja shine muka taho yanzu fa se da muka kuje kuma ashe shi kaɗai ne yazo banda matar sa, naga zasu ɓata lokaci da hira shine fa nace ya kawo ni nan na dubaki kafin su gama mu wuce, su Halima matar Bilal, irin wannan mulmul da kika yi lallai Bilal ya iya kiwo" ta ƙarasa tana kallo na. Na rufe fuska cikin jin kunya ina cewa
"Kai Anty, kamar kin shekara baki ganni ba"
"A shekarar kaɗan ne babu ai, haɗuwa tayi wuya se dai mu gamu a hanya nan kuma ai ba wani ganin ki nakeyi sosai ba kamar yanzu ko?" Ta faɗa, nasan magana ta gaya mun dan haka nayi murmushi kawai na shiga tambayar ta su Inayah.
"Dama suna gidan Mama ɗazu shine su Amirah basu taho da su ba?" Na faɗa, se tace
"Aa, se gobe zamu je. Amir ne kawai yaje su je kallon hawa tare da su Mu'azzam". Hira muka shiga yi gwanin daɗi, har tara da rabi sannan Uncle Saleh ya kirata yace gashi nan ya taho. Se sannan ta tambaye ni Bilal, tambayar da nake ta addu'ar kar Allah ya buɗi bakinta ta mun dan ban san me zan ce mata ba sanin tun kafin muyi aure da Bilal duk wanda ya sanshi ze bada shaidar baya yawon dare. Duk in da akayi sallar isha'i ya shiga gida in dai ba guri na ze je ba.
Ce mata nayi yana can gidan su ai be jima da fita ba suka zo, kallon da ta mun yasa na fahimci bata kama zancen ba. Ta ƙare mun kallo tace
"Wannan kayan ma tun na kwalliyar safe ne da kikayi baki sake wasu ba". Zan kwaso rantsuwa ta dakatar dani tace
"Idan kika zauna shashanci kanki zakiwa sagegeduwa. Ba yanzu zaki takaicin barin sa ya koyi yawon dare ba se nan gaba dan haka tun lokaci be ƙure miki ba ki gyara. Duk irin hirar da zeje yayi a wajen ki tanade ta ki ringa yi masa a gida ya fiye miki alkhairi idan ba haka ba ke kika sani kina zaune can wasu zasu ringa cusa masa wasu ra'ayoyi na banza a lalata miki miji".
Tunani maganar ta ta jefa ni, anya babu saka hannun abokai cikin baƙin halayen Bilal da nake cin karo dasu? Waya sani kam ko a yawon da yake tafiya ake yo masa wasu karatu na banza suna gurbata masa tunani dan dai ni shaida ce ba haka Bilal ɗin dana sani yake ba tabbas. Buɗe ƙofar da akayi ya dawo dani daga tunanin da na tafi. Muka haɗa ido da Bilal ya galla mun harara ba tare da yayi ko da sallama ba ya wuce kitchen yana sakin ƙaramin tsaki. Se da naji ina ma da damar da ƙasa zata tsage na shige ciki na ɓuya ko kuma ace abin da ya farun yanzu mafarki ne zan tashi naga zuwan Anty Labiba be faru ba. Kamar me ciwon wuya daƙyar na waiga na kalli Anty Labiba dake danna wayarta se ka rantse bata ji shigowar Bilal ɗin ba. Nayi ƙasa da kai kamar munafuka ina jan yatsun hannu na, daga kitchen ɗin ya ƙwalo mun kira. Ƙafafu na sun yi sanyin da bazan iya miƙewa ba, sake kiran yayi se lokacin Anty Labiba ta ɗaga kai ta kalle ni tace
"Ba kiran ki yake yi ba?"
Ina zaton baƙuwar muryar da yaji se gashi ya fito kamar an jefo shi, yayi turus a bakin ƙofa yana raba ido kafin yayi ƙasa da kai yana shafa ƙeya kamar mara gaskiya lokaci ɗaya ya lalubo murmushi ya ɗora a fuskar sa ya nufo in da muke yana cewa
"Kune a gidan namu yau Anty"
"Mun same mu lafiya? Ya sallah?" Ta faɗa tana miƙewa saboda wayar ta data ɗauki ƙarar shigowar kira. Bata amsa gaisuwar da ya shiga yi mata ba ta nufi ƙofa tana ce mun
"Allah ya ƙara sauƙi Halima na wuce se da safe" ta fice daga falon. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka na bi bayan ta. Yanzu Allah kaɗai yasan tunanin da zata yi kuma. Dubu goma Uncle Saleh ya bani barka da sallah, Anty Labiba dai tunda ta zauna a motar ko kallo na bata sake yi ba yaja suka tafi.
A kan kujera na tarar da Bilal ya dafe kai da hannu biyu yana jin motsi na ya miƙe fuska ba yabo ba fallasa yana kallo na yace
"Me yasa baki kira ni kin ce mun ta zo ba?"
[1/15, 11:17 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 15*
Ban tanka masa ba na shiga tattare kayan dake ajiye dana gama kuma na wuce ɗakina na kwanta, nayi mamakin ganin ya biyo ni, nayi lamo a kan gado ina sauraren sa har ya gama uzure uzurensa na bacci kafin ya kwanta a baya na tare da jana jikin sa yana cewa
"Nasan ba bacci kike yi ba juyo na baki barka da sallah" nayi masa banza duk yanda yake ya mutsani da son se na biye masa na dake daya gaji ya sake ni ina jin sa yana tsaki har baccin gaske ya ɗauke ni. Washe gari nayi zaton ze cigaba da fushin amma naga akasin haka dan tun asuba daya tashi be zauna ba seda ya share gidan tas yayi mopping ya wanke banɗakuna harda na tsakar gida.
Ina kwance a falo kan carpet in da nayi sallah ya shigo bayan ya gama gyara tsakar gidan, zazzaɓi ne a jiki na sosai, na lulluɓe har kaina ga iskar hadari dake kaɗawa tasa har karkarwar sanyi nake yi. Sama sama nake jin sa yana kiran suna na, jin ban amsa ba yasa ya ƙaraso in da nake ya duƙa yana kirana tare da ɗan bubbuga gefen pillow da nake kwance.
"Dame zaki karya?" Ya tambaye ni, nayi shiru dan baki na yayi mun nauyi kuma kusancin da mukayi ƙamshin turaren sa dake bugun hanci na duk se ya sake hautsinamun kai baki na har ya fara tara yawu alamar amai na son taso mun. Miƙewa yayi yana cewa
"Shikenan ai, tun jiya nake binki kina mun wulaƙanci. Fitina kike nema ni kuma ba zakiyi da ni ba" ya shige kitchen. Se maganar sa ta ma bani dariya, wai yana bina ina masa wulaƙanci Bilal kenan me abin mamaki. Ƙarfe tara na farka daga baccin da ban san sanda ya ɗauke ni ba, zazzaɓin ya saukar mun dan haka na miƙe ina kallon falon dake ta tashin ƙamshin turaren wuta da roomfreshener. Zancen gaskiya iya gyaran gidan Bilal ba duk mace ba. Haka nan idan ya bushi iska har canza jeren kujeru ya keyi. Se da nayi wanka nayi kwalliya cikin sababbin ɗinkin sallar da nayi kafin na shiga kitchen neman abinci. Doya ya dafa da sauce ɗin ƙwai. Dake akwai wuta se nayi microwaving na haɗa baƙin shayi na dawo falo na zauna kan carpet na shiga karyawa. Bilal ya shigo falon da sallama, kan kujerar dake kallo na ya zauna yana murmushi yace
"Ranki ya daɗe an tashi kenan". Kallon sa nayi ba yabo ba fallasa na gaishe shi. Surutu ya fara mun ina bin sa da eh da aa har na ƙare cin abincin na yunƙura zan maida kwanon kitchen ya karɓa se gashi ya dawo harda ruwa me sanyi ya ajiye mun.
"Yanzu Hajja ta kira ni kin ji kuma wai taron suna suke so suyi, na zata tun da aka wuce satin ga kuma daga ita har yaron ba wata lafiya ta ishe su ba ai se su haƙura ko?" Ya faɗa yana kallo na. Na gyara kwanciya ta nace
"Eh, dama Fadilan tace mun zatayi taron suna ai, kuma haihuwar fari ai ya kamata tayi dama kuma yawanci in dai C's ne se sati biyu akeyin taro ba ranar kwana bakwai ba"
"Amma dai ƙarawa mutane ɗawainiya ne, baki ga jiya nayi dare ba? Wai fa ɗan iskan mijin nan nata se jiya sannan suka zo da yayyen sa biyu wai bada haƙuri suka kawo wasu shegun kayan su a leda wai na barka. Wlh badan Hajja tace nayi shiru ba niyya nayi nace su tafi da tsiyar su tunda da basu kawo ba ɗin ma babu abin da aka fasa yi mata da ɗan nasu har suna cewa a musu lissafin abin da aka kashe na asibiti zasu biya kamar gaske" ya sake faɗa. Tun da ya fara maganar na zuba masa ido ina kallon sa, so nake nace masa kawo kaya a leda ai ba kansu aka fara ba ƙarewar kayan barka naga har lefe sun kai a leda me yasa dan an musu yanzu abin ze yi musu zafi amma na kasa faɗa saboda nasan ƙarshe ze iya juyawa maganar manufa yace na masa gori ko wani abu se kawai na datse zancen da cewa
"Allah ya rufa asiri kawai".
"Kai Anty, kamar kin shekara baki ganni ba"
"A shekarar kaɗan ne babu ai, haɗuwa tayi wuya se dai mu gamu a hanya nan kuma ai ba wani ganin ki nakeyi sosai ba kamar yanzu ko?" Ta faɗa, nasan magana ta gaya mun dan haka nayi murmushi kawai na shiga tambayar ta su Inayah.
"Dama suna gidan Mama ɗazu shine su Amirah basu taho da su ba?" Na faɗa, se tace
"Aa, se gobe zamu je. Amir ne kawai yaje su je kallon hawa tare da su Mu'azzam". Hira muka shiga yi gwanin daɗi, har tara da rabi sannan Uncle Saleh ya kirata yace gashi nan ya taho. Se sannan ta tambaye ni Bilal, tambayar da nake ta addu'ar kar Allah ya buɗi bakinta ta mun dan ban san me zan ce mata ba sanin tun kafin muyi aure da Bilal duk wanda ya sanshi ze bada shaidar baya yawon dare. Duk in da akayi sallar isha'i ya shiga gida in dai ba guri na ze je ba.
Ce mata nayi yana can gidan su ai be jima da fita ba suka zo, kallon da ta mun yasa na fahimci bata kama zancen ba. Ta ƙare mun kallo tace
"Wannan kayan ma tun na kwalliyar safe ne da kikayi baki sake wasu ba". Zan kwaso rantsuwa ta dakatar dani tace
"Idan kika zauna shashanci kanki zakiwa sagegeduwa. Ba yanzu zaki takaicin barin sa ya koyi yawon dare ba se nan gaba dan haka tun lokaci be ƙure miki ba ki gyara. Duk irin hirar da zeje yayi a wajen ki tanade ta ki ringa yi masa a gida ya fiye miki alkhairi idan ba haka ba ke kika sani kina zaune can wasu zasu ringa cusa masa wasu ra'ayoyi na banza a lalata miki miji".
Tunani maganar ta ta jefa ni, anya babu saka hannun abokai cikin baƙin halayen Bilal da nake cin karo dasu? Waya sani kam ko a yawon da yake tafiya ake yo masa wasu karatu na banza suna gurbata masa tunani dan dai ni shaida ce ba haka Bilal ɗin dana sani yake ba tabbas. Buɗe ƙofar da akayi ya dawo dani daga tunanin da na tafi. Muka haɗa ido da Bilal ya galla mun harara ba tare da yayi ko da sallama ba ya wuce kitchen yana sakin ƙaramin tsaki. Se da naji ina ma da damar da ƙasa zata tsage na shige ciki na ɓuya ko kuma ace abin da ya farun yanzu mafarki ne zan tashi naga zuwan Anty Labiba be faru ba. Kamar me ciwon wuya daƙyar na waiga na kalli Anty Labiba dake danna wayarta se ka rantse bata ji shigowar Bilal ɗin ba. Nayi ƙasa da kai kamar munafuka ina jan yatsun hannu na, daga kitchen ɗin ya ƙwalo mun kira. Ƙafafu na sun yi sanyin da bazan iya miƙewa ba, sake kiran yayi se lokacin Anty Labiba ta ɗaga kai ta kalle ni tace
"Ba kiran ki yake yi ba?"
Ina zaton baƙuwar muryar da yaji se gashi ya fito kamar an jefo shi, yayi turus a bakin ƙofa yana raba ido kafin yayi ƙasa da kai yana shafa ƙeya kamar mara gaskiya lokaci ɗaya ya lalubo murmushi ya ɗora a fuskar sa ya nufo in da muke yana cewa
"Kune a gidan namu yau Anty"
"Mun same mu lafiya? Ya sallah?" Ta faɗa tana miƙewa saboda wayar ta data ɗauki ƙarar shigowar kira. Bata amsa gaisuwar da ya shiga yi mata ba ta nufi ƙofa tana ce mun
"Allah ya ƙara sauƙi Halima na wuce se da safe" ta fice daga falon. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka na bi bayan ta. Yanzu Allah kaɗai yasan tunanin da zata yi kuma. Dubu goma Uncle Saleh ya bani barka da sallah, Anty Labiba dai tunda ta zauna a motar ko kallo na bata sake yi ba yaja suka tafi.
A kan kujera na tarar da Bilal ya dafe kai da hannu biyu yana jin motsi na ya miƙe fuska ba yabo ba fallasa yana kallo na yace
"Me yasa baki kira ni kin ce mun ta zo ba?"
[1/15, 11:17 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 15*
Ban tanka masa ba na shiga tattare kayan dake ajiye dana gama kuma na wuce ɗakina na kwanta, nayi mamakin ganin ya biyo ni, nayi lamo a kan gado ina sauraren sa har ya gama uzure uzurensa na bacci kafin ya kwanta a baya na tare da jana jikin sa yana cewa
"Nasan ba bacci kike yi ba juyo na baki barka da sallah" nayi masa banza duk yanda yake ya mutsani da son se na biye masa na dake daya gaji ya sake ni ina jin sa yana tsaki har baccin gaske ya ɗauke ni. Washe gari nayi zaton ze cigaba da fushin amma naga akasin haka dan tun asuba daya tashi be zauna ba seda ya share gidan tas yayi mopping ya wanke banɗakuna harda na tsakar gida.
Ina kwance a falo kan carpet in da nayi sallah ya shigo bayan ya gama gyara tsakar gidan, zazzaɓi ne a jiki na sosai, na lulluɓe har kaina ga iskar hadari dake kaɗawa tasa har karkarwar sanyi nake yi. Sama sama nake jin sa yana kiran suna na, jin ban amsa ba yasa ya ƙaraso in da nake ya duƙa yana kirana tare da ɗan bubbuga gefen pillow da nake kwance.
"Dame zaki karya?" Ya tambaye ni, nayi shiru dan baki na yayi mun nauyi kuma kusancin da mukayi ƙamshin turaren sa dake bugun hanci na duk se ya sake hautsinamun kai baki na har ya fara tara yawu alamar amai na son taso mun. Miƙewa yayi yana cewa
"Shikenan ai, tun jiya nake binki kina mun wulaƙanci. Fitina kike nema ni kuma ba zakiyi da ni ba" ya shige kitchen. Se maganar sa ta ma bani dariya, wai yana bina ina masa wulaƙanci Bilal kenan me abin mamaki. Ƙarfe tara na farka daga baccin da ban san sanda ya ɗauke ni ba, zazzaɓin ya saukar mun dan haka na miƙe ina kallon falon dake ta tashin ƙamshin turaren wuta da roomfreshener. Zancen gaskiya iya gyaran gidan Bilal ba duk mace ba. Haka nan idan ya bushi iska har canza jeren kujeru ya keyi. Se da nayi wanka nayi kwalliya cikin sababbin ɗinkin sallar da nayi kafin na shiga kitchen neman abinci. Doya ya dafa da sauce ɗin ƙwai. Dake akwai wuta se nayi microwaving na haɗa baƙin shayi na dawo falo na zauna kan carpet na shiga karyawa. Bilal ya shigo falon da sallama, kan kujerar dake kallo na ya zauna yana murmushi yace
"Ranki ya daɗe an tashi kenan". Kallon sa nayi ba yabo ba fallasa na gaishe shi. Surutu ya fara mun ina bin sa da eh da aa har na ƙare cin abincin na yunƙura zan maida kwanon kitchen ya karɓa se gashi ya dawo harda ruwa me sanyi ya ajiye mun.
"Yanzu Hajja ta kira ni kin ji kuma wai taron suna suke so suyi, na zata tun da aka wuce satin ga kuma daga ita har yaron ba wata lafiya ta ishe su ba ai se su haƙura ko?" Ya faɗa yana kallo na. Na gyara kwanciya ta nace
"Eh, dama Fadilan tace mun zatayi taron suna ai, kuma haihuwar fari ai ya kamata tayi dama kuma yawanci in dai C's ne se sati biyu akeyin taro ba ranar kwana bakwai ba"
"Amma dai ƙarawa mutane ɗawainiya ne, baki ga jiya nayi dare ba? Wai fa ɗan iskan mijin nan nata se jiya sannan suka zo da yayyen sa biyu wai bada haƙuri suka kawo wasu shegun kayan su a leda wai na barka. Wlh badan Hajja tace nayi shiru ba niyya nayi nace su tafi da tsiyar su tunda da basu kawo ba ɗin ma babu abin da aka fasa yi mata da ɗan nasu har suna cewa a musu lissafin abin da aka kashe na asibiti zasu biya kamar gaske" ya sake faɗa. Tun da ya fara maganar na zuba masa ido ina kallon sa, so nake nace masa kawo kaya a leda ai ba kansu aka fara ba ƙarewar kayan barka naga har lefe sun kai a leda me yasa dan an musu yanzu abin ze yi musu zafi amma na kasa faɗa saboda nasan ƙarshe ze iya juyawa maganar manufa yace na masa gori ko wani abu se kawai na datse zancen da cewa
"Allah ya rufa asiri kawai".