Sashe 72
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tare muka shiga cikin falon ya dakatar da ni cikin ɗaga murya yace
"Daga yau na soke shigowar duk wata matar unguwar nan cikin gidan nan kema kuma na hana miki hulɗa da su tunda a gurin su kike koyon duk wani rashin mutunchin da kikeyi".
Nayi kasaƙe ina kallon sa kawai, wai nake koyon rashin mutunchi, ya cigaba da cewa
"Ita ga munafuka ta fito kai tsaye ta ce kina fita cefane za'a ce Mijinki baya kulawa dake shine take ta wani zagaye zagaye. Shi Mijin nasu da ya gina musu ƙaton gida ya basu motoci suke wani jin kansu waye bai san ɗan damfara bane ba? In sake ganin ta a gidan nan wlh sai na mata rashin mutunchi aikin banza kawai" fuuu ya fice.
Nayi murmushin takaici a fili na ce
"Ashe kasan mutane zasu ringa kallonka a matsayin wanda bai iya riƙe gidan nasa ba amma saboda rashin son gaskiya zaka ɓige da faɗan rashin dalili. Da ya dawo can falon sa ya ce na kai masa abinci na haɗa komai na kai masa bayan ya gama ya kira ni a waya ya ce na zo na kwashe kwanukan bayan na kwashe ya ce idan na kai su kitchen na je yana son magana da ni.
Kayan abinci ya nuna mun da ban san sanda ya shigo da su gidan ba, ya ce
"Gashi nan na siyo kafin ki cigaba da yi mun Gorin tunda na aureki abincin da kika zo da shi daga gidan ku kike ci". Ni dai na yi murmushi kawai yace na je na shirya na dawo yana jira na, na san me yake nufi.
Washe gari da safe sauran abincin dare na ɗumama muka karya da shi, mun tashi da walwala ba laifi saboda yanda daren jiyan ya kasance mana. Har ya gama shirin fita banga ya fito da kayan abincin ya kai su store ba dan haka na tuna masa, ina tsaye ya shiga kitchen ya fito da kwanuka na ringa kallon sa ina mamakin mai zaiyi ya wuce ya koma can ɗakin ba daɗewa ya ƙwala mun kira na je, ya nuna mun shinkafar daya auna cikin roba da ba zata wuce gwangwani uku ba sai mai da maggi, ya zaro ɗari biyar daga aljihun sa ya miƙa mun. Na ringa kallon kayan da kuɗin gaba ɗaya na rasa kalmar da zan yi amfani da ita gurin magana, shi kam ko a jikin sa ya ce
"Ki ɗauka zan rufe ƙofa sauri nake yi kada na makara". Haka na fito da kwanon shinkafa da mai da Maggi na guda biyar akai kamar wacce ta je roƙo maƙwafta. Na daɗe a zaune baƙin ƙofar falo na mamakin abun bai sake ni ba. Kenan awo Bilal zai ringa mun ko me? Ni bani da yancin da zan ɗibi abinci na dafa a cikin gida na sai iya abinda yaga dama ya ɗebo ya bani shi zanyi amfani da shi kenan?
Mai yake damun Bilal? Wai dama haka yake ko kuwa dai wani abun ne ya canza shi da ban sani ba?
Yini guda na kasa kataɓus duk in na kalli shinkafar sai na ji duniyar ta mun duhu wani abu ya tsaya mun a ƙahon zuci na ma kasa dafata balle na ci. Gashi na rasa wanda zan kira na samu sauƙin abinda nake ji a raina, wai wa zan ma zan iya gayawa wannan abun takaicin? Haka nan daga ƙarshe na ganin la'asar ta kawo kai na dafa masa da sauran cefanen da nake da shi amma ban iya ci ba cikin provision ɗin da na ɗan yi nayi ta dama Golden morn da cornflakes yini guda ina sha. Da yamma daya dawo ya taho da nama, kifi harda kayan miya. Haka ya zauna ya raba su ya ƙulla a ledoji ya zuba a frizeer tare da gaya mun tsahon lokacin da yake da yaƙinin zasu kai kafin su ƙare.
Tun daga sannan muka ɗoru akan sabon tsari, yawanci da safe zai siyo Lipton da sugar da buredi, wata rana in ya ga dama ya siyo madara da Milo ko ya siyo ƙwai. Su dankali, doya duk zai siyo ya ajiye sai dai irin ikon da yake gwadamun akan abinci ya saka lokuta da yawa nake haƙura da ko menene ya kawo sai dai na bar masa kayan sa ya ci.
Da rana kuma shi zai ɗiba mun iya abunda zan dafa cikina da nashi. Sau ɗaya na masa magana akan idan kuma muka yi baƙi fa? Yaya zanyi tunda kulle ɗakin yake yi? Bai bani amsa ba nima kuma ban sake tayar da zancen ba, sauƙin ta ban fiya yin baƙi daga ɓangare na ba, shima yan uwansan da suke zuwa a da yanzu duk sun ɗauke ƙafa Abubakar ne kaɗai zan ce har yanzu alaƙar mu take nan bai canza layi ba sai kuma Anty Amina ita kuma tsakanin mu gaisuwa a waya ne ko kuma idan mun haɗu a gidan Hajja.
A haka rayuwa ta buɗe sabon shafi, na yaye Al'amin na ɗauki cikin Sharifa. Tun ina ganin bazan iya jurewa ba har na haƙura na saba abin ma ya dena damuna musamman da hakan ya kasance silar dawowar nutsuwa da kuma walwala cikin zamantakewa ta da Bilal. Mun dena faɗa, soyayya da tattalin da nake kwaɗayin ina samun su da na zauna nayi tunani sai naga dama ita rayuwa bata taɓa zamowa mutum ɗari bisa ɗari yanda yake burin ta kasance masa.
Wasu matan sukan samu biyan buƙata na ababen more rayuwa amma kuma su rasa kula da farin ciki a gurin mazajen su. Wasu kuma su rasa wadata amma su samu farin cikin. Ni da na faɗa a tsaka tsaki domin dai ko da bana samun abinda na saba da shi ko nake so bai bar ni da yunwa ba. Sannan ina samun soyayya da tattalin da na tabbatar ba kowacce mace ke samun irin haka a gidan auren ta ba, amma duk da haka na sani Son da nake masa ne ya lulluɓe komai a ido na. Allah ya sani ina son Bilal son da ban san iyakar sa ba ba kuma na fatan ruyuwa babu shi dan nasan bazan iya ba.
Cikin kuɗin da nake dasu a hannu na da na account nake cira nayi duk abinda nake da buƙata wanda bai bani ba. Sau tari zuciya ta takan raya mun na siya abinda nake so na dafa na ci ni kaɗai idan baya nan amma sam na kasa yarda da hakan, ko gida na je na samo abu bazan iya ɓoye masa ba. Tunda kuma ya fahimci akwai kuɗi a hannu na ɗari biyar ɗin da ya fara bani a matsayin kuɗin cefane ma ya daina kwata kwata. A cewar sa babu abinda baya siyowa bai kuma taɓa tunanin abinda yake siyowar ko yake ɗibar mun baya isa ba. Zan dafa abinci da naman kaza ya ci har ya fini iko akai ba tare da ya tambaye ni a ina na samu kuɗin da na siyi kazar ba.
Bai taɓa gani na da wata sutura ko abin kwalliya wanda ba shi ya siya mun ba kuma ya tambaye ni a ina na samu, idan akwai abinda nake jin damuwa akai har ya jefa ni a tunani bai wuci yanda bai damu da komai ba har idan ba hurumin sa na shiga ba. Amma kuma daga ranar da ya faɗa mun wata magana, daga lokacin na fahimci kuskuren da mutane suke ta faɗin na yi akan auren Bilal, a ranar kuma na fara shakkun sahihancin ƙaunar da nake tunanin yana yi mun ya saka mun kokwanto akan aihinin manufar sa akan aure na.
Kuyi haƙuri, In sha Allahu daga yau har Friday zanyi post. Daga nan zamu tafi hutun azumi idan Allah ya saka mun kasance cikin waɗanda zasu gani.
[2/26, 11:11 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 30*
Watan Al'amin goma sha takwas na yaye shi a kuma watan na samu wani cikin wanda ko kusa Bilal bai yi maraba da samuwar sa ba.
"Wai dama bakiyi komai na tsarin Iyali ba? Ni na zata hankalin ki zai baki da kiyi ba sai an tuna miki ba, kina kallon yanda abubuwa duke tafiya kuma kawai zaki kama ki wani sake yin ciki. To ni dai gaskiya ban so haka ba" Abun da ya faɗa kenan lokacin da na shaida masa ina da cikin.
Gaba ɗaya sai na rasa yanda zan fassara maganganun sa. Fassara ta kai tsaye dai na san yana nufin baya son cikin kenan sai dai nayi ƙoƙarin kyautata masa zato da bashi damar gyara maganar sa ta hanyar cewa
"Yanzu mai kake nufi kenan?"
"Duk yanda kika ɗauka haka nake nufi ni dai na faɗa miki ban so kika sake samun wani ciki yanzu ba. Kina sane tun ba yanzu ba na gaya miki a tsari na gaba ɗaya bana so yayana su haura guda uku, yanzu ƙasa da shekara huɗu kina shirin yin yaya biyu" ya yi tsaki haɗi da tashi ya bar mun ɗakin.
Ko a mafarki ban taɓa zaton Bilal zai ƙyamaci abinda ya fito daga guri na ba. Na jinjinawa ƙarfin halin sa da har ya iya runtse ido ya ke faɗar abinda ni da shi mun san ƙarya ne Bilal da yake cewa idan munyi aure duk shekara zan ringa haihu muyi dariya na ce Akuya yake so na zama kenan amma wai yau shine zai dubi tsabar ido na ya ce mun baya son cikin da yake jiki na.
"Daga yau na soke shigowar duk wata matar unguwar nan cikin gidan nan kema kuma na hana miki hulɗa da su tunda a gurin su kike koyon duk wani rashin mutunchin da kikeyi".
Nayi kasaƙe ina kallon sa kawai, wai nake koyon rashin mutunchi, ya cigaba da cewa
"Ita ga munafuka ta fito kai tsaye ta ce kina fita cefane za'a ce Mijinki baya kulawa dake shine take ta wani zagaye zagaye. Shi Mijin nasu da ya gina musu ƙaton gida ya basu motoci suke wani jin kansu waye bai san ɗan damfara bane ba? In sake ganin ta a gidan nan wlh sai na mata rashin mutunchi aikin banza kawai" fuuu ya fice.
Nayi murmushin takaici a fili na ce
"Ashe kasan mutane zasu ringa kallonka a matsayin wanda bai iya riƙe gidan nasa ba amma saboda rashin son gaskiya zaka ɓige da faɗan rashin dalili. Da ya dawo can falon sa ya ce na kai masa abinci na haɗa komai na kai masa bayan ya gama ya kira ni a waya ya ce na zo na kwashe kwanukan bayan na kwashe ya ce idan na kai su kitchen na je yana son magana da ni.
Kayan abinci ya nuna mun da ban san sanda ya shigo da su gidan ba, ya ce
"Gashi nan na siyo kafin ki cigaba da yi mun Gorin tunda na aureki abincin da kika zo da shi daga gidan ku kike ci". Ni dai na yi murmushi kawai yace na je na shirya na dawo yana jira na, na san me yake nufi.
Washe gari da safe sauran abincin dare na ɗumama muka karya da shi, mun tashi da walwala ba laifi saboda yanda daren jiyan ya kasance mana. Har ya gama shirin fita banga ya fito da kayan abincin ya kai su store ba dan haka na tuna masa, ina tsaye ya shiga kitchen ya fito da kwanuka na ringa kallon sa ina mamakin mai zaiyi ya wuce ya koma can ɗakin ba daɗewa ya ƙwala mun kira na je, ya nuna mun shinkafar daya auna cikin roba da ba zata wuce gwangwani uku ba sai mai da maggi, ya zaro ɗari biyar daga aljihun sa ya miƙa mun. Na ringa kallon kayan da kuɗin gaba ɗaya na rasa kalmar da zan yi amfani da ita gurin magana, shi kam ko a jikin sa ya ce
"Ki ɗauka zan rufe ƙofa sauri nake yi kada na makara". Haka na fito da kwanon shinkafa da mai da Maggi na guda biyar akai kamar wacce ta je roƙo maƙwafta. Na daɗe a zaune baƙin ƙofar falo na mamakin abun bai sake ni ba. Kenan awo Bilal zai ringa mun ko me? Ni bani da yancin da zan ɗibi abinci na dafa a cikin gida na sai iya abinda yaga dama ya ɗebo ya bani shi zanyi amfani da shi kenan?
Mai yake damun Bilal? Wai dama haka yake ko kuwa dai wani abun ne ya canza shi da ban sani ba?
Yini guda na kasa kataɓus duk in na kalli shinkafar sai na ji duniyar ta mun duhu wani abu ya tsaya mun a ƙahon zuci na ma kasa dafata balle na ci. Gashi na rasa wanda zan kira na samu sauƙin abinda nake ji a raina, wai wa zan ma zan iya gayawa wannan abun takaicin? Haka nan daga ƙarshe na ganin la'asar ta kawo kai na dafa masa da sauran cefanen da nake da shi amma ban iya ci ba cikin provision ɗin da na ɗan yi nayi ta dama Golden morn da cornflakes yini guda ina sha. Da yamma daya dawo ya taho da nama, kifi harda kayan miya. Haka ya zauna ya raba su ya ƙulla a ledoji ya zuba a frizeer tare da gaya mun tsahon lokacin da yake da yaƙinin zasu kai kafin su ƙare.
Tun daga sannan muka ɗoru akan sabon tsari, yawanci da safe zai siyo Lipton da sugar da buredi, wata rana in ya ga dama ya siyo madara da Milo ko ya siyo ƙwai. Su dankali, doya duk zai siyo ya ajiye sai dai irin ikon da yake gwadamun akan abinci ya saka lokuta da yawa nake haƙura da ko menene ya kawo sai dai na bar masa kayan sa ya ci.
Da rana kuma shi zai ɗiba mun iya abunda zan dafa cikina da nashi. Sau ɗaya na masa magana akan idan kuma muka yi baƙi fa? Yaya zanyi tunda kulle ɗakin yake yi? Bai bani amsa ba nima kuma ban sake tayar da zancen ba, sauƙin ta ban fiya yin baƙi daga ɓangare na ba, shima yan uwansan da suke zuwa a da yanzu duk sun ɗauke ƙafa Abubakar ne kaɗai zan ce har yanzu alaƙar mu take nan bai canza layi ba sai kuma Anty Amina ita kuma tsakanin mu gaisuwa a waya ne ko kuma idan mun haɗu a gidan Hajja.
A haka rayuwa ta buɗe sabon shafi, na yaye Al'amin na ɗauki cikin Sharifa. Tun ina ganin bazan iya jurewa ba har na haƙura na saba abin ma ya dena damuna musamman da hakan ya kasance silar dawowar nutsuwa da kuma walwala cikin zamantakewa ta da Bilal. Mun dena faɗa, soyayya da tattalin da nake kwaɗayin ina samun su da na zauna nayi tunani sai naga dama ita rayuwa bata taɓa zamowa mutum ɗari bisa ɗari yanda yake burin ta kasance masa.
Wasu matan sukan samu biyan buƙata na ababen more rayuwa amma kuma su rasa kula da farin ciki a gurin mazajen su. Wasu kuma su rasa wadata amma su samu farin cikin. Ni da na faɗa a tsaka tsaki domin dai ko da bana samun abinda na saba da shi ko nake so bai bar ni da yunwa ba. Sannan ina samun soyayya da tattalin da na tabbatar ba kowacce mace ke samun irin haka a gidan auren ta ba, amma duk da haka na sani Son da nake masa ne ya lulluɓe komai a ido na. Allah ya sani ina son Bilal son da ban san iyakar sa ba ba kuma na fatan ruyuwa babu shi dan nasan bazan iya ba.
Cikin kuɗin da nake dasu a hannu na da na account nake cira nayi duk abinda nake da buƙata wanda bai bani ba. Sau tari zuciya ta takan raya mun na siya abinda nake so na dafa na ci ni kaɗai idan baya nan amma sam na kasa yarda da hakan, ko gida na je na samo abu bazan iya ɓoye masa ba. Tunda kuma ya fahimci akwai kuɗi a hannu na ɗari biyar ɗin da ya fara bani a matsayin kuɗin cefane ma ya daina kwata kwata. A cewar sa babu abinda baya siyowa bai kuma taɓa tunanin abinda yake siyowar ko yake ɗibar mun baya isa ba. Zan dafa abinci da naman kaza ya ci har ya fini iko akai ba tare da ya tambaye ni a ina na samu kuɗin da na siyi kazar ba.
Bai taɓa gani na da wata sutura ko abin kwalliya wanda ba shi ya siya mun ba kuma ya tambaye ni a ina na samu, idan akwai abinda nake jin damuwa akai har ya jefa ni a tunani bai wuci yanda bai damu da komai ba har idan ba hurumin sa na shiga ba. Amma kuma daga ranar da ya faɗa mun wata magana, daga lokacin na fahimci kuskuren da mutane suke ta faɗin na yi akan auren Bilal, a ranar kuma na fara shakkun sahihancin ƙaunar da nake tunanin yana yi mun ya saka mun kokwanto akan aihinin manufar sa akan aure na.
Kuyi haƙuri, In sha Allahu daga yau har Friday zanyi post. Daga nan zamu tafi hutun azumi idan Allah ya saka mun kasance cikin waɗanda zasu gani.
[2/26, 11:11 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 30*
Watan Al'amin goma sha takwas na yaye shi a kuma watan na samu wani cikin wanda ko kusa Bilal bai yi maraba da samuwar sa ba.
"Wai dama bakiyi komai na tsarin Iyali ba? Ni na zata hankalin ki zai baki da kiyi ba sai an tuna miki ba, kina kallon yanda abubuwa duke tafiya kuma kawai zaki kama ki wani sake yin ciki. To ni dai gaskiya ban so haka ba" Abun da ya faɗa kenan lokacin da na shaida masa ina da cikin.
Gaba ɗaya sai na rasa yanda zan fassara maganganun sa. Fassara ta kai tsaye dai na san yana nufin baya son cikin kenan sai dai nayi ƙoƙarin kyautata masa zato da bashi damar gyara maganar sa ta hanyar cewa
"Yanzu mai kake nufi kenan?"
"Duk yanda kika ɗauka haka nake nufi ni dai na faɗa miki ban so kika sake samun wani ciki yanzu ba. Kina sane tun ba yanzu ba na gaya miki a tsari na gaba ɗaya bana so yayana su haura guda uku, yanzu ƙasa da shekara huɗu kina shirin yin yaya biyu" ya yi tsaki haɗi da tashi ya bar mun ɗakin.
Ko a mafarki ban taɓa zaton Bilal zai ƙyamaci abinda ya fito daga guri na ba. Na jinjinawa ƙarfin halin sa da har ya iya runtse ido ya ke faɗar abinda ni da shi mun san ƙarya ne Bilal da yake cewa idan munyi aure duk shekara zan ringa haihu muyi dariya na ce Akuya yake so na zama kenan amma wai yau shine zai dubi tsabar ido na ya ce mun baya son cikin da yake jiki na.