Sashe 3
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wannan halin naki yake tabbatar mun zaki kula da cikina idan mukayi aure, Allah dai yayi miki albarka ya barmu tare my Halims" ya faɗa sanda ya karɓi ledar. Muka jera yana mun surutu, seda na buɗe masa get ya fita da mashin na rufe kafin na fita na same shi ya ɗaure ledar yanda abin ciki ba zasu zube ba kafin ya hau mashin ɗin yana kallona yace
"Da yanzu zaki wuce gida se mu tafi na ɗana ki". Tunda yazo nake raya in masa magana akan da canza mashin ɗin da yayi dama gini ya cigaba ko yayi amfani kuɗin ya haɗa kayan saka ranar tunda dai tsohon nasan babu abinda yayi ai amma gudun kar yaga na shiga rayuwarsa yasa nayi shiru se nace
"To bari kawai nayiwa Anty Labiba sallama se mu tafi dama na gaji gashi kuma gobe ina da practical exam ina so nayi karatu" na juya cikin gidan.
Toshe kunne kawai nayi na haɗa kayana na gudu na bar mata wanke wanke ina tana faɗin zan sake zuwa ne na tafi, faɗan mu ba wani jimawa yake ba da kanta ma zata nemo ni musamman yanzu da yara zasuyi hutun makaranta ga tsohon ciki tana dashi dole ta nemo me tayata da kayaniyar yaran. Na ɗane tsuntsun soyayya ya lula damu muna tafe yana mun surutan da ba wani ji nake sosai ba saboda iska har muka isa sabon titi gidan mu. A bakin gate ya tsaya na sauka ya kalli ginin benen da ake ɗora mana da har an fara fenti yace
"Ashe aikin nan yayi nisa haka, wato mu talakawa ne muke jin garin nan masu kuɗi sha'aninku kawai kikeyi". Fuska ta ba yabo ba fallasa ban dai ce masa komai ba ya shiga laluben aljihu, harga Allah na saka ran tunda yace mun ya siyi mashin idan ya tashi zuwa ko 5k ce ze bani shiyasa ma banji komai ba na kashe kuɗin transport ɗina na sati da Abba ya bani nayi masa abinci ko be biyani duka ba a ƙalla zan rage wani abun musamman da yake ta koɗa daɗin abincin yana faɗin na cancanci tukuici ganin yana laluben Aljihun yasa nayi ɗan murmushi ina jira se naga ya zaro wayarsa ya buɗe kafin ya juyo yana cewa
"Bari in sake miki hoto wlh kin mun kyau yau ɗin nan irin sosai fa My Halims.
Takaici ya kamani amma haka na gyara ya shiga ɗauka na hoton seda aka kira sallah kafin yamun sallama ya burga mashin ɗinsa ya tafi na juya jiki ba ƙwari na shiga gida a raina ina ayyana ƙila se jibi da yace ze zo ko kuma ya mun transfer.
[12/12/2024, 3:30 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi.*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 2*
Washe gari daƙyar na yakice bacci nayi shirin makaranta, ina gama karatu Bilal ya kirani har gurin ƙarfe ɗaya muna hira kafin ya barni na kwanta dama ga gajiyar dana kwaso a makaranta jiyan na ɗora data girki sannan dana dawo gidan ma ban zauna ba na tarar anyi fenti a ɗakina gaba ɗaya an hargitsamun kaya seda na gyara su sannan na kwanta. Shaf na manta da munyi faɗa da Hansa'u jiya na zauna jiran zuwanta har ƙarfe tara seda na kirata sau biyu bata amsa ba wanda nasan ba halin ta bane da wuya na kirata a waya bata amsa ba sedai irin haka idan munyi faɗa. A fili nace
"Lallai, wai ita ta ɗauki abun har zuci ashe. Ni da ya kamata nayi fushi ta zagar mun Habibi banyi ba se ita? To ai shikenan" na ɗauki jakata da Lab coat na fito falo na tarar da Mama tana ware atamfofi. Sau biyu ina ce mata zan tafi tana mun Allah ya tsare hanya. Ɗari biyar ce a jakata, zata kaini ta dawo dani amma bani da canjin da zanci wani abu kuma yau ɗin wuni zamuyi se ƙarfe huɗu zuwa biyar zamu taso. Ganin na tsaya yasa ta tambayeni lafiya? Na shiga sosa kai, tsaki kawai Mama tayi ta buɗe POS ɗin ta dake gefe ta zaro dubu ɗaya ta miƙa mun tana cewa
"Banda shegen iyayinki me yasa baki zo kin masa abincin a nan ba?" Karɓa nayi tareda mata godiya na fita. Ina son Mama, bata zafafawa a lamuranta. Nasan ba wani son zancen aure na da Bilal take ba musamman yanda duk yan uwanta suke sukar abun amma tunda nida Abba muna son ita ma ta karɓa tana mana addu'a.
Seda muka fito break kafin muka tsaya da Hansa'u nace mata "wai saboda maganar jiya yasa baki biyo mun ba yau kuma na kiraki baki amsa ba?"
"In biyo miki kuma? Ina ce kikayi kowa tasa ta fishsheki babu kr babu ni akan Bilal iyayenki ne kawai na zaki bari ba. To tunda ni ba iyayenki bace ai gara na tattara tsumman rayuwata na baki guri tunda baki na baze iya shiru ba har idan naga abinda ba daidai ba se nayi magana" Hansa'u ta bani amsa, sena rungumeta ina cewa
"Haba ƙawata ki barni in kama wa? Ai kin san dai tsakani na dake ya wuce ƙawance kema yar uwata ce kina cikin waɗanda bazan rabu dasu ba ai" ta mun banza, dake nasan nice da laifi dukda naji haushin abinda ta faɗa akan Bilal amma kuma nima abinda na mata ya shallake wanda tamun hakan tasa na ringa bata haƙuri harta sakko muka tafi siyo fanke da lemo. Bayan mun zauna nace mata
"Amma tsakani da Hansy dole a ringa jin kanmu har idan zaki ringa taɓa mun Yarima. Ya kamata ki ringa mun kara, ko baki son Bilal darajar ƙaunar dake tsakani na dashi ai yaci ki mun kara. Bana so ki dena zaginsa a gabana idan ma zaki zage shi kiyi can a inda bazanji ba dan nima bazan miki kara ba sena rama masa"
"Ai shikenan, ni dai bazan zauna tare dake ina kallo kina ƙoƙarin jefa kanki a halaka kuma nayi shiru na barki ba dole in faɗa miki gaskiya ko ki ɗauka ko karki ɗauka ruwanki" ta bani amsa, a hasale nace
"Auren Bilal ɗin ne kike kira da halaka Hansa'u? Wai me kike nufi da Bilal ne? Ki gaya mun me yake aikatawa da har kike kiran aurensa da jefa kai a halaka wane mugun hali yake dashi da ban sani ba?" Na ƙarasa ina miƙewa tsaye. Watsa hannu tayi tace
"Kin fini sanin halakar da nake nufi sedai idan kin so ne zakiwa maganata mummunar fassara. Akwai halakar duniya data wuce mace tayi rashin dacen mijin aure? Bilal be dace dake ba, kiso ko karki so sena faɗa ke kike sonsa amma shi ba sonki yake ba idan ma kuma yana sonki to akwai dalilinsa na hakan amma ba zaki fahimci abinda nake faɗa miki yanzu ba ba kuma na miki fatan kiyi nadamar kin jij maganar masu sonki a sanda komai ya lalace miki. Tun wuri ga maza fululu masu ƙaunar ki dagaske ki nemi mijin aure a cikinsu ina mai tabbatar miki har ba Allah ya ƙaddara ba Bilal ya samu wadda ta fiki sedai kiji wani zancen wlh" ta ƙarasa tana bari na a gurin. A maimakon sulhu se gashi mun sake tafka wani faɗan dan da aka tashi ban tafi ba seda na sameta na sake zazzaga mata rashin mutunchi na faɗa mata nasan baƙin ciki take mun ba wani abu da saboda na samu me so na zamuyi auren soyayya da ƙuruciyarmu ba irinta ba da zata auri tsoho sa'an Babanta shine take mun baƙin ciki. Kwaɗayin daya kaita ta amsa zata auri tsoho shi zesa ta haɗiyi baƙin cikinta ta kalle mu ni da Habibi na musha soyayya. A bakin titi na cimmata suna jiran Adaidaita da ƙawayenmu biyu Zainab da Hussaina duk yan unguwar mu ne tare muke tafiya dama. Hansa'u ta ringa kuka ko a jikina su biyun ma da suka shigar mata nayi musu tatas nayi tafiyata na barsu raina fes domin ba wanda ya isa ya taɓa Bilal na barshi, dama ta kama kanta ta fita a sabgata dashi se mu cigaba da lallaɓa zumunchin mu amma ta soka kanta a inda ba'a gayyaceta ba.
Dana koma gida tsaf na kwashe labari na bawa Bilal daya kirani, ga mamakina se yace wai ban kyauta ba me yasa zan mata haka ai kamata yayi naji uzurinta domin yanda muke da ita kowa yasan ba zata cutar dani ba
"Kenan ka yarda kana da mugun halin da har zata ringa faɗar irin Maganganun nan akanka?" Na tambayeshi, se yace
"No Halims ba haka bane. Abinda nake nufi da se ki mata uzuri ki bita a hankali kiji menene hujjojinta amma yanzu abinda kika mata gaskiya baki kyauta ba ai tsakaninku ya zarce haka gaskiya banji daɗi ba" ya ringa mun faɗa har naji haushi ma na kashe wayar.
Kwana biyu da suka biyo baya banje makaranta ba mun samu interval kafin mu fara theory parts na jarabawa. Tun a washe gari da Mama taga har yamma bance zanje gidansu Hansa'u ba ita kuma bata ga tazo ba ta tambayeni ko lafiya se kawai nace mata jiya da muka taho gadon ƙaya ta wuce gidan yayarsu. A washe garin ranar da rana Abba ya dawo daga Enugu sunje wani aiki da magriba bayan ya dawo daga masallaci ina ɗakina na idar da sallah na jiyo yana ƙwala mun kira, Abba bashi da faɗa daga sautin muryarsa na san akwai wani abu abinda ya fara zuwar mun ko zancen Bilal ze mun tunda yace kafin ya dawo musan abinda muke ciki.
"Da yanzu zaki wuce gida se mu tafi na ɗana ki". Tunda yazo nake raya in masa magana akan da canza mashin ɗin da yayi dama gini ya cigaba ko yayi amfani kuɗin ya haɗa kayan saka ranar tunda dai tsohon nasan babu abinda yayi ai amma gudun kar yaga na shiga rayuwarsa yasa nayi shiru se nace
"To bari kawai nayiwa Anty Labiba sallama se mu tafi dama na gaji gashi kuma gobe ina da practical exam ina so nayi karatu" na juya cikin gidan.
Toshe kunne kawai nayi na haɗa kayana na gudu na bar mata wanke wanke ina tana faɗin zan sake zuwa ne na tafi, faɗan mu ba wani jimawa yake ba da kanta ma zata nemo ni musamman yanzu da yara zasuyi hutun makaranta ga tsohon ciki tana dashi dole ta nemo me tayata da kayaniyar yaran. Na ɗane tsuntsun soyayya ya lula damu muna tafe yana mun surutan da ba wani ji nake sosai ba saboda iska har muka isa sabon titi gidan mu. A bakin gate ya tsaya na sauka ya kalli ginin benen da ake ɗora mana da har an fara fenti yace
"Ashe aikin nan yayi nisa haka, wato mu talakawa ne muke jin garin nan masu kuɗi sha'aninku kawai kikeyi". Fuska ta ba yabo ba fallasa ban dai ce masa komai ba ya shiga laluben aljihu, harga Allah na saka ran tunda yace mun ya siyi mashin idan ya tashi zuwa ko 5k ce ze bani shiyasa ma banji komai ba na kashe kuɗin transport ɗina na sati da Abba ya bani nayi masa abinci ko be biyani duka ba a ƙalla zan rage wani abun musamman da yake ta koɗa daɗin abincin yana faɗin na cancanci tukuici ganin yana laluben Aljihun yasa nayi ɗan murmushi ina jira se naga ya zaro wayarsa ya buɗe kafin ya juyo yana cewa
"Bari in sake miki hoto wlh kin mun kyau yau ɗin nan irin sosai fa My Halims.
Takaici ya kamani amma haka na gyara ya shiga ɗauka na hoton seda aka kira sallah kafin yamun sallama ya burga mashin ɗinsa ya tafi na juya jiki ba ƙwari na shiga gida a raina ina ayyana ƙila se jibi da yace ze zo ko kuma ya mun transfer.
[12/12/2024, 3:30 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi.*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 2*
Washe gari daƙyar na yakice bacci nayi shirin makaranta, ina gama karatu Bilal ya kirani har gurin ƙarfe ɗaya muna hira kafin ya barni na kwanta dama ga gajiyar dana kwaso a makaranta jiyan na ɗora data girki sannan dana dawo gidan ma ban zauna ba na tarar anyi fenti a ɗakina gaba ɗaya an hargitsamun kaya seda na gyara su sannan na kwanta. Shaf na manta da munyi faɗa da Hansa'u jiya na zauna jiran zuwanta har ƙarfe tara seda na kirata sau biyu bata amsa ba wanda nasan ba halin ta bane da wuya na kirata a waya bata amsa ba sedai irin haka idan munyi faɗa. A fili nace
"Lallai, wai ita ta ɗauki abun har zuci ashe. Ni da ya kamata nayi fushi ta zagar mun Habibi banyi ba se ita? To ai shikenan" na ɗauki jakata da Lab coat na fito falo na tarar da Mama tana ware atamfofi. Sau biyu ina ce mata zan tafi tana mun Allah ya tsare hanya. Ɗari biyar ce a jakata, zata kaini ta dawo dani amma bani da canjin da zanci wani abu kuma yau ɗin wuni zamuyi se ƙarfe huɗu zuwa biyar zamu taso. Ganin na tsaya yasa ta tambayeni lafiya? Na shiga sosa kai, tsaki kawai Mama tayi ta buɗe POS ɗin ta dake gefe ta zaro dubu ɗaya ta miƙa mun tana cewa
"Banda shegen iyayinki me yasa baki zo kin masa abincin a nan ba?" Karɓa nayi tareda mata godiya na fita. Ina son Mama, bata zafafawa a lamuranta. Nasan ba wani son zancen aure na da Bilal take ba musamman yanda duk yan uwanta suke sukar abun amma tunda nida Abba muna son ita ma ta karɓa tana mana addu'a.
Seda muka fito break kafin muka tsaya da Hansa'u nace mata "wai saboda maganar jiya yasa baki biyo mun ba yau kuma na kiraki baki amsa ba?"
"In biyo miki kuma? Ina ce kikayi kowa tasa ta fishsheki babu kr babu ni akan Bilal iyayenki ne kawai na zaki bari ba. To tunda ni ba iyayenki bace ai gara na tattara tsumman rayuwata na baki guri tunda baki na baze iya shiru ba har idan naga abinda ba daidai ba se nayi magana" Hansa'u ta bani amsa, sena rungumeta ina cewa
"Haba ƙawata ki barni in kama wa? Ai kin san dai tsakani na dake ya wuce ƙawance kema yar uwata ce kina cikin waɗanda bazan rabu dasu ba ai" ta mun banza, dake nasan nice da laifi dukda naji haushin abinda ta faɗa akan Bilal amma kuma nima abinda na mata ya shallake wanda tamun hakan tasa na ringa bata haƙuri harta sakko muka tafi siyo fanke da lemo. Bayan mun zauna nace mata
"Amma tsakani da Hansy dole a ringa jin kanmu har idan zaki ringa taɓa mun Yarima. Ya kamata ki ringa mun kara, ko baki son Bilal darajar ƙaunar dake tsakani na dashi ai yaci ki mun kara. Bana so ki dena zaginsa a gabana idan ma zaki zage shi kiyi can a inda bazanji ba dan nima bazan miki kara ba sena rama masa"
"Ai shikenan, ni dai bazan zauna tare dake ina kallo kina ƙoƙarin jefa kanki a halaka kuma nayi shiru na barki ba dole in faɗa miki gaskiya ko ki ɗauka ko karki ɗauka ruwanki" ta bani amsa, a hasale nace
"Auren Bilal ɗin ne kike kira da halaka Hansa'u? Wai me kike nufi da Bilal ne? Ki gaya mun me yake aikatawa da har kike kiran aurensa da jefa kai a halaka wane mugun hali yake dashi da ban sani ba?" Na ƙarasa ina miƙewa tsaye. Watsa hannu tayi tace
"Kin fini sanin halakar da nake nufi sedai idan kin so ne zakiwa maganata mummunar fassara. Akwai halakar duniya data wuce mace tayi rashin dacen mijin aure? Bilal be dace dake ba, kiso ko karki so sena faɗa ke kike sonsa amma shi ba sonki yake ba idan ma kuma yana sonki to akwai dalilinsa na hakan amma ba zaki fahimci abinda nake faɗa miki yanzu ba ba kuma na miki fatan kiyi nadamar kin jij maganar masu sonki a sanda komai ya lalace miki. Tun wuri ga maza fululu masu ƙaunar ki dagaske ki nemi mijin aure a cikinsu ina mai tabbatar miki har ba Allah ya ƙaddara ba Bilal ya samu wadda ta fiki sedai kiji wani zancen wlh" ta ƙarasa tana bari na a gurin. A maimakon sulhu se gashi mun sake tafka wani faɗan dan da aka tashi ban tafi ba seda na sameta na sake zazzaga mata rashin mutunchi na faɗa mata nasan baƙin ciki take mun ba wani abu da saboda na samu me so na zamuyi auren soyayya da ƙuruciyarmu ba irinta ba da zata auri tsoho sa'an Babanta shine take mun baƙin ciki. Kwaɗayin daya kaita ta amsa zata auri tsoho shi zesa ta haɗiyi baƙin cikinta ta kalle mu ni da Habibi na musha soyayya. A bakin titi na cimmata suna jiran Adaidaita da ƙawayenmu biyu Zainab da Hussaina duk yan unguwar mu ne tare muke tafiya dama. Hansa'u ta ringa kuka ko a jikina su biyun ma da suka shigar mata nayi musu tatas nayi tafiyata na barsu raina fes domin ba wanda ya isa ya taɓa Bilal na barshi, dama ta kama kanta ta fita a sabgata dashi se mu cigaba da lallaɓa zumunchin mu amma ta soka kanta a inda ba'a gayyaceta ba.
Dana koma gida tsaf na kwashe labari na bawa Bilal daya kirani, ga mamakina se yace wai ban kyauta ba me yasa zan mata haka ai kamata yayi naji uzurinta domin yanda muke da ita kowa yasan ba zata cutar dani ba
"Kenan ka yarda kana da mugun halin da har zata ringa faɗar irin Maganganun nan akanka?" Na tambayeshi, se yace
"No Halims ba haka bane. Abinda nake nufi da se ki mata uzuri ki bita a hankali kiji menene hujjojinta amma yanzu abinda kika mata gaskiya baki kyauta ba ai tsakaninku ya zarce haka gaskiya banji daɗi ba" ya ringa mun faɗa har naji haushi ma na kashe wayar.
Kwana biyu da suka biyo baya banje makaranta ba mun samu interval kafin mu fara theory parts na jarabawa. Tun a washe gari da Mama taga har yamma bance zanje gidansu Hansa'u ba ita kuma bata ga tazo ba ta tambayeni ko lafiya se kawai nace mata jiya da muka taho gadon ƙaya ta wuce gidan yayarsu. A washe garin ranar da rana Abba ya dawo daga Enugu sunje wani aiki da magriba bayan ya dawo daga masallaci ina ɗakina na idar da sallah na jiyo yana ƙwala mun kira, Abba bashi da faɗa daga sautin muryarsa na san akwai wani abu abinda ya fara zuwar mun ko zancen Bilal ze mun tunda yace kafin ya dawo musan abinda muke ciki.