Sashe 69
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai da kin ɗakko mata ta gani dai tun da har ta tambaya" Mama ta faɗa bayan da na gaya mata yanda muka yi da Fadila, na taɓe baki kawai ba tare da na ce komai ba. Da gaske ban shirya sake ɗaukar kowanne wulaƙanci daga gurin su ba, ko Anty Labiba ba ta ce na tashi na ƙwaci yancina ba nima a karan kaina na ƙosa da abinda Hajja da yayanta suke yi mun, ko zan ɗaga wa wani ƙafa a cikin su yanzu ita Hajjan ce darajar ta haifi Bilal, bayan haka babu wani da zan sake takurawa kaina akan sai ya so ni, miji na ne kaɗai zan tabbatar da soyayyar sa gare ni ko ta halin ya ya.
Sai bayan la'asar na tafi gidan Anty Labiba saboda Abba da na yi ta jira ya dawo muyi sallama. A ɗakin ta ta sauke ni, tun kuma daga zuwa na na san yanzu ne zan yi jegon gaske, gyaran da nake ta zullumin ta ina zan fara da na zauna a can gida na nasan duk zata yi mun.
Har muka kwanta ina jiran tsammanin kiran Bilal ko dan zuwan su Fadila amma na ji shiru, sai da asubar washe gari na ga missed calls ɗin sa kiran kuma gurin ƙarfe biyu da rabi aka yi shi. Ban bi sahu ba na watsar da shi kuma ni da kaina na yi mamakin yanda na iya share shi duk da yanda zuciya ta take azazzalata da kewar sa da kuma son jin muryar sa amma na kanne, ina so na tabbatar da gaske ni kaɗai na ke haukana akan Bilal kamar yanda kowa yake cewa ko kuwa ba haka bane?
Ina cikin karyawa ya sake kira, ji na yi kamar an yi mun yayyafin ruwan sanyi, na saci kallon Anty Labiba dake rirriga Al'amin naga sam hankalin ta baya kaina, dama shayi ya rage ban ƙarasa shanyewa ba dan haka na miƙe da kofin har kuma na shige ɗaki aka yi sa'a bata ce mun komai ba. Ajiye wayar na yi ganin ta katse kafin na kai ga amsawa na cigaba da kurɓar shayin da ya daina mun daɗi a baki, na saki ajiyar zuciya jin wayar ta sake ɗaukar ƙara, duk da haka sai da ma ɗan ja aji kafin na amsa cikin shan ƙamshi.
"Lallai kin ji daɗin gida wato sai yanzu ma kika tashi" ya faɗa bayan da na amsa sallamar da ya farayi, gaishe shi na shiga yi ya amsa kafin ya sake cewa
"Ina fatan dai yanzu zuciyar gimbiya ta yi sanyi?"
"Da na ce maka zuciya ta tayi zafi ne?" Na faɗa sai ya sake kwantar da murya ya ce
"Shekaran jiya, daga kalamanki na san bakya cikin yanayi me daɗi a lokacin shiyasa na barki har tsayin jiya ki huta amma na kasa jurewa cikin dare bacci ya gaza ɗauka ta na kira ki amma baki amsa ba" ya ƙarasa da wani munafukin sauti kamar me shirin fashewa da kuka. Take jiki na ya hau tsuma, So da muradin kasancewa tare da shi irin wanda na ke ciki a koda yaushe suka motsa mun. Nima na narke murya na ce
"Ashe ma ka fahimci bana cikin yanayi mai daɗi amma ka kasa tsayawa ka lallashe ni"
"Ba haka bane" ya faɗa nayi saurin katse shi da cewa
"To yaya ne? Saboda bani da muhimmanci ne ko?" Na ƙarasa ina fashewa da kukan kissa. Tamkar lokacin yammatanci haka ya rikice ya shiga rarrashi na, ni kuma na samu yanda nake so na cigaba da kukan ina faɗar maganganun da na tabbatar zasu ƙara hargitsa masa tunani. Mun fi minti talatin muna waya yana rarrashi na ina ƙara botsarewa har kuma muka gama ban ji ya sako zancen zuwan su Fadila ba dan da farko na zata ko ta kai gulmar ne shi ne ya biyo kadi ashe ba haka ba ne.
Wunin ranar da sauran ranakun da suka biyo bayan ta cikin farin ciki na yi su saboda yanda Bilal ya rikice akan boren da na tayar masa, bini bini zai kira ni ya cigaba da bani haƙuri da maganganu masu daɗi haɗi da tsayawa a zuciya.
Kwanan mu uku a gidan Anty Labiba wanda ya kama kwanan Bilal biyar a Abuja ya gaya mun zai dawo jibi, kwanaki bakwai kenan kamar yanda dama ya sanar mun zai yi.
"Me zan samu idan na dawo My Halims? Kin san nayi kewar ki da yawa har ban san iyaka ba" ya faɗa cikin marairaicewa, maganar da yayi ta sa na ji ina ma ina can gida na zai dawo dan gaskiya nima nayi kewar sa da gaske musamman yanzu da nake ganin komai ya dai daitu idan ya dawo zamu cigaba da gudanar da rayuwa ne irin yanda na ke mafarkin kasancewa da shi.
Na sake nitsewa cikin gadon da nake kwance kafin na ce
"Nima na yi kewar ka sosai, zan girka maka duka favourites, har da alawar madara da Iloka zan yi maka" na ƙarasa cikin dariyar tsokana"
"Amma kin san ba abinda nake nufi kenan ba ko? Wane kalar abinci ne bana ci kin san a in da na sauka kuwa a Abuja kin san kalar daɗin abincin su?" Cewar Bilal. A shagwaɓe na ce
"Kana nufin abincin su ya fiye maka nawa daɗi kuma baka kewar girki na kenan?"
"Ba haka nake nufin ba ai kin sani a guri na komai na ki daban ne kawai dai ina gaya miki akwai abin da zan iya samu a ko ina akwai kuma wanda a gurin kaɗai zan samu na ci na ƙoshi kuma ya gamsar da ni".
Da maganar, da yanda ya yi maganar sai da na rufe ido saboda nauyi da kunyar da suka saukar mun, ina jin sa yana cewa
"Kawai ki san yanda zakiyi da ni shiyasa ma na gaya miki tun yau idan ba dan haka ba sai dai kawai na ce miki gani na dawo"
"Amma dai kasan jego nakeyi" na faɗa jin yana so ya mayar da maganar da gaske, ya ce
"And so? Ai kin fara sallah. Ni fa ba wani abu da zaki kawo mun uzuri da shi na karɓa, kawai ki shirya tarbata Hajiya".
Haka na shiga zullumin yanda zata kaya tsakanina da Bilal domin dai ko karen hauka ya cijeni ba zan biye masa muyi wani abu a cikin gidan Anty Labiba ba. Na ce kuma zan bishi na sani shine abu na ƙarshe da zanyi tunanin aikatawa, tsine mun zatayi kawai na bi duniya. Na dai yi ƙarfin halin sanar mata da zancen dawowar sa.
"Allah ya dawo da shi lafiya" ta faɗa na amsa da "Amin" daga nan muka yi shiru. Akwai shaƙuwa da sakewa tsakanina da ita da zan iya tattauna maganar da mukayi da Bilal amma yanda abubuwa suke tafiya yanzu a tsakanin mu nasan wani ruwan zan ɓallo duk da dai na lura dagaske kamar yanda ta faɗa babu ruwanta da sabgata da Bilal ta zame hannun ta a ciki ba wasa take yi ba.
Ranar da zai dawo ɗin da kanta tace na duba kitchen naga idan akwai abin da zan buƙata da babu a siyo, jirgin sha biyu ya ce zai biyo dan haka da wuri na fara girkin mai aikin ta ta taya ni kafin sha biyun mun gama komai. Bilal na sauka ya kira ni ya gaya mun,
"Na biyo mu tafi ko zaki zo daga baya?" Ya faɗa. Na rasa me zance masa sai kawai na ɓige da cewar bana jin sa na kashe wayar. Babu daɗewa ya sake kira na akan gashi a waje, da na gaya mata ta ce ya shigo mana ko kuma gidan baƙon sa ne.
Nayi zaton yanda yake nanata yayi kewata idan muka haɗu zai yi kamar ya cinyeni amma sai naga akasin haka, rungumar da ya mun ma ni ban wani ji ta ba, a gidan ya ci abinci yana ta mun hirar aikin da suka je. Anty Labiba suka fita harda Al'amin ta ce zasu je karɓo ɗinki ba jimawa zasuyi ba na yi zaton zaiyi amfani da wannan lokaci ya rage zafi kamar yanda yake ta kwakwazo a waya amma bai nuna alamar komai ba ƙarshe ya ɓige da nuna mun hotunan da ya yi a gurare cikin sabuwar wayar sa Iphone da ya siya. Sai da aka kira la'asar kafin ya ce mun zai tafi, ya ja ni jikin sa yana murmushin da ke wanke dukkan laifukan sa a gare ni ya ce
"Tun da na zo kike fushi kuma ko dai baki so dawowa ta bane?"
Gefe na ɗauke kai ba tare da na ce masa komai ba, ya juyo da fuskata ya haɗe bakin mu guri ɗaya.
Yanda kasan na rufe kaina da duka saboda takaicin yanda na kasa riƙe kaina a gaban Bilal. Da ya kira ni ma kasa amsa wayar na yi to na ce masa me bayan abin kunyar da na kusa tafkawa na je ina ta wani rawar jiki shi da yake namiji ma bai nuna min zumuɗin sa ba sai ni.
Kwanaki ukun da suka biyo baya kullum zai zo da daddare bayan magriba muyi hira har zuwa ƙarfe tara ko goma kafin ya tafi. Satin sa ɗaya da dawowa ya sake ce mun zai koma Abujan dama wai basu gama aikin ba kawai kewata ta saka ya zo. Dama Anty Labiba ta fara ƙananan maganganu akan ɗan abincin da yake ci idan ya zo abinda dama ko ya zo ko bai zo ba dole za'a dafa ba wai wani abu na daban na ke bashi ba da ta ke mita akai.
A haka muka cigaba da gungurawa har muka yi arba'in, a ranar kuma na tattara na koma gidana dan tun ana saura kwana uku aka je aka gyara mun Bilal ma ya dawo daga Abujar da na kasa gane abinda ya samu a can da ya tattare kusan sati uku tun da ya zo ya tafi bai sake dawowa sai yanzun.
Sai bayan la'asar na tafi gidan Anty Labiba saboda Abba da na yi ta jira ya dawo muyi sallama. A ɗakin ta ta sauke ni, tun kuma daga zuwa na na san yanzu ne zan yi jegon gaske, gyaran da nake ta zullumin ta ina zan fara da na zauna a can gida na nasan duk zata yi mun.
Har muka kwanta ina jiran tsammanin kiran Bilal ko dan zuwan su Fadila amma na ji shiru, sai da asubar washe gari na ga missed calls ɗin sa kiran kuma gurin ƙarfe biyu da rabi aka yi shi. Ban bi sahu ba na watsar da shi kuma ni da kaina na yi mamakin yanda na iya share shi duk da yanda zuciya ta take azazzalata da kewar sa da kuma son jin muryar sa amma na kanne, ina so na tabbatar da gaske ni kaɗai na ke haukana akan Bilal kamar yanda kowa yake cewa ko kuwa ba haka bane?
Ina cikin karyawa ya sake kira, ji na yi kamar an yi mun yayyafin ruwan sanyi, na saci kallon Anty Labiba dake rirriga Al'amin naga sam hankalin ta baya kaina, dama shayi ya rage ban ƙarasa shanyewa ba dan haka na miƙe da kofin har kuma na shige ɗaki aka yi sa'a bata ce mun komai ba. Ajiye wayar na yi ganin ta katse kafin na kai ga amsawa na cigaba da kurɓar shayin da ya daina mun daɗi a baki, na saki ajiyar zuciya jin wayar ta sake ɗaukar ƙara, duk da haka sai da ma ɗan ja aji kafin na amsa cikin shan ƙamshi.
"Lallai kin ji daɗin gida wato sai yanzu ma kika tashi" ya faɗa bayan da na amsa sallamar da ya farayi, gaishe shi na shiga yi ya amsa kafin ya sake cewa
"Ina fatan dai yanzu zuciyar gimbiya ta yi sanyi?"
"Da na ce maka zuciya ta tayi zafi ne?" Na faɗa sai ya sake kwantar da murya ya ce
"Shekaran jiya, daga kalamanki na san bakya cikin yanayi me daɗi a lokacin shiyasa na barki har tsayin jiya ki huta amma na kasa jurewa cikin dare bacci ya gaza ɗauka ta na kira ki amma baki amsa ba" ya ƙarasa da wani munafukin sauti kamar me shirin fashewa da kuka. Take jiki na ya hau tsuma, So da muradin kasancewa tare da shi irin wanda na ke ciki a koda yaushe suka motsa mun. Nima na narke murya na ce
"Ashe ma ka fahimci bana cikin yanayi mai daɗi amma ka kasa tsayawa ka lallashe ni"
"Ba haka bane" ya faɗa nayi saurin katse shi da cewa
"To yaya ne? Saboda bani da muhimmanci ne ko?" Na ƙarasa ina fashewa da kukan kissa. Tamkar lokacin yammatanci haka ya rikice ya shiga rarrashi na, ni kuma na samu yanda nake so na cigaba da kukan ina faɗar maganganun da na tabbatar zasu ƙara hargitsa masa tunani. Mun fi minti talatin muna waya yana rarrashi na ina ƙara botsarewa har kuma muka gama ban ji ya sako zancen zuwan su Fadila ba dan da farko na zata ko ta kai gulmar ne shi ne ya biyo kadi ashe ba haka ba ne.
Wunin ranar da sauran ranakun da suka biyo bayan ta cikin farin ciki na yi su saboda yanda Bilal ya rikice akan boren da na tayar masa, bini bini zai kira ni ya cigaba da bani haƙuri da maganganu masu daɗi haɗi da tsayawa a zuciya.
Kwanan mu uku a gidan Anty Labiba wanda ya kama kwanan Bilal biyar a Abuja ya gaya mun zai dawo jibi, kwanaki bakwai kenan kamar yanda dama ya sanar mun zai yi.
"Me zan samu idan na dawo My Halims? Kin san nayi kewar ki da yawa har ban san iyaka ba" ya faɗa cikin marairaicewa, maganar da yayi ta sa na ji ina ma ina can gida na zai dawo dan gaskiya nima nayi kewar sa da gaske musamman yanzu da nake ganin komai ya dai daitu idan ya dawo zamu cigaba da gudanar da rayuwa ne irin yanda na ke mafarkin kasancewa da shi.
Na sake nitsewa cikin gadon da nake kwance kafin na ce
"Nima na yi kewar ka sosai, zan girka maka duka favourites, har da alawar madara da Iloka zan yi maka" na ƙarasa cikin dariyar tsokana"
"Amma kin san ba abinda nake nufi kenan ba ko? Wane kalar abinci ne bana ci kin san a in da na sauka kuwa a Abuja kin san kalar daɗin abincin su?" Cewar Bilal. A shagwaɓe na ce
"Kana nufin abincin su ya fiye maka nawa daɗi kuma baka kewar girki na kenan?"
"Ba haka nake nufin ba ai kin sani a guri na komai na ki daban ne kawai dai ina gaya miki akwai abin da zan iya samu a ko ina akwai kuma wanda a gurin kaɗai zan samu na ci na ƙoshi kuma ya gamsar da ni".
Da maganar, da yanda ya yi maganar sai da na rufe ido saboda nauyi da kunyar da suka saukar mun, ina jin sa yana cewa
"Kawai ki san yanda zakiyi da ni shiyasa ma na gaya miki tun yau idan ba dan haka ba sai dai kawai na ce miki gani na dawo"
"Amma dai kasan jego nakeyi" na faɗa jin yana so ya mayar da maganar da gaske, ya ce
"And so? Ai kin fara sallah. Ni fa ba wani abu da zaki kawo mun uzuri da shi na karɓa, kawai ki shirya tarbata Hajiya".
Haka na shiga zullumin yanda zata kaya tsakanina da Bilal domin dai ko karen hauka ya cijeni ba zan biye masa muyi wani abu a cikin gidan Anty Labiba ba. Na ce kuma zan bishi na sani shine abu na ƙarshe da zanyi tunanin aikatawa, tsine mun zatayi kawai na bi duniya. Na dai yi ƙarfin halin sanar mata da zancen dawowar sa.
"Allah ya dawo da shi lafiya" ta faɗa na amsa da "Amin" daga nan muka yi shiru. Akwai shaƙuwa da sakewa tsakanina da ita da zan iya tattauna maganar da mukayi da Bilal amma yanda abubuwa suke tafiya yanzu a tsakanin mu nasan wani ruwan zan ɓallo duk da dai na lura dagaske kamar yanda ta faɗa babu ruwanta da sabgata da Bilal ta zame hannun ta a ciki ba wasa take yi ba.
Ranar da zai dawo ɗin da kanta tace na duba kitchen naga idan akwai abin da zan buƙata da babu a siyo, jirgin sha biyu ya ce zai biyo dan haka da wuri na fara girkin mai aikin ta ta taya ni kafin sha biyun mun gama komai. Bilal na sauka ya kira ni ya gaya mun,
"Na biyo mu tafi ko zaki zo daga baya?" Ya faɗa. Na rasa me zance masa sai kawai na ɓige da cewar bana jin sa na kashe wayar. Babu daɗewa ya sake kira na akan gashi a waje, da na gaya mata ta ce ya shigo mana ko kuma gidan baƙon sa ne.
Nayi zaton yanda yake nanata yayi kewata idan muka haɗu zai yi kamar ya cinyeni amma sai naga akasin haka, rungumar da ya mun ma ni ban wani ji ta ba, a gidan ya ci abinci yana ta mun hirar aikin da suka je. Anty Labiba suka fita harda Al'amin ta ce zasu je karɓo ɗinki ba jimawa zasuyi ba na yi zaton zaiyi amfani da wannan lokaci ya rage zafi kamar yanda yake ta kwakwazo a waya amma bai nuna alamar komai ba ƙarshe ya ɓige da nuna mun hotunan da ya yi a gurare cikin sabuwar wayar sa Iphone da ya siya. Sai da aka kira la'asar kafin ya ce mun zai tafi, ya ja ni jikin sa yana murmushin da ke wanke dukkan laifukan sa a gare ni ya ce
"Tun da na zo kike fushi kuma ko dai baki so dawowa ta bane?"
Gefe na ɗauke kai ba tare da na ce masa komai ba, ya juyo da fuskata ya haɗe bakin mu guri ɗaya.
Yanda kasan na rufe kaina da duka saboda takaicin yanda na kasa riƙe kaina a gaban Bilal. Da ya kira ni ma kasa amsa wayar na yi to na ce masa me bayan abin kunyar da na kusa tafkawa na je ina ta wani rawar jiki shi da yake namiji ma bai nuna min zumuɗin sa ba sai ni.
Kwanaki ukun da suka biyo baya kullum zai zo da daddare bayan magriba muyi hira har zuwa ƙarfe tara ko goma kafin ya tafi. Satin sa ɗaya da dawowa ya sake ce mun zai koma Abujan dama wai basu gama aikin ba kawai kewata ta saka ya zo. Dama Anty Labiba ta fara ƙananan maganganu akan ɗan abincin da yake ci idan ya zo abinda dama ko ya zo ko bai zo ba dole za'a dafa ba wai wani abu na daban na ke bashi ba da ta ke mita akai.
A haka muka cigaba da gungurawa har muka yi arba'in, a ranar kuma na tattara na koma gidana dan tun ana saura kwana uku aka je aka gyara mun Bilal ma ya dawo daga Abujar da na kasa gane abinda ya samu a can da ya tattare kusan sati uku tun da ya zo ya tafi bai sake dawowa sai yanzun.