Sashe 127
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A haka suka kwashe kusan shekaru biyu da Nura kafin ya tafi ƙasar waje karatu tun daga nan kuma har kawo yau bata sake ko jin labarinsa ba dan dama ba yan Kano bane daga baya suka bar can unguwar tun ma kafin su Zulaihan su bari. Rabuwarsu da Nura ta saka ta rasa abubuwa da yawa waɗanda yakeyi mata, babu tsoron Allah Ummansu ta ce ai ba zasu zauna haka ba, tunda dai ko da batada fuskar da zata burge maza dukda ƙananan shekarunta da yake tana da garin jiki ai ba zata gagara nemo musu abinda zasu ringa kaiwa bakin salati ba.
Daga nan ta fara zuwa gurin masu shaguna, wasu su biye mata su bata kuɗi ko abin amfani masu tsoron Allah su kai ƙara gurin mahaifinsu wanda yake tamkar hoto dan ko ya faɗa ba ji zatayi ba tunda uwarta ta tsaya mata. A haka Bilal ya shiga rayuwarsu zuwansa kuma ya kawo sauƙi cikin al'amuran domin kan jiki kan karɓi yake tallafa musu kuma shi yayi fafutuka ya samawa Babansu motar haya da yake direba ne yake hawa abinda yake samowa da wanda Bilal ɗin yake basu ya taimaka ƙwarai har Zulaihan ta hau saiti ta mayar da hankali kan karatu.
Sai dai kuma daga sanda ta shiga shekarun budurci na sosai a lokacin mahaifin su ya samu hatsari ya gamu da jinyar da bai warke ba har ya koma ga mahaliccinsa sai ya zamana Bilal ne kaɗai madogararsu dan haka ta sake komawa ruwa har tayi nasarar jan ƙanwarta Nuratu da huɗubar Ummansu wacce kullum take mata tilawar ba zai yuwu ta zauna yar uwarta ta nemo a ci da ita ba tunda itama tana da abin bayarwa idan ta zauna duk idan aurenta ya tashi kada tayi kuka da kowa ta kuka da kanta.
Tafiyar kuma ta canza salo sanda ta shiga Jami'a ta haɗu da gogaggun da suka fita ido a harkar, haka ta ringa zuba sharafinta cikin takatsantsan kuma Allah ya ara mata lokaci musamman da suka koma unguwar da babu wanda ya sansu suka fara sabuwar rayuwa.
Kullum ƙawayenta suna mata mitar basuga amfanin kuɗin da take samu ba domin dai kullum ka ganta tana nan kalar tausayi cikin tsumma ba sutura mai kyau mayukan gyaran fata da turaruka ma saboda ƙorafin mazan da take ta'ammali dasu ya saka ta fara siya saboda ta gyara jikinta duk a salon kada a fahimci halin da take ciki ya saka take takatsantsan da gudun mallakar duk wani abu da zai janyo hankalin mutane kanta, suna dai cin daɗi a cikinsu amma abubuwan more rayuwa dole ta haƙura da su saboda gujewa zargi sai dai tayi ta tara kuɗin idan sunyi yawa ta siyi wani abu kamar zobe ko fili ta ajiye.
A silar Nuratun asirinsu ya tonu har yan uwan mahaifinsu suka san halin da suke ciki dukda suna ji a jita jita wanda kuma da yawa Bilal da kowa ya san yana wahalta musu har gida ya siya musu shi mutane sukewa kallon abokin shashancin nata domin dai a rayuwar da muke ciki yanzu haka kawai wani bare ya ringa maka hidima kwatankwacin wacce yake musu tabbas abar dubawa ce dukda na Allah basa ƙarewa a duniya.
Ciki Nuratun tayi wanda baƙin cikin haka shine silar ajalin mahaifinsu. Ita bata kai wayewa da buɗewar idon Zulaihan ba kusan ma tursasawata sukayi ta shiga rayuwar da ba tata ba, bata ma san da tayi cikin ba har saida ya bayyana kansa fallasa kansa tukunna aka sha gurmi da dangin Babansu duk kuma yanda Umman da Zulaiha suka kaɗa suka raya tace ba zata zubar ba iya zunubin data kwasa harta same shi ya isheta ba zasu ɗora mata wani ba da Allah kuma ya nufa ba mai taka ƙasa bane tayi ɓari dukda da saka hannun su Zulaihan daga nan kuma ta tuba ita kanta Zulaihan daga lokacin ta rage abubuwa da yawa musamman kuma da Bilal ya fara taso da maganar aurensu ta shiga tsoron kar maganar ta koma masa a samu matsala dukda dai na Nuratu ne ya fito fili ita aka san bata ji amma ta san hakan zai iya shafarta shiyasa ta tattara hankalinta guri ɗaya ta saki harkar dama kuma tayi alƙawarin daga sanda aka saka musu rana zata bari to hakance ta kasance ta dena zuwa gurin kowa sai dai yan dabaru na waya data cigaba domin cigaba da samun kuɗin riƙe kai zuwa sanda zatayi auren.
Sai da ta cire Bedsheet ɗin da ɗaure shi a leda domin ba zata iya wankewa ba dama kuma amfaninsa kenan bata shimfiɗa wani ba ta shiga wanka a gurguje sai dai tana saɓa sabulu ta jiyo bugun ƙofa ta kasa kunne taji ko Bilal data leƙa falo ta ganshi a kwance zai tashi ya buɗe amma shiru shine ta zuciya ta fito da kumfa a jikinta zataje ta buɗe musu.
Wankan ta koma bayan sun gama iyashegensu suna tsokanarta wai amarya suka ringa dariyar da su suka san dalilinta sanin yana gidan kuma ya saka suka kama bakunansu dake cike da maganganu da son jin ya aka ƙare, abubuwan da suka kashe kuɗi tayi dan ta lulluɓe rayuwarta ta baya sun ci ko kuwa an samu akasi?
Wanka ta koma ta barsu suna haɗa TV da suka biya suka karɓo mata, Asmy ta ce bata karya ba gashi dan wulaƙanci bata ajiye musu sauran kaza ba kamar yanda ta ce sun cinye dan haka ta duba kitchen babu komai sai kayan shayi da burodi, ganin akwai ƙwai da mai babu albasa dai haka ta fitar da camping gas tsakar gidan suka ɗora ruwan tea bayan ya tafasa aka soua ƙwai dan ma Suby ta taho mata kayan spices garda garlic powder da yayarta ta bata gudummawa shi suka saka a ƙwan da suka fashe kusan rabin creat suka baje a falo suka karya tareda amarya bayan ta yi sallah ta fito.
Suna tsaka da jin labarin yanda akayi ya kirata, tayi tsaki bayan ta kashe wayar ta ce
"Banda rashin Imani ya raba dare yana sukuwa akaina yanzu gari ya waye ya ce wai in bashi abin kari maimakon shi ya dafa mun".
Sadiya ta ce
"Maganar gaskiya ba shiya kamata ki haɗawa abinci harda farfesu ma saboda ya mayar da jinin jikinsa dan abinda kika zuƙe ya fi ƙarfin ruwa ma" gaba ɗaya suka sheƙe da dariyar shaƙiyanci suna tafawa. A wani shegen tea flask iya ta da ta zuba masa ruwan zafin data taro a banɗaki ta haɗa da guntun bread ɗin da suka rage da sauran Milo dan sun shanye ledar Peak 500g daya siyo, a hannu ta riƙe kayan Suby na cewa ta ɗora a try mana tayi wucewarta.
BILAL
Kallon sama zuwa ƙasa yayi mata kafin ya tsayar da idonsa kan hannunta yana duban abinda ta ruƙo harta dungurar dasu a gabansa tana cika tana batsewa ko me ta tuna kuma sai ta saki fuska kaɗan ta zauna a gefensa ta shiga gaishe shi tana ƙoƙarin shiga jikinsa cike da kissa. Janyeta yayi ya miƙe zaune daƙyar dan kwanciyar da yayi zazzaɓi ya rufe shi, ya dafw kansa dake bugawa yana kallon kayan dake gabansa kafin ya ce
"Menene wannan?"
"Breakfast mana" ta faɗa tana sake matsawa kusa da shi dan ganinsa da tayi babu riga ya saka ta fara jin muradin kasancewa dashi dan abubuwan data sha jiya basu gama sakinta ba dukda taga alama shi nasa ya sake shi.
"Ni zanci wannan sauran biredin sai kace wani almajiri kuma ina madarar?" Ya faɗa, ta yamutsa fuska ta ce
"Ai dai kana kallo baƙi nayi ka godewa Allah ma daka samu sauran madara kuma sun shanye"ta ƙarasa tana harararsa. Da mamaki ya ce
"Ita madarar suka shanye duka?"
"Dan Allah ji yanda kake magana sai kace wanda suka shanye bugu ɗaya, su huɗu fa, ko ni kaɗai waccen yar madarar da ƙalau nake ai zama ɗaya zan shanyeta".
Kasa ce mata komai yayi ya tsaya kawai yana kallonta kafin ya sauke ajiyar zuciya ya koma ya kwanta saboda yanda zazzaɓin yake nuƙurƙusar jikinsa ya ce
"Ki soya mun ƙwai toh".
Haka ya ringa tura ƙwan daya ga kamar da gayya aka ƙone shi ga ga uban ƙarni daƙyar ya iya haɗa Milon a kofin robar data haɗo masa da shi. Safiyarsu ta farko da Halima ta shiga dawo masa, dukda yanda ta ke a wani yanayi na shiga sabuwar rayuwa haka ta ringa kai da kawowa bata nutsu ba saida ta cika masa dining da lafiyayyun breakfast bayan dankali da ƙwai nama kansu kusan kala uku ga sauran kazar amarci ga wanda aka taho mata da su daga gida komai cikin kwanuka na alfarma suna ci suna annashuwa amma yau shine aka bawa sauran biredi a gidansa da shayi a flask ɗin roba da kofin roba kuma babu yanda ya iya ya ci.
Baccin wahala ya sake komawa bayan ya sha paracetamol Zulaiha kuwa dama tunda ta dangwarar masa da ƙwan ta koma gurin ƙawayenta suka cigaba da sabgarsu.
HALIMA
Dole ta saka nake ƙarfafa jikina domin na yiwa kaina alƙawarin ƙaryata Bilal da yake cewa dole ya san zan neme shi. Ina son sa ba zan ƙaryata hakan ba amma kuma ni da kaina dana nutsu na fahimci cewar rabuwata da shi shine alkhairi a tare da ni.
Daga kalaman daya kalli idona ya faɗa mun na tabbatar dagaske yakeyi baya so na, albarkacin soyayyar da nakeyi masa ta saka ya aureni idan ma kuma yana so na ɗin tunda ya fahimci so na ya fi nasa yawa ya sakawa ransa zan zauna dashi komai wahala zan jure shine dalilin daya saka ya ringa azabtar dani a fili da baɗini har kuma da yake gargadar rasani bai yi nadamar hakan ba sai ma ƙara tabbatar mun da yakeyi ya sani ba zan iya rayuwa da waninsa ba.
Tsayin wata biyu da nayi tun barowata daga gidansa bai biyo ni ba ko a waya bai kirani ba sai yanzu haka wani nasa bai zo ba duk sai bayan da iyayena suka ɗauki matakin da suke ganin shi zai kawo mun maslaha a rayuwata.
Daga nan ta fara zuwa gurin masu shaguna, wasu su biye mata su bata kuɗi ko abin amfani masu tsoron Allah su kai ƙara gurin mahaifinsu wanda yake tamkar hoto dan ko ya faɗa ba ji zatayi ba tunda uwarta ta tsaya mata. A haka Bilal ya shiga rayuwarsu zuwansa kuma ya kawo sauƙi cikin al'amuran domin kan jiki kan karɓi yake tallafa musu kuma shi yayi fafutuka ya samawa Babansu motar haya da yake direba ne yake hawa abinda yake samowa da wanda Bilal ɗin yake basu ya taimaka ƙwarai har Zulaihan ta hau saiti ta mayar da hankali kan karatu.
Sai dai kuma daga sanda ta shiga shekarun budurci na sosai a lokacin mahaifin su ya samu hatsari ya gamu da jinyar da bai warke ba har ya koma ga mahaliccinsa sai ya zamana Bilal ne kaɗai madogararsu dan haka ta sake komawa ruwa har tayi nasarar jan ƙanwarta Nuratu da huɗubar Ummansu wacce kullum take mata tilawar ba zai yuwu ta zauna yar uwarta ta nemo a ci da ita ba tunda itama tana da abin bayarwa idan ta zauna duk idan aurenta ya tashi kada tayi kuka da kowa ta kuka da kanta.
Tafiyar kuma ta canza salo sanda ta shiga Jami'a ta haɗu da gogaggun da suka fita ido a harkar, haka ta ringa zuba sharafinta cikin takatsantsan kuma Allah ya ara mata lokaci musamman da suka koma unguwar da babu wanda ya sansu suka fara sabuwar rayuwa.
Kullum ƙawayenta suna mata mitar basuga amfanin kuɗin da take samu ba domin dai kullum ka ganta tana nan kalar tausayi cikin tsumma ba sutura mai kyau mayukan gyaran fata da turaruka ma saboda ƙorafin mazan da take ta'ammali dasu ya saka ta fara siya saboda ta gyara jikinta duk a salon kada a fahimci halin da take ciki ya saka take takatsantsan da gudun mallakar duk wani abu da zai janyo hankalin mutane kanta, suna dai cin daɗi a cikinsu amma abubuwan more rayuwa dole ta haƙura da su saboda gujewa zargi sai dai tayi ta tara kuɗin idan sunyi yawa ta siyi wani abu kamar zobe ko fili ta ajiye.
A silar Nuratun asirinsu ya tonu har yan uwan mahaifinsu suka san halin da suke ciki dukda suna ji a jita jita wanda kuma da yawa Bilal da kowa ya san yana wahalta musu har gida ya siya musu shi mutane sukewa kallon abokin shashancin nata domin dai a rayuwar da muke ciki yanzu haka kawai wani bare ya ringa maka hidima kwatankwacin wacce yake musu tabbas abar dubawa ce dukda na Allah basa ƙarewa a duniya.
Ciki Nuratun tayi wanda baƙin cikin haka shine silar ajalin mahaifinsu. Ita bata kai wayewa da buɗewar idon Zulaihan ba kusan ma tursasawata sukayi ta shiga rayuwar da ba tata ba, bata ma san da tayi cikin ba har saida ya bayyana kansa fallasa kansa tukunna aka sha gurmi da dangin Babansu duk kuma yanda Umman da Zulaiha suka kaɗa suka raya tace ba zata zubar ba iya zunubin data kwasa harta same shi ya isheta ba zasu ɗora mata wani ba da Allah kuma ya nufa ba mai taka ƙasa bane tayi ɓari dukda da saka hannun su Zulaihan daga nan kuma ta tuba ita kanta Zulaihan daga lokacin ta rage abubuwa da yawa musamman kuma da Bilal ya fara taso da maganar aurensu ta shiga tsoron kar maganar ta koma masa a samu matsala dukda dai na Nuratu ne ya fito fili ita aka san bata ji amma ta san hakan zai iya shafarta shiyasa ta tattara hankalinta guri ɗaya ta saki harkar dama kuma tayi alƙawarin daga sanda aka saka musu rana zata bari to hakance ta kasance ta dena zuwa gurin kowa sai dai yan dabaru na waya data cigaba domin cigaba da samun kuɗin riƙe kai zuwa sanda zatayi auren.
Sai da ta cire Bedsheet ɗin da ɗaure shi a leda domin ba zata iya wankewa ba dama kuma amfaninsa kenan bata shimfiɗa wani ba ta shiga wanka a gurguje sai dai tana saɓa sabulu ta jiyo bugun ƙofa ta kasa kunne taji ko Bilal data leƙa falo ta ganshi a kwance zai tashi ya buɗe amma shiru shine ta zuciya ta fito da kumfa a jikinta zataje ta buɗe musu.
Wankan ta koma bayan sun gama iyashegensu suna tsokanarta wai amarya suka ringa dariyar da su suka san dalilinta sanin yana gidan kuma ya saka suka kama bakunansu dake cike da maganganu da son jin ya aka ƙare, abubuwan da suka kashe kuɗi tayi dan ta lulluɓe rayuwarta ta baya sun ci ko kuwa an samu akasi?
Wanka ta koma ta barsu suna haɗa TV da suka biya suka karɓo mata, Asmy ta ce bata karya ba gashi dan wulaƙanci bata ajiye musu sauran kaza ba kamar yanda ta ce sun cinye dan haka ta duba kitchen babu komai sai kayan shayi da burodi, ganin akwai ƙwai da mai babu albasa dai haka ta fitar da camping gas tsakar gidan suka ɗora ruwan tea bayan ya tafasa aka soua ƙwai dan ma Suby ta taho mata kayan spices garda garlic powder da yayarta ta bata gudummawa shi suka saka a ƙwan da suka fashe kusan rabin creat suka baje a falo suka karya tareda amarya bayan ta yi sallah ta fito.
Suna tsaka da jin labarin yanda akayi ya kirata, tayi tsaki bayan ta kashe wayar ta ce
"Banda rashin Imani ya raba dare yana sukuwa akaina yanzu gari ya waye ya ce wai in bashi abin kari maimakon shi ya dafa mun".
Sadiya ta ce
"Maganar gaskiya ba shiya kamata ki haɗawa abinci harda farfesu ma saboda ya mayar da jinin jikinsa dan abinda kika zuƙe ya fi ƙarfin ruwa ma" gaba ɗaya suka sheƙe da dariyar shaƙiyanci suna tafawa. A wani shegen tea flask iya ta da ta zuba masa ruwan zafin data taro a banɗaki ta haɗa da guntun bread ɗin da suka rage da sauran Milo dan sun shanye ledar Peak 500g daya siyo, a hannu ta riƙe kayan Suby na cewa ta ɗora a try mana tayi wucewarta.
BILAL
Kallon sama zuwa ƙasa yayi mata kafin ya tsayar da idonsa kan hannunta yana duban abinda ta ruƙo harta dungurar dasu a gabansa tana cika tana batsewa ko me ta tuna kuma sai ta saki fuska kaɗan ta zauna a gefensa ta shiga gaishe shi tana ƙoƙarin shiga jikinsa cike da kissa. Janyeta yayi ya miƙe zaune daƙyar dan kwanciyar da yayi zazzaɓi ya rufe shi, ya dafw kansa dake bugawa yana kallon kayan dake gabansa kafin ya ce
"Menene wannan?"
"Breakfast mana" ta faɗa tana sake matsawa kusa da shi dan ganinsa da tayi babu riga ya saka ta fara jin muradin kasancewa dashi dan abubuwan data sha jiya basu gama sakinta ba dukda taga alama shi nasa ya sake shi.
"Ni zanci wannan sauran biredin sai kace wani almajiri kuma ina madarar?" Ya faɗa, ta yamutsa fuska ta ce
"Ai dai kana kallo baƙi nayi ka godewa Allah ma daka samu sauran madara kuma sun shanye"ta ƙarasa tana harararsa. Da mamaki ya ce
"Ita madarar suka shanye duka?"
"Dan Allah ji yanda kake magana sai kace wanda suka shanye bugu ɗaya, su huɗu fa, ko ni kaɗai waccen yar madarar da ƙalau nake ai zama ɗaya zan shanyeta".
Kasa ce mata komai yayi ya tsaya kawai yana kallonta kafin ya sauke ajiyar zuciya ya koma ya kwanta saboda yanda zazzaɓin yake nuƙurƙusar jikinsa ya ce
"Ki soya mun ƙwai toh".
Haka ya ringa tura ƙwan daya ga kamar da gayya aka ƙone shi ga ga uban ƙarni daƙyar ya iya haɗa Milon a kofin robar data haɗo masa da shi. Safiyarsu ta farko da Halima ta shiga dawo masa, dukda yanda ta ke a wani yanayi na shiga sabuwar rayuwa haka ta ringa kai da kawowa bata nutsu ba saida ta cika masa dining da lafiyayyun breakfast bayan dankali da ƙwai nama kansu kusan kala uku ga sauran kazar amarci ga wanda aka taho mata da su daga gida komai cikin kwanuka na alfarma suna ci suna annashuwa amma yau shine aka bawa sauran biredi a gidansa da shayi a flask ɗin roba da kofin roba kuma babu yanda ya iya ya ci.
Baccin wahala ya sake komawa bayan ya sha paracetamol Zulaiha kuwa dama tunda ta dangwarar masa da ƙwan ta koma gurin ƙawayenta suka cigaba da sabgarsu.
HALIMA
Dole ta saka nake ƙarfafa jikina domin na yiwa kaina alƙawarin ƙaryata Bilal da yake cewa dole ya san zan neme shi. Ina son sa ba zan ƙaryata hakan ba amma kuma ni da kaina dana nutsu na fahimci cewar rabuwata da shi shine alkhairi a tare da ni.
Daga kalaman daya kalli idona ya faɗa mun na tabbatar dagaske yakeyi baya so na, albarkacin soyayyar da nakeyi masa ta saka ya aureni idan ma kuma yana so na ɗin tunda ya fahimci so na ya fi nasa yawa ya sakawa ransa zan zauna dashi komai wahala zan jure shine dalilin daya saka ya ringa azabtar dani a fili da baɗini har kuma da yake gargadar rasani bai yi nadamar hakan ba sai ma ƙara tabbatar mun da yakeyi ya sani ba zan iya rayuwa da waninsa ba.
Tsayin wata biyu da nayi tun barowata daga gidansa bai biyo ni ba ko a waya bai kirani ba sai yanzu haka wani nasa bai zo ba duk sai bayan da iyayena suka ɗauki matakin da suke ganin shi zai kawo mun maslaha a rayuwata.