Sashe 97
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 41*
A yayinda muke shirin kammala wannan littafi, idan kin san kina karantawa ba tareda kin siya ba kiyi ƙoƙari ki sauke nauyi domin babu lallai in yafe haƙƙina. Account details suna sama 🙏🏽🙏🏽
A hankali na buɗe ido na jin saukar abu mai sanyi a goshi na, ganin na buɗe idon ya saka Mama janye hannunta, ganin da tayi ina shirin sake komawa baccin ya saka ta ce
"Da dai kin tashi haka nan kuma ki ƙarfafa jikinki tunda dai zazzaɓin ya sauka". Na yunƙura na zauna ina cije baki saboda kaina daya sara, dukda zazzaɓin da rafke ni ya sauka amma har yanzun bana jin ƙwarin jikina. Banɗaki ta shiga bata jima ba ta fito tana cewa
"Ga ruwa can na tara miki kiyi wankan Zainab zata kawo miki abinci" daga haka ta juya ta fita na rakata da ido ƙauna da kuma tausayinta suna sake ratsani. Allah sarki iyaye masu daɗi duk inda akaje aka dawo su ɗin dai ko sun yi fushi a hakan zasuyi haƙuri su karɓe ka. Jiya ta gama nanata ta gaji da zaman da nake gabanta amma hankalinta yafi na kowa tashi da yanayin da na shigo gidan bayan da na baro Hafiz.
Na runtse ido na saboda yanda tuna Hafiz ɗin ya dawo mun da zantukansa da sukayi matuƙar kiɗimani haɗi da hargitsamun tunani, hawaye suka ɓalle mun, dukda har yanzun na kasa gasgata maganarsa wai Bilal yayi aure amma tunanin hakan kaɗai da nakeyi ace da gaske ne ji nake zuciyata kamar zata ƙone saboda zafin da takeyi mun, ba zan taɓa iya jurar ganin wannan baƙin cikin ba wata mace a rayuwar Bilal sai kawai na haɗe kai da guiwa tareda fashewa da kuka mai sauti harda shassheƙa.
Ƙarar ruwa dake ta zuba ya saka na tashi daƙyar bayan da na haɗiye kukan nayo wanka haɗi da alwala na fito, kan gado na sake komawa na zauna, gaba ɗaya komai ya sake jagulemun na sake komawa yanayin da nasha wahala kafin na samu kaina daga cikin sa. Saƙe saƙe kala kala zuciya ta ringa kawo mun, daga ƙarshe na yaƙi kaina ta hanyar tashi na ɗora dogon hijabi kan towel ɗin dake ɗaure jikina na shiga jera nafila duk da cewar bayan la'asar ne magriba ma ta gabato lokacin.
Bayan sallar isha'i ina kwance a ƙasa, duk yanda naso na mayar da hankali na kan lazumin da nakeyi na kasa gaba ɗaya tunani na ya tafi akan son sanin haƙiƙanin gaskiyar abinda Hafiz ya faɗa mun. Idan har da gasken ne Bilal yayi aure toh wa ya aura? Ko Jalilan da suka gama sheƙe ayarsu a titi ya aura? ko kuma wata daban?
Zuciya ta raya mun 'ko kuma duniyar sa ba? Ko wacce ya kaini gidansu gaisuwa. Duk a rana ɗaya na sansu ranar da na bankaɗo sirrinsa da Jalilah ƙila ɗaya daga cikinsu ya aura. Sabbin hawaye suka ɓalle mun, bai ko bani damar yi masa tambayoyi da yawa da suke cunkushe cikin zuciyata ba kafin na baro gidan sa har a yanzun kuma daya dawo daga yanda ya ɓullo na fahimci baya buƙatar warware ƙullin baya kawai so yakeyi mu ɗora sabon babi.
Da hannu biyu na rufe fuskata ina jan kuka, na rasa tunanin daya kamata nayi, mai yasa Bilal zai mun haka? Duk haƙurin da nayi duk juriyar da nayi akan lamuransa lokaci ɗaya ya rasa irin sakayyar da zaiyi mun sai wannan?
Jin ana ƙwanƙwasa ƙofa ya saka na shiga goge fuskata da sauri dan zaryar da Zainab take mun na san da wahala idan ba CID Mama ta sakata ba, kuma daga yanayinta tun jiya da yanda Abba da kansa ya ce na fita gurin Hafiz ɗin na tabbatar ma abinda na jima ina ɓoye musu ya rigada ya bayyana ma'ana ya faɗa musu komai akan Bilal da Jalilah ga kuma wata sabuwa data ɓullo yanzu.
Ɗaga murya nayi na ce ta shigo bayan da na tashi zaune na jingina da Gado. Ganin Abba ya saka zuciyata ta shiga bugawa da sauri da sauri, haka nan ban tuna sanda Abba ya shigo ɗakina ba tun ma zamanin yammatanci balle yanzun na san dole abu ne me muhimmanci ya kawo shi. Kan bedside drawer ya zauna ba yabo ba fallasa yana amsa gaisuwar da nake masa, muka yi shiru kafin can ya ce
"Kin san me yasa na biyo ki har ɗaki?" Na girgiza kai alamar aa, ya ce
"Saboda ki gane muhimmancin maganar da nake so mu tattauna dake". Bugun da zuciyata keyi ya saka tsananta har wani ɗumi numfashina ya ɗauka gaba ɗaya a tsorace nake ban san wace magana zai mun ba dukda bana raba ɗaya biyu akan Bilal ce amma me zai ce mun?
"Nasan baki manta ba ni nayi tsaye na goya miki baya kika auri yaron nan dukda yanda mahaifiyarki da yan uwanta har ma da nawa yan uwan suke ganin rashin dacewarki dashi. Ki sani, abu biyu zuwa uku na duba da har na amince da aurenku. Na farko, a iya binciken da nayi akansa ba'a same shi da wani mugun hali wanda zai saka a ƙi bashi aure ba, dai dai gwargwado ya samu shaida ta mu'amala kuma ana kyautata masa zato akan addininsa. Abu na biyu soyayyarki gare shi, yanda kike mu'amalantar sa ya tuna mun yanda muka rayu da mahaifiyarki a lokacin da ban ma kai shi ba domin ni sanda na aureta banida da ko tartibiyar sana'a amma a hakan ta ƙaunace ni har kuma Allah ya kawo mu matsayin da muke kai a yanzu.
Na kyautata masa zato kuma son da nake miki da burin ganin na samar miki da farinciki a rayuwarki ya saka na amince na bashi aurenki bisa kyakkyawan yaƙinin zai riƙe mun ke amana amma baki ɗauki dogon lokaci a gidan aurenki ba na fara dana sanin biyewa zuciya, a ƙoƙarin son samuwar farin cikinki har hakan ya rufe mun ido na kasa hasaso idan aka samu akasi wani hali rayuwarki zata shiga?
Duk da haka ban sare ba, na cigaba da yi muku addu'a na kuma ringa tallafa miki a ganina raguwar ɗawainiyar zata taimaka gurin samun dai daito a zamantakewarku musamman tunda na fahimci halayya da kuma ɗabi'ar mijin da kika zaɓi rayuwa dashi. Ko da baki taɓa zuwa kin faɗi laifin sa ba amma komai a bayyane yake, kuma wannan hujjar na riƙe a duk sanda mahaifiyarki ta so yin bore ko kawo hargitsi cikin zamanki da shi na kan nusassheta da cewar a gurinta ne take ganin gazawa ko matsi a zaman da kikeyi amma ni a guri na lafiya kike zaune domin baki taɓa zuwa kin kawo ƙara ko kin faɗawa wani damuwarki ba na kuma san ba dan baki da damuwar bane sai dan halin zurfin ciki da kuma soyayyar dake wahalar dake kin kuma yarda zaki rayuwa dashi cikin kowanne irin yanayi sa'annan akwai nauyi da gudun kar ayi miki dariya sanin kowa sai da ya ce miki kar kiyi kikace kinji kin gani.
Duk da dai da fari na ɗauka rashin wadata ne sanadin abubuwan da suke wakana a tsakaninku shiyasa ban taɓa cewa komai ba nake kuma iya bakin ƙoƙari na gurin ganin na samar miki da abinda ya gagara baki sannan kuma na hana mahaifiyar ki ko wani nata duk sanda sukayi yunƙurin ɗaukar wani mataki akan zamantakewarku amma daga baya idona ya buɗe na kuma fahimci komai, tsantsar son kai da mugunta ce kawai take damun sa ba wai babu bace.
Ina so san cewa ke kike son Bilal Halimatu kuma ko da ace yana sonki to ki sani bai kai ko kwatan soyayyarki gare shi ba. Iya zamanki a gidan nan daga zuwanki zuwa rashin lafiyar da kikayi kawo yanzu ta isa hujjar da zakiyiwa kanki Hisabi ba tareda wani ya ce miki komai ba, idan ba dan na samu tabbaci daga wanda ba zai mun ƙarya ba da banzan taɓa yarda da cewar da igiyar aurensa akanki yayi miki irin wannan tozarcin ba".
Sai lokacin na ɗaga kaina na kalle shi jin kalmar tozarci daya faɗa idanuwana basa ko gani da kyau saboda hawayen da suke cikinsu, ya gyaɗa mun kai cikin tabbatarwa ya ce
"Babu wani namiji da yake ganin matarsa da ƙima da zaiyi kwatankwacin abinda Bilal ya aikata miki. Da kansa ya ɗakko ki ya kawoki gidan nan saboda ya nuna miki cewar ke bakya gabansa, a sanadin sa kika kusa rasa rayuwarki kuma har kikayi jinya kika gama shi ki wani nasa babu wanda ya tako yazo yaga ya kike sai surutu da maganganun da suka ringa yawo da su suna faɗan abubuwa marasa daɗi akanki, duk wannan bai isa ba tunda ya fahimci har yanzun kina yawo cikin duniyar mafarkinki shiyasa ya ɗaura aure abunsa da wata.
Kin san duk me yasa na tsaya ina miki wannan dogon bayanin kafin na faɗa miki ainihin abinda ya kawo ni?" Cikin kuka na ce
"Aa Abba" ya gyara zama ya ce
"Saboda na lura baki da tunanin kanki ba kuma kya gane komai sai abinda zuciyarki ta aminta dashi. Tuntuni na tsammaci ganin sauyi tattare dake amma akasin haka na lura a maimakon sauƙi kullum al'amuranki ƙara lalacewa sukeyi. A cikin zuciyarki nan na tabbatar duk lokacin nan kina jiran Bilal ya zo ya lallasheki ya faɗa miki maganganu dai dai da waɗanda kike so kiji daga nan ku shirya ku koma shiyasa kika zaɓi haɗiye baƙin cikinki ke kaɗai kika ƙi gayawa kowa dan kar hakan ya saka a baki shawarar ki haƙura dashi ko?"
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 41*
A yayinda muke shirin kammala wannan littafi, idan kin san kina karantawa ba tareda kin siya ba kiyi ƙoƙari ki sauke nauyi domin babu lallai in yafe haƙƙina. Account details suna sama 🙏🏽🙏🏽
A hankali na buɗe ido na jin saukar abu mai sanyi a goshi na, ganin na buɗe idon ya saka Mama janye hannunta, ganin da tayi ina shirin sake komawa baccin ya saka ta ce
"Da dai kin tashi haka nan kuma ki ƙarfafa jikinki tunda dai zazzaɓin ya sauka". Na yunƙura na zauna ina cije baki saboda kaina daya sara, dukda zazzaɓin da rafke ni ya sauka amma har yanzun bana jin ƙwarin jikina. Banɗaki ta shiga bata jima ba ta fito tana cewa
"Ga ruwa can na tara miki kiyi wankan Zainab zata kawo miki abinci" daga haka ta juya ta fita na rakata da ido ƙauna da kuma tausayinta suna sake ratsani. Allah sarki iyaye masu daɗi duk inda akaje aka dawo su ɗin dai ko sun yi fushi a hakan zasuyi haƙuri su karɓe ka. Jiya ta gama nanata ta gaji da zaman da nake gabanta amma hankalinta yafi na kowa tashi da yanayin da na shigo gidan bayan da na baro Hafiz.
Na runtse ido na saboda yanda tuna Hafiz ɗin ya dawo mun da zantukansa da sukayi matuƙar kiɗimani haɗi da hargitsamun tunani, hawaye suka ɓalle mun, dukda har yanzun na kasa gasgata maganarsa wai Bilal yayi aure amma tunanin hakan kaɗai da nakeyi ace da gaske ne ji nake zuciyata kamar zata ƙone saboda zafin da takeyi mun, ba zan taɓa iya jurar ganin wannan baƙin cikin ba wata mace a rayuwar Bilal sai kawai na haɗe kai da guiwa tareda fashewa da kuka mai sauti harda shassheƙa.
Ƙarar ruwa dake ta zuba ya saka na tashi daƙyar bayan da na haɗiye kukan nayo wanka haɗi da alwala na fito, kan gado na sake komawa na zauna, gaba ɗaya komai ya sake jagulemun na sake komawa yanayin da nasha wahala kafin na samu kaina daga cikin sa. Saƙe saƙe kala kala zuciya ta ringa kawo mun, daga ƙarshe na yaƙi kaina ta hanyar tashi na ɗora dogon hijabi kan towel ɗin dake ɗaure jikina na shiga jera nafila duk da cewar bayan la'asar ne magriba ma ta gabato lokacin.
Bayan sallar isha'i ina kwance a ƙasa, duk yanda naso na mayar da hankali na kan lazumin da nakeyi na kasa gaba ɗaya tunani na ya tafi akan son sanin haƙiƙanin gaskiyar abinda Hafiz ya faɗa mun. Idan har da gasken ne Bilal yayi aure toh wa ya aura? Ko Jalilan da suka gama sheƙe ayarsu a titi ya aura? ko kuma wata daban?
Zuciya ta raya mun 'ko kuma duniyar sa ba? Ko wacce ya kaini gidansu gaisuwa. Duk a rana ɗaya na sansu ranar da na bankaɗo sirrinsa da Jalilah ƙila ɗaya daga cikinsu ya aura. Sabbin hawaye suka ɓalle mun, bai ko bani damar yi masa tambayoyi da yawa da suke cunkushe cikin zuciyata ba kafin na baro gidan sa har a yanzun kuma daya dawo daga yanda ya ɓullo na fahimci baya buƙatar warware ƙullin baya kawai so yakeyi mu ɗora sabon babi.
Da hannu biyu na rufe fuskata ina jan kuka, na rasa tunanin daya kamata nayi, mai yasa Bilal zai mun haka? Duk haƙurin da nayi duk juriyar da nayi akan lamuransa lokaci ɗaya ya rasa irin sakayyar da zaiyi mun sai wannan?
Jin ana ƙwanƙwasa ƙofa ya saka na shiga goge fuskata da sauri dan zaryar da Zainab take mun na san da wahala idan ba CID Mama ta sakata ba, kuma daga yanayinta tun jiya da yanda Abba da kansa ya ce na fita gurin Hafiz ɗin na tabbatar ma abinda na jima ina ɓoye musu ya rigada ya bayyana ma'ana ya faɗa musu komai akan Bilal da Jalilah ga kuma wata sabuwa data ɓullo yanzu.
Ɗaga murya nayi na ce ta shigo bayan da na tashi zaune na jingina da Gado. Ganin Abba ya saka zuciyata ta shiga bugawa da sauri da sauri, haka nan ban tuna sanda Abba ya shigo ɗakina ba tun ma zamanin yammatanci balle yanzun na san dole abu ne me muhimmanci ya kawo shi. Kan bedside drawer ya zauna ba yabo ba fallasa yana amsa gaisuwar da nake masa, muka yi shiru kafin can ya ce
"Kin san me yasa na biyo ki har ɗaki?" Na girgiza kai alamar aa, ya ce
"Saboda ki gane muhimmancin maganar da nake so mu tattauna dake". Bugun da zuciyata keyi ya saka tsananta har wani ɗumi numfashina ya ɗauka gaba ɗaya a tsorace nake ban san wace magana zai mun ba dukda bana raba ɗaya biyu akan Bilal ce amma me zai ce mun?
"Nasan baki manta ba ni nayi tsaye na goya miki baya kika auri yaron nan dukda yanda mahaifiyarki da yan uwanta har ma da nawa yan uwan suke ganin rashin dacewarki dashi. Ki sani, abu biyu zuwa uku na duba da har na amince da aurenku. Na farko, a iya binciken da nayi akansa ba'a same shi da wani mugun hali wanda zai saka a ƙi bashi aure ba, dai dai gwargwado ya samu shaida ta mu'amala kuma ana kyautata masa zato akan addininsa. Abu na biyu soyayyarki gare shi, yanda kike mu'amalantar sa ya tuna mun yanda muka rayu da mahaifiyarki a lokacin da ban ma kai shi ba domin ni sanda na aureta banida da ko tartibiyar sana'a amma a hakan ta ƙaunace ni har kuma Allah ya kawo mu matsayin da muke kai a yanzu.
Na kyautata masa zato kuma son da nake miki da burin ganin na samar miki da farinciki a rayuwarki ya saka na amince na bashi aurenki bisa kyakkyawan yaƙinin zai riƙe mun ke amana amma baki ɗauki dogon lokaci a gidan aurenki ba na fara dana sanin biyewa zuciya, a ƙoƙarin son samuwar farin cikinki har hakan ya rufe mun ido na kasa hasaso idan aka samu akasi wani hali rayuwarki zata shiga?
Duk da haka ban sare ba, na cigaba da yi muku addu'a na kuma ringa tallafa miki a ganina raguwar ɗawainiyar zata taimaka gurin samun dai daito a zamantakewarku musamman tunda na fahimci halayya da kuma ɗabi'ar mijin da kika zaɓi rayuwa dashi. Ko da baki taɓa zuwa kin faɗi laifin sa ba amma komai a bayyane yake, kuma wannan hujjar na riƙe a duk sanda mahaifiyarki ta so yin bore ko kawo hargitsi cikin zamanki da shi na kan nusassheta da cewar a gurinta ne take ganin gazawa ko matsi a zaman da kikeyi amma ni a guri na lafiya kike zaune domin baki taɓa zuwa kin kawo ƙara ko kin faɗawa wani damuwarki ba na kuma san ba dan baki da damuwar bane sai dan halin zurfin ciki da kuma soyayyar dake wahalar dake kin kuma yarda zaki rayuwa dashi cikin kowanne irin yanayi sa'annan akwai nauyi da gudun kar ayi miki dariya sanin kowa sai da ya ce miki kar kiyi kikace kinji kin gani.
Duk da dai da fari na ɗauka rashin wadata ne sanadin abubuwan da suke wakana a tsakaninku shiyasa ban taɓa cewa komai ba nake kuma iya bakin ƙoƙari na gurin ganin na samar miki da abinda ya gagara baki sannan kuma na hana mahaifiyar ki ko wani nata duk sanda sukayi yunƙurin ɗaukar wani mataki akan zamantakewarku amma daga baya idona ya buɗe na kuma fahimci komai, tsantsar son kai da mugunta ce kawai take damun sa ba wai babu bace.
Ina so san cewa ke kike son Bilal Halimatu kuma ko da ace yana sonki to ki sani bai kai ko kwatan soyayyarki gare shi ba. Iya zamanki a gidan nan daga zuwanki zuwa rashin lafiyar da kikayi kawo yanzu ta isa hujjar da zakiyiwa kanki Hisabi ba tareda wani ya ce miki komai ba, idan ba dan na samu tabbaci daga wanda ba zai mun ƙarya ba da banzan taɓa yarda da cewar da igiyar aurensa akanki yayi miki irin wannan tozarcin ba".
Sai lokacin na ɗaga kaina na kalle shi jin kalmar tozarci daya faɗa idanuwana basa ko gani da kyau saboda hawayen da suke cikinsu, ya gyaɗa mun kai cikin tabbatarwa ya ce
"Babu wani namiji da yake ganin matarsa da ƙima da zaiyi kwatankwacin abinda Bilal ya aikata miki. Da kansa ya ɗakko ki ya kawoki gidan nan saboda ya nuna miki cewar ke bakya gabansa, a sanadin sa kika kusa rasa rayuwarki kuma har kikayi jinya kika gama shi ki wani nasa babu wanda ya tako yazo yaga ya kike sai surutu da maganganun da suka ringa yawo da su suna faɗan abubuwa marasa daɗi akanki, duk wannan bai isa ba tunda ya fahimci har yanzun kina yawo cikin duniyar mafarkinki shiyasa ya ɗaura aure abunsa da wata.
Kin san duk me yasa na tsaya ina miki wannan dogon bayanin kafin na faɗa miki ainihin abinda ya kawo ni?" Cikin kuka na ce
"Aa Abba" ya gyara zama ya ce
"Saboda na lura baki da tunanin kanki ba kuma kya gane komai sai abinda zuciyarki ta aminta dashi. Tuntuni na tsammaci ganin sauyi tattare dake amma akasin haka na lura a maimakon sauƙi kullum al'amuranki ƙara lalacewa sukeyi. A cikin zuciyarki nan na tabbatar duk lokacin nan kina jiran Bilal ya zo ya lallasheki ya faɗa miki maganganu dai dai da waɗanda kike so kiji daga nan ku shirya ku koma shiyasa kika zaɓi haɗiye baƙin cikinki ke kaɗai kika ƙi gayawa kowa dan kar hakan ya saka a baki shawarar ki haƙura dashi ko?"