Sashe 10
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata Juma'a sati biyu kenan da yin sa ranar mu watanni biyar da sati biyu kuma a cikin kwanakin da suka rage ma aurena da Bilal kamar ko yaushe munyi waya yace mun ze zo gurin ƙarfe biyu kuma se ya kirani yace na faɗawa Mama idan ya zo ɗin zamu ɗan je wata unguwa. Na ringa juya maganar, ba sabon abu bane fitar mu taren amma tun bayan da akayi sa ranar mu Mama ta zaunar dani tana mun faɗa da wasu maganganu in rage rawar kai karna kuskura ganin an saka mana rana da Bilal na ɗauki halin da bani dashi a da. Ko zuwa yayi yanzu se tace mu zauna a falonta muyi hira ko a compound a maimakon falon Abba da muka saba zama kamar kuma kaɗan take jira dani abu ƙarami zanyi ta fara mun faɗa shi yasa duk na rasa ta yanda zan ce mata zamu fita tare.
Ina tsaka da tunanin Amirah dake gidan Anty Labiba taje hutu tayi sallama, naji daɗin zuwan nata sosai, tare suke da Inaya da Amir wai Babansu Amir ɗin ne ya kawo su. Seda na fita na gaishe shi yana ta tsokanata wai amarya bayan ya tafi na cewa Mama zanje gidansu Hansa'u in karɓo atamfar ankon Baby an kawo mana tana can daga nan zamu kai ɗinki. Da Inayah muka tafi Amirah tace ba zata raka ni ba, seda nawa Bilal text na gaya masa ina gidansu Hansa'u cikin sa'a bata nan wai ta tafi wankin kai bayan tare mukayi zamuje shine bata kira ni ba. Zama nayi muka ɗan yi hira da Ummansu kafin muka tafi bayan da Bilal ya kirani akan yazo.
Page ɗaya ya rage free, ina fatan kin aika 800 ɗin ki kuɗin karatu 💃🏼💃🏼💃🏼
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk*
[12/14/2024, 12:03 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 5*
A motar Nasir na ganshi, ya kame a ciki yanda kasan tasa. A raina nace kuɗi dai ze yi wa Bilal kyau dan kalarsu aka masa. Yanayin surarsa da irin kayan da yake sakawa ba zaka kalli gidansu kace daga nan ya fito ba. Yana son gayu, sau tari na kan raya a raina nan yake kashe kuɗin sa gurin siyan sutura da takalma haɗi da agogo masu tsada duk abin da samari sa'anninsa suke yayi zaka ganshi dashi hakan kuma yana burge ni duk da ba wadata ce dashi ba amma ba yanda za'a yi ka ganshi ka raina shi.
A gaban motar nima na kame Inayah ta shiga baya muka tafi muna hirar mu gwanin sha'awa, ban tambaye shi in da zamu je ba shima be gaya mun ba har muka isa Goron dutse cikin GRA dake bayan matatar ruwa (WRECA). Na ringa kallon unguwar, a iya sani na banda kowa a gurin shima kuma bamu taɓa hirar wani nasu a nan ɗin ba, cikin wani da ke jere da gidaje hagu da dama muka shiga, gidaje uku ne ba kammalallu ba a ciki ɗaya ma kamar da mutane a ciki benen sama ne ba'a ƙarasa ba se fili da aka zagaye da alama ba'a fara gina shi ba. A ƙofar kangon dake ƙarshe layin ya tsaye dake layin baya ɓullewa, ya kashe motar muka fita na cigaba da kallon gurin ganin ya nufi kofar shiga gidan ya buɗe da muƙulli yasa muka bi bayansa se dai ban shiga ba na tsaya a waje ina kallon cikin gidan.
"Ya kuka tsaya a waje? Ku shigo mana" ya fada bayan daya juya ya ganmu a tsaye. Se da na ɗan yi jumm ina kallon cikin gidan kafin nayi bismillah na shiga. Tsakar gidan bashi da girma sosai amma ze iya cin mota ɗaya ko ma biyu. Duk da ginin ba'a kammala shi ba amma yana yin tsarin yayi kyau. Akwai babbar ƙofa dake tsakiya tana kallon get, se kuma daga gefe can akwai wata ƙofar ƙarama. Ya buɗe babbar kofar ya shiga muka bishi, a cikin falon da ba'a yiwa fulasta ba ya tsaya yana kallona yace
"Barka da zuwa gidan Bilal". Se na saki murmushi, wato nan ne gidan da yake gina mana. Ya nuna bangon hagu in da ƙofa take yace
"Bedrooms ne guda biyu kowanne da toilet, suna da girma nasan zasu ci kowanne irin saitin gado". Seya matsa ya buɗe kofar dake bangon gabas yana cewa
"Nan kuma kitchen ne da store", waccen ƙofar ta waje kuma ɗaki ne da falo a ciki Master room kenan ina tunanin ko a faso da ƙofa ta nan" ya nuna mun ɗan corridor dake gefe yace
"Saboda sauƙaƙa miki zirga zirga tsakanin nan da can ko dan yanayi na ruwa da sanyi". Ni dai murmushi kawai nake kamar wata sokuwa. Ya buɗe ɗakunan muka leƙa har cikin toilets ɗin kamar yan da ya faɗa suna da girma sosai kam zasu ɗauki kaya har a samu gurin shimfiɗa carpet me ɗan girma. Har can part ɗin da yace nasa se da muka shiga, a nan naga ya aje buhunhunan sumunti da sauran kwanon da akayi rufi dukda saman gota ce se kayan toilet da sink na kitchen.Tsakar gida muka koma ya nuna mun ɗan filin dake kusa da part ɗin yace
"Da nan gurin Hajja tace se ayi ɗaki tun da ga banɗaki a tsakar gida dama ko da zamuyi baƙi maza masu kwana"
"Uhm" kawai na ce a raina ina lissafa ɗan abinda nake ganin ya rage a aikin ginin. Fulastar ciki ce dan an yi ta waje da ɗakuna guda biyu nawa, falo ne da kitchen suka rage se can ɓangaren sa.
"Yau kin ga gidanki" ya faɗa bayan da muka zauna a mota. Nayi murmushi nace "guri yayi kyau sosai Allah ya sa rai aka yi wa"
"Amin My Halims ai se ma an gama aiki an gwagwaje gurin da kaya yan kamfani kyansa ze sake fitowa" ya bani amsa na amsa masa da
"Haka ne, to Allah ya nuna mana lokaci". Shirun minti biyar ya gifta tsakaninmu ya ci gaba da tuƙi ni kuma na tsunduma tunanin abinda ya rage a aikin gidan yanzu wanda a gani na saura ne kawai tun da an yi me wuyar kammala ginin da rufi. Ni duk da yake ta zancen gini na zata irin ko linta be kai ba ashe ma ƙarashe ne kawai.
"Yanzu kin ga abin da nake gaya miki na akwai sauran shiri a gaba na ko?" Ya katse mun shirun, se na kalle shi. Ya ci gaba da cewa
"Ban siyi ko kwali ɗaya na Tiles ba. Ga gilasan winduna kin ga boggler kawai aka saka. Ban da ƙarashen fulasta sannan azo uwa uba wiring ɗin wuta da ruwa ga fenti dasu pop aikin fa ba ƙarami bane Halima".
Nayi kasaƙe ina sauraronsa, se da ya kai aya kafin nace
"Allahn daya hore akayi wannan ze rufa asiri in sha Allah"
"Haka ne" ya bani amsa daga nan be sake cewa komai ba har muka je unguwar mu. A hanya muka sauka ya wuce ina ɗaga masa hannu, se da na sake komawa gidansu Hansa'u cikin sa'a na tarar ta dawo nan muka zauna na shiga labarta mata yanda gida na yake.
"Lallai Halima ba kunya kika bishi ganin gida ko?" Ta faɗa se na harare ta nace
"Ji banza wai kunya. Kawai naje naga gidan ne wani abu da zan ji kunya lallai ma". Seda Mama ta kira ni kafin muka fito ta rakani rabin hanya. Sau biyu cikin zirgilli na ina kusan gaya wa Mama zancen munje ganin gidan se Allah ya cece ni na canza maganar da wata. Abin na mintsili na, nayi kamar na gayawa Anty Labiba se dai nasan yanda take a cike dani tsaf zata haɗa ni da Mama se kawai na kama kaina na bar murna ta a ciki na. Bilal dai da ake ganin be kai ba gashi nan cikin hukuncin ubangiji ze yi abinda kowa se yayi mamaki ga dai gida nan na nunawa sa'a da nasan iya kar masu ƙaryar kuɗin dai suyi kamar shi ko wanda be kai shi ba kuma a unguwar yan gayu da na tabbatar ƙasa tana tsada a gurin.
Shi ma a yanda yace filin na gadon sa ne ya adana gashi kuwa ya masa rana babu yanda masu gidajen kusa dashi da ma na nesa basuyi akan ya bar musu ba har musanyan ginannen gida aka bashi da cikon kuɗi duk yaƙi a cewar sa baze maida kamar sa ba kuma unguwar ta masa da irin tsarin rayuwar da yake so ya gudanar da iyalansa.
Watanni uku suka shuɗe cikin wata shida na ranar auren mu data rage har sannan kuma daga ɓangare biyu nawa dana Bilal ba zan ce ga wani shiri da aka fara na biki ba. A gidanmu dai nasan Abba ya yiwa Mama magana akan abin da ya kamata ayi tace masa suna kan lissafi ne idan ta gama haɗa komai zata sanar masa ban sake jin sun tada maganar ba. Ina da abubuwan da nake so a mun daga kan zaɓin kayan ɗaki zuwa sauran kayan amfani se dai ban ga fuskar da zan sakowa Mama maganar ba. Anty Labiba ko yanzu ban ma isa na doshe ta da wannan zancen ba tun da ƙiris take jira dama ta samu nayi mun. A haka a ka fara azumi, na ƙudurce a raina har aka sallace ban ga an motsa ba to fa zanyi magana se dai ace nayi rashin kunya.
Ina tsaka da tunanin Amirah dake gidan Anty Labiba taje hutu tayi sallama, naji daɗin zuwan nata sosai, tare suke da Inaya da Amir wai Babansu Amir ɗin ne ya kawo su. Seda na fita na gaishe shi yana ta tsokanata wai amarya bayan ya tafi na cewa Mama zanje gidansu Hansa'u in karɓo atamfar ankon Baby an kawo mana tana can daga nan zamu kai ɗinki. Da Inayah muka tafi Amirah tace ba zata raka ni ba, seda nawa Bilal text na gaya masa ina gidansu Hansa'u cikin sa'a bata nan wai ta tafi wankin kai bayan tare mukayi zamuje shine bata kira ni ba. Zama nayi muka ɗan yi hira da Ummansu kafin muka tafi bayan da Bilal ya kirani akan yazo.
Page ɗaya ya rage free, ina fatan kin aika 800 ɗin ki kuɗin karatu 💃🏼💃🏼💃🏼
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk*
[12/14/2024, 12:03 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 5*
A motar Nasir na ganshi, ya kame a ciki yanda kasan tasa. A raina nace kuɗi dai ze yi wa Bilal kyau dan kalarsu aka masa. Yanayin surarsa da irin kayan da yake sakawa ba zaka kalli gidansu kace daga nan ya fito ba. Yana son gayu, sau tari na kan raya a raina nan yake kashe kuɗin sa gurin siyan sutura da takalma haɗi da agogo masu tsada duk abin da samari sa'anninsa suke yayi zaka ganshi dashi hakan kuma yana burge ni duk da ba wadata ce dashi ba amma ba yanda za'a yi ka ganshi ka raina shi.
A gaban motar nima na kame Inayah ta shiga baya muka tafi muna hirar mu gwanin sha'awa, ban tambaye shi in da zamu je ba shima be gaya mun ba har muka isa Goron dutse cikin GRA dake bayan matatar ruwa (WRECA). Na ringa kallon unguwar, a iya sani na banda kowa a gurin shima kuma bamu taɓa hirar wani nasu a nan ɗin ba, cikin wani da ke jere da gidaje hagu da dama muka shiga, gidaje uku ne ba kammalallu ba a ciki ɗaya ma kamar da mutane a ciki benen sama ne ba'a ƙarasa ba se fili da aka zagaye da alama ba'a fara gina shi ba. A ƙofar kangon dake ƙarshe layin ya tsaye dake layin baya ɓullewa, ya kashe motar muka fita na cigaba da kallon gurin ganin ya nufi kofar shiga gidan ya buɗe da muƙulli yasa muka bi bayansa se dai ban shiga ba na tsaya a waje ina kallon cikin gidan.
"Ya kuka tsaya a waje? Ku shigo mana" ya fada bayan daya juya ya ganmu a tsaye. Se da na ɗan yi jumm ina kallon cikin gidan kafin nayi bismillah na shiga. Tsakar gidan bashi da girma sosai amma ze iya cin mota ɗaya ko ma biyu. Duk da ginin ba'a kammala shi ba amma yana yin tsarin yayi kyau. Akwai babbar ƙofa dake tsakiya tana kallon get, se kuma daga gefe can akwai wata ƙofar ƙarama. Ya buɗe babbar kofar ya shiga muka bishi, a cikin falon da ba'a yiwa fulasta ba ya tsaya yana kallona yace
"Barka da zuwa gidan Bilal". Se na saki murmushi, wato nan ne gidan da yake gina mana. Ya nuna bangon hagu in da ƙofa take yace
"Bedrooms ne guda biyu kowanne da toilet, suna da girma nasan zasu ci kowanne irin saitin gado". Seya matsa ya buɗe kofar dake bangon gabas yana cewa
"Nan kuma kitchen ne da store", waccen ƙofar ta waje kuma ɗaki ne da falo a ciki Master room kenan ina tunanin ko a faso da ƙofa ta nan" ya nuna mun ɗan corridor dake gefe yace
"Saboda sauƙaƙa miki zirga zirga tsakanin nan da can ko dan yanayi na ruwa da sanyi". Ni dai murmushi kawai nake kamar wata sokuwa. Ya buɗe ɗakunan muka leƙa har cikin toilets ɗin kamar yan da ya faɗa suna da girma sosai kam zasu ɗauki kaya har a samu gurin shimfiɗa carpet me ɗan girma. Har can part ɗin da yace nasa se da muka shiga, a nan naga ya aje buhunhunan sumunti da sauran kwanon da akayi rufi dukda saman gota ce se kayan toilet da sink na kitchen.Tsakar gida muka koma ya nuna mun ɗan filin dake kusa da part ɗin yace
"Da nan gurin Hajja tace se ayi ɗaki tun da ga banɗaki a tsakar gida dama ko da zamuyi baƙi maza masu kwana"
"Uhm" kawai na ce a raina ina lissafa ɗan abinda nake ganin ya rage a aikin ginin. Fulastar ciki ce dan an yi ta waje da ɗakuna guda biyu nawa, falo ne da kitchen suka rage se can ɓangaren sa.
"Yau kin ga gidanki" ya faɗa bayan da muka zauna a mota. Nayi murmushi nace "guri yayi kyau sosai Allah ya sa rai aka yi wa"
"Amin My Halims ai se ma an gama aiki an gwagwaje gurin da kaya yan kamfani kyansa ze sake fitowa" ya bani amsa na amsa masa da
"Haka ne, to Allah ya nuna mana lokaci". Shirun minti biyar ya gifta tsakaninmu ya ci gaba da tuƙi ni kuma na tsunduma tunanin abinda ya rage a aikin gidan yanzu wanda a gani na saura ne kawai tun da an yi me wuyar kammala ginin da rufi. Ni duk da yake ta zancen gini na zata irin ko linta be kai ba ashe ma ƙarashe ne kawai.
"Yanzu kin ga abin da nake gaya miki na akwai sauran shiri a gaba na ko?" Ya katse mun shirun, se na kalle shi. Ya ci gaba da cewa
"Ban siyi ko kwali ɗaya na Tiles ba. Ga gilasan winduna kin ga boggler kawai aka saka. Ban da ƙarashen fulasta sannan azo uwa uba wiring ɗin wuta da ruwa ga fenti dasu pop aikin fa ba ƙarami bane Halima".
Nayi kasaƙe ina sauraronsa, se da ya kai aya kafin nace
"Allahn daya hore akayi wannan ze rufa asiri in sha Allah"
"Haka ne" ya bani amsa daga nan be sake cewa komai ba har muka je unguwar mu. A hanya muka sauka ya wuce ina ɗaga masa hannu, se da na sake komawa gidansu Hansa'u cikin sa'a na tarar ta dawo nan muka zauna na shiga labarta mata yanda gida na yake.
"Lallai Halima ba kunya kika bishi ganin gida ko?" Ta faɗa se na harare ta nace
"Ji banza wai kunya. Kawai naje naga gidan ne wani abu da zan ji kunya lallai ma". Seda Mama ta kira ni kafin muka fito ta rakani rabin hanya. Sau biyu cikin zirgilli na ina kusan gaya wa Mama zancen munje ganin gidan se Allah ya cece ni na canza maganar da wata. Abin na mintsili na, nayi kamar na gayawa Anty Labiba se dai nasan yanda take a cike dani tsaf zata haɗa ni da Mama se kawai na kama kaina na bar murna ta a ciki na. Bilal dai da ake ganin be kai ba gashi nan cikin hukuncin ubangiji ze yi abinda kowa se yayi mamaki ga dai gida nan na nunawa sa'a da nasan iya kar masu ƙaryar kuɗin dai suyi kamar shi ko wanda be kai shi ba kuma a unguwar yan gayu da na tabbatar ƙasa tana tsada a gurin.
Shi ma a yanda yace filin na gadon sa ne ya adana gashi kuwa ya masa rana babu yanda masu gidajen kusa dashi da ma na nesa basuyi akan ya bar musu ba har musanyan ginannen gida aka bashi da cikon kuɗi duk yaƙi a cewar sa baze maida kamar sa ba kuma unguwar ta masa da irin tsarin rayuwar da yake so ya gudanar da iyalansa.
Watanni uku suka shuɗe cikin wata shida na ranar auren mu data rage har sannan kuma daga ɓangare biyu nawa dana Bilal ba zan ce ga wani shiri da aka fara na biki ba. A gidanmu dai nasan Abba ya yiwa Mama magana akan abin da ya kamata ayi tace masa suna kan lissafi ne idan ta gama haɗa komai zata sanar masa ban sake jin sun tada maganar ba. Ina da abubuwan da nake so a mun daga kan zaɓin kayan ɗaki zuwa sauran kayan amfani se dai ban ga fuskar da zan sakowa Mama maganar ba. Anty Labiba ko yanzu ban ma isa na doshe ta da wannan zancen ba tun da ƙiris take jira dama ta samu nayi mun. A haka a ka fara azumi, na ƙudurce a raina har aka sallace ban ga an motsa ba to fa zanyi magana se dai ace nayi rashin kunya.