Sashe 66
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To yanzu zaki iya zama a nan gidan idan ya so a samo miki wata a Galadanci ku zauna tare ko kuma can gidan Antyn ki zaki tafi?"
Yanda Mama ta kalle shi sai na ga kamar ba haka suka tsara ba da alama ya sauka daga layin maganar da suka ƙulla kafin shigowa ta. Da sauri na ce
"Eh Abba, ko Baba Salamatu ma ko Innar su Salaha tun da babu abin da suke yi kuma ga Zainab sai mu yi zaman mu".
"Daga haka ta koma gidan ta mana sai su je can su taya ta zaman menene amfanin zaman ta a nan bama nan?" Mama ta faɗa, na marairaice fuska ina jira na ji Abban ya ce Aa sai ji na yi ya ce
"Hakan ma babu laifi ai, sai ki kira Yaya Salamatun kiji idan zata yarda taje can gidan nata, na san halin ta dai zata ce gidan siriki ba zata zauna ba shi yasa na ce ta zo nan ɗin su zauna"
"Ni fa kulle gida na zanyi na gaya maka Zainab ma garin su zata tafi dama akwai bikin yayan ta da za'a yi wani satin, Yaya Salamatu kuwa ba za'a ɗora mata hidimar Halima tana fama da kanta ba, iya kukan ɗan ta kai kanka raba dare kayi jiya kana zarya balle ita da ba cikakkiyar lafiya ba. Gara ta koma can gidan ta ta gaya masa ya samo mata wata cikin dangin sa su zauna kafin ya dawo tun da ai sati ɗaya ta ce zai yi ba wai daɗewa zai yi a can ba" Mama ta sake faɗa sai Abba ya ce
"Gara da kika tuna mun, Halimatu maza ki shirya ki tashi Ibrahim ya kaiku asibiti, bari na kira Dr Lawal kafin ku isa kukan da yaron nan ya ke yi bai yi kama da na lafiya ba".
"Mantawa dai kayi, ita sanda aka haife ta ba haka ta ringa kukan ba sai da muka kusan yada wanka kafin ta daina shima na lokaci ne zai dai na" Mama ta faɗa. Bai saurareta ba ya zaro wayar sa yana cewa
"Duk kukan da ta ke yi jikin ta baya ɗaukar zafi irin yanda na sa ya yi kuma har ƙaƙƙafewa idanuwan sa na ga suna yi kamar wanda zai suma". Sum sum na fice ina jin wani iri a zuciya ta. Daren jiya hatta da Mu'azzam da ke bacci kamar gawa Al'amin na fara kuka ya farka haka suka ringa karɓa karɓa dan cewa Mama ta yi na kwanta amma na kasa yin baccin. Na tuna yanda shi Bilal ko a jikin sa amma su duk hankalin su ya tashi ba su samu nutsuwa ba sai da ya samu bacci dagaske dai ita soyayyar jini ba ta da mahaɗi.
Haka muka tafi asibitin a raina ina tunanin yanzu Mama zata yarda na zauna a gidan ko kuwa dai korata za ta yi?
Dr da muka gani ya gama jagwalgwala shi ya ce lafiyar sa ƙalau babu wani abu da yake damun sa ciki da kunne da cibiya da kai da duk sauran guraren da zasu iya masa ciwo ya duba amma bai ga komai ba. Har ƙafafun sa da hannaye da su baya ya duba wai ko da a garin ɗauka an gurɗe masa wani guri still dai komi lafiya. Paracetamol ya rubuta mana kawai ya ce a ringa bashi sau biyu safe da dare ko gajiya ce ta ke saka shi koke koken.
Muna hanyar komawa gida Suhaila matar Hafiz ta kira ni wai su na ta bugun ƙofa ko bacci na ke yi na sanar mata ina gidan mu ai, address ta ce na tura mata, bayan na tura ta sake kira na akan na yi mata sharing location kawai zai fi sauƙi basu gane kwatancen a rubuce ba. Da ke muna dab da gida ina shiga na hau WhatsApp na tura mata sannan na shiga kitchen bayan na gayawa Mama zuwan na su. Frozen snacks da Mama bata rabo da su na fitar da samosa na ce Zainab ta soya musu, sai dubulan da dambun nama. Na zuba dambun shinkafar da ta gama na abincin rana da peppered chicken a warmers masu kyau duk da bana zaton za su ci amma dai na aje mata komai yanda kawowa kawai za tayi idan sun zo.
Ba'a ɗauki lokaci mai tsayi ba kuwa suka ƙaraso, babyn ta ya girma masha Allah jikin nan luhu luhu kamar an hura masa iska, tare suka shigo da Hafiz ɗin suka gaisa da Mama ya wuce akan zai je ya dawo ita kuma ya barta. Kusan awan ta uku sai bayan la'asar kafin ya dawo suka tafi bayan sun sauke mana tulin kayan tsaraba manyan ledoji guda uku cike da designers kayan jarirai da ko ba'a faɗa ba kana gani kasan ba ƙananun kuɗi suka lashe ba ga kuma atamfofi super wax turmi biyu da wani arnen lace da ta ce sirikarta ce ta bayar a kawo mun.
Haka Mama ta cika mata bokiti da dubulan da dambun naman da ta ce sun yi mata daɗi, dambun ma tafiya ta yi da shi kamar yanda ta ce Hafiz na son Dambu ita kuma bata iya ba. Bayan tafiyar su Mama ta tsare ni da tambayar ina na samo su? Na ce mata abokin Bilal ne ɗan gurin aikin su.
"Ikon Allah, abokin ma na gurin aiki ne amma ya yi masa wannan hidimar?" Ta faɗa. Na taɓe baki na ce
"Kuma basu wani daɗe tare ba, bayan auren mu aka kawo Hafiz ɗin ma kawai dai Allah ne ya haɗa jinin su, shima sanda ta haihu baki ga kayan da ya siya musu da zamu je barka ba. Da babbar sallama fa Hafiz ɗin har rago ya bashi da ke an ce Baban sa mai kuɗi ne sosai nasan Abba ma zai iya sanin sa dan shima tsohon ɗan kwangila ne" na bata amsa. Ta yi jum kafin ta ce
"Ku dai kiyaye, duk dai a yanyin su babu kalar rashin gaskiya ko makamancin haka amma dai ku kama kanku ku kuma guji abin hannun su ko dan saboda mutunchin ku"
"Shi dai, ni ina ruwa na da su? Ita ce ma take nacin sai mun yi mu'amala amma ni wlh idan ma ba ta kira ni a waya ba mantawa nake yi da ita shine dai bini bini ya ke zuwa gidan su" na faɗa ina taɓe baki, Mu'azzam da ya shigo ya ce
"Dama ai dole ya bi su tun da suna da kuɗi. Shi fa mijin nan na ki kwaɗayayye ne kawai, idan kika duba circle ɗin abokanan sa kaf sun fi shi wadata, kowa a unguwar su ma ya sani an masa tambari baya abota da talaka, idan kuwa kika ganshi da wanda ya fi rufin asiri to wlh aboki ne irin tun na ƙuruciya da ba yanda ya iya da shi irin su Nura Tela, su ɗin ma da ta in da yake morar su shi ya sa yake tare da su".
"Kai kuma na hanaka magana akan yaron nan in dai ba alkhairin za zaka faɗa ba amma ka ƙi ji ko Mu'azzam? Ai shikenan" Mama ta faɗa.
Ya wuce yana cewa
"Ni fa gaskiya na ke faɗi ba wani abu ba ko tun da na ke na taɓa yi masa sharri? Duk abin da zan faɗa halin sa ne idan kuma ƙarya aka masa ai ga ta nan ta faɗo abokanan sa guda biyu da suke ƙasa da shi".
Ni dai shiru na yi kawai ina bin sa da kallo can ƙasan raina kuma ina ƙoƙarin lissafo abokanan Bilal ɗin da ya ce wanda suke ƙasa da shi a wadata amma na gaza samo ko guda ɗaya a waɗanda na sani.
Abokanan sa da na yiwa farin sani mutum huɗu ne. Nasir chemist ɗin sa uku kuma na cikin unguwar mu ma shi ne ƙarami a cikin su banda gidan gona da ya ke da shi yana siyar da kaji da ƙwai sai Abduljabbar su maƙwaftan mu ne a da kafin suka koma Abuja da zama yanzu haka a CBN yake aiki, sai Nura Tela shi ma kuma ni dai ba zan saka shi a layin marasa wadata ba domin a shaidar gani da ido ma a guri na ya fi Bilal tun da matar sa ko makaho ya shafa jikin ta ya san tana cikin jin daɗi, gi da ne kawai za'a ce na Bilal ya fi na sa kyau da tsari baya ga haka banga ta in da ya fishi ba sai kuma Aliko, shi kam ko a kantin Kwari ma oga ne. Su ne kusan abokanan sa da duk wanda ya san shi ya san su, sauran ma kuma duk daga na gurin aikin har na gari kowa da sabgogin sa, gaskiyar Mu'azzam Billa ba shi da abokanai talakawa. Amma kuma wannan ba hujja ba ce da za'a ce masa kwaɗayayye ko mai son zuciya.
Sai da Anty Labiba ta zo ta ringa fitar da kayan tana faɗar kuɗin su jiki na ya sake sanyi da lamarin Hafiz, a wata akwati ta zuba kayan dan rigunan duk manya ne ƙananan ciki ba su da yawa ta haɗe su da sauran na barkar mu data ware ta ɓoye bayan ta gama ta ce
"Na san a ranki zagi na kike kina cewa na tattare muku kaya na ɓoye ko? Duk idan lokacin amfanin su ya kai da kaina zan fito da su na kawo miki dan wlh ba za'a tattara kaya ki kaisu gidan na san ki sarai yanda kika ringa kwasar suturun ki kina rabawa ƙannen sa suma haka zaki kwashe ki basu tun da ba sanin zafin su kika yi ba. Ranar suna ina kallon Lace ɗin da figaggiyar ƙanwar nan ta sa ta saka ko kin zata ban gane shi ba? Tun ranar ɗaurin auren ki bana jin kin sake sakawa shine kika bata, zanin da ta yi goyo da shi ma na super da aka kai ki da ita a jikin ki ne".
Yanda Mama ta kalle shi sai na ga kamar ba haka suka tsara ba da alama ya sauka daga layin maganar da suka ƙulla kafin shigowa ta. Da sauri na ce
"Eh Abba, ko Baba Salamatu ma ko Innar su Salaha tun da babu abin da suke yi kuma ga Zainab sai mu yi zaman mu".
"Daga haka ta koma gidan ta mana sai su je can su taya ta zaman menene amfanin zaman ta a nan bama nan?" Mama ta faɗa, na marairaice fuska ina jira na ji Abban ya ce Aa sai ji na yi ya ce
"Hakan ma babu laifi ai, sai ki kira Yaya Salamatun kiji idan zata yarda taje can gidan nata, na san halin ta dai zata ce gidan siriki ba zata zauna ba shi yasa na ce ta zo nan ɗin su zauna"
"Ni fa kulle gida na zanyi na gaya maka Zainab ma garin su zata tafi dama akwai bikin yayan ta da za'a yi wani satin, Yaya Salamatu kuwa ba za'a ɗora mata hidimar Halima tana fama da kanta ba, iya kukan ɗan ta kai kanka raba dare kayi jiya kana zarya balle ita da ba cikakkiyar lafiya ba. Gara ta koma can gidan ta ta gaya masa ya samo mata wata cikin dangin sa su zauna kafin ya dawo tun da ai sati ɗaya ta ce zai yi ba wai daɗewa zai yi a can ba" Mama ta sake faɗa sai Abba ya ce
"Gara da kika tuna mun, Halimatu maza ki shirya ki tashi Ibrahim ya kaiku asibiti, bari na kira Dr Lawal kafin ku isa kukan da yaron nan ya ke yi bai yi kama da na lafiya ba".
"Mantawa dai kayi, ita sanda aka haife ta ba haka ta ringa kukan ba sai da muka kusan yada wanka kafin ta daina shima na lokaci ne zai dai na" Mama ta faɗa. Bai saurareta ba ya zaro wayar sa yana cewa
"Duk kukan da ta ke yi jikin ta baya ɗaukar zafi irin yanda na sa ya yi kuma har ƙaƙƙafewa idanuwan sa na ga suna yi kamar wanda zai suma". Sum sum na fice ina jin wani iri a zuciya ta. Daren jiya hatta da Mu'azzam da ke bacci kamar gawa Al'amin na fara kuka ya farka haka suka ringa karɓa karɓa dan cewa Mama ta yi na kwanta amma na kasa yin baccin. Na tuna yanda shi Bilal ko a jikin sa amma su duk hankalin su ya tashi ba su samu nutsuwa ba sai da ya samu bacci dagaske dai ita soyayyar jini ba ta da mahaɗi.
Haka muka tafi asibitin a raina ina tunanin yanzu Mama zata yarda na zauna a gidan ko kuwa dai korata za ta yi?
Dr da muka gani ya gama jagwalgwala shi ya ce lafiyar sa ƙalau babu wani abu da yake damun sa ciki da kunne da cibiya da kai da duk sauran guraren da zasu iya masa ciwo ya duba amma bai ga komai ba. Har ƙafafun sa da hannaye da su baya ya duba wai ko da a garin ɗauka an gurɗe masa wani guri still dai komi lafiya. Paracetamol ya rubuta mana kawai ya ce a ringa bashi sau biyu safe da dare ko gajiya ce ta ke saka shi koke koken.
Muna hanyar komawa gida Suhaila matar Hafiz ta kira ni wai su na ta bugun ƙofa ko bacci na ke yi na sanar mata ina gidan mu ai, address ta ce na tura mata, bayan na tura ta sake kira na akan na yi mata sharing location kawai zai fi sauƙi basu gane kwatancen a rubuce ba. Da ke muna dab da gida ina shiga na hau WhatsApp na tura mata sannan na shiga kitchen bayan na gayawa Mama zuwan na su. Frozen snacks da Mama bata rabo da su na fitar da samosa na ce Zainab ta soya musu, sai dubulan da dambun nama. Na zuba dambun shinkafar da ta gama na abincin rana da peppered chicken a warmers masu kyau duk da bana zaton za su ci amma dai na aje mata komai yanda kawowa kawai za tayi idan sun zo.
Ba'a ɗauki lokaci mai tsayi ba kuwa suka ƙaraso, babyn ta ya girma masha Allah jikin nan luhu luhu kamar an hura masa iska, tare suka shigo da Hafiz ɗin suka gaisa da Mama ya wuce akan zai je ya dawo ita kuma ya barta. Kusan awan ta uku sai bayan la'asar kafin ya dawo suka tafi bayan sun sauke mana tulin kayan tsaraba manyan ledoji guda uku cike da designers kayan jarirai da ko ba'a faɗa ba kana gani kasan ba ƙananun kuɗi suka lashe ba ga kuma atamfofi super wax turmi biyu da wani arnen lace da ta ce sirikarta ce ta bayar a kawo mun.
Haka Mama ta cika mata bokiti da dubulan da dambun naman da ta ce sun yi mata daɗi, dambun ma tafiya ta yi da shi kamar yanda ta ce Hafiz na son Dambu ita kuma bata iya ba. Bayan tafiyar su Mama ta tsare ni da tambayar ina na samo su? Na ce mata abokin Bilal ne ɗan gurin aikin su.
"Ikon Allah, abokin ma na gurin aiki ne amma ya yi masa wannan hidimar?" Ta faɗa. Na taɓe baki na ce
"Kuma basu wani daɗe tare ba, bayan auren mu aka kawo Hafiz ɗin ma kawai dai Allah ne ya haɗa jinin su, shima sanda ta haihu baki ga kayan da ya siya musu da zamu je barka ba. Da babbar sallama fa Hafiz ɗin har rago ya bashi da ke an ce Baban sa mai kuɗi ne sosai nasan Abba ma zai iya sanin sa dan shima tsohon ɗan kwangila ne" na bata amsa. Ta yi jum kafin ta ce
"Ku dai kiyaye, duk dai a yanyin su babu kalar rashin gaskiya ko makamancin haka amma dai ku kama kanku ku kuma guji abin hannun su ko dan saboda mutunchin ku"
"Shi dai, ni ina ruwa na da su? Ita ce ma take nacin sai mun yi mu'amala amma ni wlh idan ma ba ta kira ni a waya ba mantawa nake yi da ita shine dai bini bini ya ke zuwa gidan su" na faɗa ina taɓe baki, Mu'azzam da ya shigo ya ce
"Dama ai dole ya bi su tun da suna da kuɗi. Shi fa mijin nan na ki kwaɗayayye ne kawai, idan kika duba circle ɗin abokanan sa kaf sun fi shi wadata, kowa a unguwar su ma ya sani an masa tambari baya abota da talaka, idan kuwa kika ganshi da wanda ya fi rufin asiri to wlh aboki ne irin tun na ƙuruciya da ba yanda ya iya da shi irin su Nura Tela, su ɗin ma da ta in da yake morar su shi ya sa yake tare da su".
"Kai kuma na hanaka magana akan yaron nan in dai ba alkhairin za zaka faɗa ba amma ka ƙi ji ko Mu'azzam? Ai shikenan" Mama ta faɗa.
Ya wuce yana cewa
"Ni fa gaskiya na ke faɗi ba wani abu ba ko tun da na ke na taɓa yi masa sharri? Duk abin da zan faɗa halin sa ne idan kuma ƙarya aka masa ai ga ta nan ta faɗo abokanan sa guda biyu da suke ƙasa da shi".
Ni dai shiru na yi kawai ina bin sa da kallo can ƙasan raina kuma ina ƙoƙarin lissafo abokanan Bilal ɗin da ya ce wanda suke ƙasa da shi a wadata amma na gaza samo ko guda ɗaya a waɗanda na sani.
Abokanan sa da na yiwa farin sani mutum huɗu ne. Nasir chemist ɗin sa uku kuma na cikin unguwar mu ma shi ne ƙarami a cikin su banda gidan gona da ya ke da shi yana siyar da kaji da ƙwai sai Abduljabbar su maƙwaftan mu ne a da kafin suka koma Abuja da zama yanzu haka a CBN yake aiki, sai Nura Tela shi ma kuma ni dai ba zan saka shi a layin marasa wadata ba domin a shaidar gani da ido ma a guri na ya fi Bilal tun da matar sa ko makaho ya shafa jikin ta ya san tana cikin jin daɗi, gi da ne kawai za'a ce na Bilal ya fi na sa kyau da tsari baya ga haka banga ta in da ya fishi ba sai kuma Aliko, shi kam ko a kantin Kwari ma oga ne. Su ne kusan abokanan sa da duk wanda ya san shi ya san su, sauran ma kuma duk daga na gurin aikin har na gari kowa da sabgogin sa, gaskiyar Mu'azzam Billa ba shi da abokanai talakawa. Amma kuma wannan ba hujja ba ce da za'a ce masa kwaɗayayye ko mai son zuciya.
Sai da Anty Labiba ta zo ta ringa fitar da kayan tana faɗar kuɗin su jiki na ya sake sanyi da lamarin Hafiz, a wata akwati ta zuba kayan dan rigunan duk manya ne ƙananan ciki ba su da yawa ta haɗe su da sauran na barkar mu data ware ta ɓoye bayan ta gama ta ce
"Na san a ranki zagi na kike kina cewa na tattare muku kaya na ɓoye ko? Duk idan lokacin amfanin su ya kai da kaina zan fito da su na kawo miki dan wlh ba za'a tattara kaya ki kaisu gidan na san ki sarai yanda kika ringa kwasar suturun ki kina rabawa ƙannen sa suma haka zaki kwashe ki basu tun da ba sanin zafin su kika yi ba. Ranar suna ina kallon Lace ɗin da figaggiyar ƙanwar nan ta sa ta saka ko kin zata ban gane shi ba? Tun ranar ɗaurin auren ki bana jin kin sake sakawa shine kika bata, zanin da ta yi goyo da shi ma na super da aka kai ki da ita a jikin ki ne".