Sashe 119
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ɓacin rai haɗi da baƙin ciki suka kamashi lokaci ɗaya, fita yayi daga nan ya wuce part ɗin sa da sauri domin zuwa yanzu ya fahimci su Halima ne sukayi gidan tsirara. Ta window nan ɗin ma ya hango filin gurin sai tsirarun kayan da suke mallakinsa na falon kamar DSTV decoder sai wani teburi da sai bayan tafiyarta ya kawo shi gidan ya ɗora computer akai dan yana shirye shiryen fara Forex trading da zarar ya haɗa kan kuɗaɗen shagunan Jalilah daya siyar.
Bai shiga ɗakin ba dan ya tabbatar yanda yaga falon an masa tik haka zai tarar da cikin ma saboda dai komai da yake gidan ya sani mallakinta idan aka cire kayan sakawarsa sai yan tsirarun abubuwan da ba za'a rasa ba. Tunga ya ja yana saƙa da warwara a ransa, bai taɓa zaton zasu kwashe kaya ba domin ya san basu rabu da Halima ba, Halimar daya sani ba zata iya rabuwa dashi haka salin alin ba tilas ta dawo masa ko kwashe kayan ma ya sani ba zai wuce wannan yar abu ta kazan ƙanwar Babar tata bace Labiba dan dai ko Mama yana da yaƙinin ba zata ce azo a kwashe kaya daga yin saki jiya ba.
Guri ya samu cikin tarkacen da suka watso tsakar gidan ya zauna saboda kansa da ya ji ya sara masa, shi da ya gama lissafi akan kawai Zulaiha zata tare a nan gidan shiyasa ko da suka kawo zancen babu kayan ɗaki bai musa ba idan ya so daga baya a hankali sai ya shiryawa Halima can gidan idan ta tashi komowa ta tare a can ɗin shine suka masa akuya suka rusa masa lissafi.
Ko me ya tuna kuma ya miƙe da sauri kamar wanda aka zabura ya fita. A ƙofar gidansa ya tsaya yana ƙwalawa Iliyas, ɗaya daga cikin masu gadin bakin layin kira yanda kasan duniya ce zata tashi. Ilyas ɗin ya taso da sauri jin kiran kamar ba na lafiya ba, ya ɗan rusuna ya ce
"Lafiya Alhaji?"
"Wace lafiya? Kuna ina ɓarayi suka hauro mun gida suka kwashe kaya suka fita da su?" Bilal ɗin ya faɗa cikin kiɗimar ƙarya, Ilyas ya kalle shi ba yabo ba fallasa ya ce
"Ɓarayi kuma?"
"Eh, ko da yake ba ma zai yuwu ace ɓarayi bane sai dai idan da ku aka haɗa baki, wato kunga matar gidan bata nan shine kuka daidaici na fita kuka shiga kuka kwashe mun kayan gida ko? Toh wlh kotu ce zata rabani da ku, sai kun gwammace kiɗa da karatu zaku san kun jangwalowa kanku tsiya" Bilal ɗin ya faɗa yana zaro waya a aljihu.
Basiru, ɗaya mai gadin da hargagin Bilal ya saka ya taso ya ce masa
"Ji mana Alaji, karka kuskura ka sake ce mana ɓarayi idan ba haka ba zaka sha mamaki wlh. Dan muna aiki a nan ba yana nufin bamu da ƙima ko daraja ba da kowa zai taka mu yanda yake so, da kuma zaka zo kanawa mutane haukar ƙarya, waye bai san ka saki matar gidan ba?
Ta zo ta kwashe kayanta, kawai ka ce yanzu ka rasa in d zaka ringa kawo matan banza ne shine zaka fiti kana wani ƙaramin hauka"
"Kai, dan abu ta kazanka ni kake faɗawa haka?" Bilal ya zaburo kamar zai kama shi da kokawa. Alhaji Bashir, mijin Maman Yusuf da mai gidan da yake jikin nasa Alhaji Sharif suka ƙaraso gurin da sauri dukda tun daga nesa duk sun ji abinda Bilal ɗin da kuma masu gadin suke tattaunawa. Su suka shiga tsakani ganin Basiru ya tattare hannun riga yana jira Bilal dake hargagi kamar zai kai masa duka Ilyas yana riƙeshi.
"Haba Alhaji Bashir, wane irin abu ne haka da girmanka zaka tsaya kana irin wannan abun da yara?" Alhaji Sharif da ya shiga tsakani ya faɗa. Bilal yayi tsaki yana kallon masu gadin ya ce
"Sata suka mun a gida na tambayi ba'asi kuma shine zasu mun rashin kunya".
"Me aka satar maka?" Alhaji Bashir ya tambaya kafin Bilal ya bashi amsa Ilyas yayi saurin cewa
"Ranka ya daɗe tabarmar kunya kawai yake naɗewa da hauka, dama kusan wata biyu kenan ai matar gidan bata nan to shine yau suka zo suka kwashe kaya da alama aure ya ƙare shikenan fa zai sauke fushinsa akanmu sai kace mu muka saka ya saketa".
"Yanzu menene amfanin haka saboda Allah? Sanda aka kwashe kayan nan babu kowa ma a layin sai su, ni kaina ba dan yar uwarta data shiga gidana neman abu ba ba zan san meya faru ba amma yanzu ka fito kana hayagaga a layi har masu wucewa ka sanar musu da kun rabu da matarka" Alhaji Bashir ya faɗa kafin ya juya kan masu gadin ya ce su wuce bakin aikinsu kowa ya fashe suka barshi shi kaɗai yana muzurai da zare ido. Sai da ya gaji da tsayuwa kafin ya koma ciki ya tsaya cike da tunanin mai ya kamata ya yi yanzu? Ko bargo baya tunanin akwai da zai shimfiɗa ya kwanta akai kafin wayewar gari, haka ya ɗauki tsintsiya a daren sai da ya share compound ɗin tas ya watsa sharar waje yanayi yana tsinewa yan uwan Halima da suka masa wannan abun.
Ɗakin sa ya shiga ya tsinci kaya kala biyu ya saka a leda dan yana ayyana abinda zaiyiwa Halima akan wannan tozarcin da ta saka aka masa, hatta takardunsa da suke cikin jakunkunanta sai da suka zazzage masa balle kayan sa na cikin akwati tunda dama ai ba shi ya siya mata ba suke nufi. Kulle gidan yayi bayan ya saukw wutar gaba ɗaya dan ba ƙaramin baƙin ciki ke kama zuciyarsa idan yaga kangon da aka bar masa ba.
Hotel ya tafi ya kama ya kwana yana Allah Allah washe gari tayi yaje ya saukewa Halima kwandon rashin mutunchi, banda dai su sun gaji tsiya sai kace wasu kayan Gwal ne aka saka mata da dan an saketa zasuce zasu kwashe kaya ya tabbatar masu arziƙin gaske ba haka sukeyi ba kuma tsabar rashin mutunchi har ajiye ajiyen sa na cikin fridge da freezer suka tattara suka tafi kamar ubansu ya siya masa.
Haka ya kwana saƙe saƙe, washe gari da wuri ya fita gurin kafinta dan ya samo kayan da za'a jerawa Zulaihan. Ya rigada ya karɓi kuɗin sa na kayan daya fara aka farayi tuni ƙarya kawai yayi mata, ya je ya samu ready made kaya kuwa na wata amarya da akayi sai kuma aka fasa auren, dake yana tsaye suka gama magana da kafintan daya karya wa kayan farashi saboda tsabar mugunta tamkar ba'a gurinsa sukayi ba wai ai tunda an rigada an ɗauka kaya sun zama second sai kuma da Bilal ɗin ya nuna yana son su ya nemi raina masa wayo zai siyar masa a sababbi daƙyar dai ciniki ya faɗa ya ɗaukar mata su set ɗin gado da kujera masu kyau harda dining ya ƙara wani set ɗin gadon ɗaya da zai saka a can ɗakinsa, har kujera ya so ya siya sai dai kuma abinda yake account ɗin sa ba zai ishe shi ba dan akawai sauran abubuwan da yake so yayi bayan nan.
A gurin ya bar musu akan gobe Alhamis za'a je a ɗauka dan yana so a ɗan sake fentin gidan yau dukda ba abinda gurin yayi amma dai amarya ce zata shiga ya kamata a gyara mata. Daga nan ya wuce gidan Hajja ya faɗa mata Halima tazo ta kwashe kaya,
"Matsitana banza da wofi, ka rabu da ita taje tayi ta yawo da aurenka a kanta ba kaya ba koma me ta kwashe a banza dan wlh ba zaka saketa ba" Hajjan ta sake jaddada masa. Shi dai bai ce komai ba dukda yayi niyyar ya gaya mata ya saki Haliman amma yanda ta haƙiƙance tana jaddada ba za'a saketa ba shiyasa yayi shiru dan ba laifi yau ɗin ya samu ta sake masa fuska dan a gidan ya tarar da Anty Habiba ya san kuma ba zai wuce zancen tariyar Zulaiha sukeyi ba tunda ya tura mata kuɗin da tace zasuyi yinin biki da shi tun jiya.
"Yanzu ina kuka tsaya da ita waccen shaiɗaniyar kuma?" Hajja ta dakatar dashi ganin yana shirin tashi, bai fahimci wa take nufi ba gane hakan ya saka ta ce
"Jalilah mana, ka san dai kamar da ƙasa aurenka da ita dan bata isa ta iskanta mun kai ta zubar mana da mutunchi sannan kuma ta ce ba zata aureka ba" cewar Hajjan. Abun sai ya ma bashi dariya, sai kace shine macen irin saurayi ya yaudareshi Hajjan take cewa dole sai an aure shi kuma. Anty Habiba ce ta ce
"Yanzu Hajja ba zaki bar maganar nan na har sai ta fita inda ba zamu so ba ko? Abinda ya faru ya faru sai mu lulluɓe magana ta wuce amma so kike sai kin ɗaga ta, tsakani da Allah yanzu ko ce miki yayi zai aureta sai ki yarda? Mai za'ayi da mace irinta? Bayan shi kika san maza nawa take ta'ammali dasu da har zaki ce kina so ki haɗa zuri'a da ita bayan abinda ya faru? Toh Allah ya rufa mana asiri gaskiya ba zaki bankaɗa mana ba kuma babu wannan maganar kai Bilal babu kai babu ita ka kama matanka ka riƙe Allah ya yafe maka abinda ya faru a baya kawai".
Haka ya lallaɓa ya fice, anan unguwar ya samu wanda zasu masa aikin fenti suka tafi tare suka duba ya basu kuɗin da suka buƙata na abinda zasu siya daga nan ya wuce gidan Hafiz wanda ya kira shi akan idan babu damuwa yana so ya ganshi.
Shi kam yanzu idan ba Hafiz ɗin ne ya kirashi ba mantawa ma yakeyi da wnazuwarsa a duniyar nan baki ɗaya. To dama dalilin bibiyar Hafiz ɗin ai saboda abun hannunsa ne da bajintar da yakeyi masa yanzu kuwa da ya fara kama ƙasa shima gani yake Hafiz ɗin ba komai bane dan sai ya ga kamar Jalilah ma tafi Hafiz ɗin kuɗi saboda irin kyautar da takeyi masa a dunƙule tashi ɗaya sai Hafiz ya rabata gida goma ko fiye da haka.
Bai shiga ɗakin ba dan ya tabbatar yanda yaga falon an masa tik haka zai tarar da cikin ma saboda dai komai da yake gidan ya sani mallakinta idan aka cire kayan sakawarsa sai yan tsirarun abubuwan da ba za'a rasa ba. Tunga ya ja yana saƙa da warwara a ransa, bai taɓa zaton zasu kwashe kaya ba domin ya san basu rabu da Halima ba, Halimar daya sani ba zata iya rabuwa dashi haka salin alin ba tilas ta dawo masa ko kwashe kayan ma ya sani ba zai wuce wannan yar abu ta kazan ƙanwar Babar tata bace Labiba dan dai ko Mama yana da yaƙinin ba zata ce azo a kwashe kaya daga yin saki jiya ba.
Guri ya samu cikin tarkacen da suka watso tsakar gidan ya zauna saboda kansa da ya ji ya sara masa, shi da ya gama lissafi akan kawai Zulaiha zata tare a nan gidan shiyasa ko da suka kawo zancen babu kayan ɗaki bai musa ba idan ya so daga baya a hankali sai ya shiryawa Halima can gidan idan ta tashi komowa ta tare a can ɗin shine suka masa akuya suka rusa masa lissafi.
Ko me ya tuna kuma ya miƙe da sauri kamar wanda aka zabura ya fita. A ƙofar gidansa ya tsaya yana ƙwalawa Iliyas, ɗaya daga cikin masu gadin bakin layin kira yanda kasan duniya ce zata tashi. Ilyas ɗin ya taso da sauri jin kiran kamar ba na lafiya ba, ya ɗan rusuna ya ce
"Lafiya Alhaji?"
"Wace lafiya? Kuna ina ɓarayi suka hauro mun gida suka kwashe kaya suka fita da su?" Bilal ɗin ya faɗa cikin kiɗimar ƙarya, Ilyas ya kalle shi ba yabo ba fallasa ya ce
"Ɓarayi kuma?"
"Eh, ko da yake ba ma zai yuwu ace ɓarayi bane sai dai idan da ku aka haɗa baki, wato kunga matar gidan bata nan shine kuka daidaici na fita kuka shiga kuka kwashe mun kayan gida ko? Toh wlh kotu ce zata rabani da ku, sai kun gwammace kiɗa da karatu zaku san kun jangwalowa kanku tsiya" Bilal ɗin ya faɗa yana zaro waya a aljihu.
Basiru, ɗaya mai gadin da hargagin Bilal ya saka ya taso ya ce masa
"Ji mana Alaji, karka kuskura ka sake ce mana ɓarayi idan ba haka ba zaka sha mamaki wlh. Dan muna aiki a nan ba yana nufin bamu da ƙima ko daraja ba da kowa zai taka mu yanda yake so, da kuma zaka zo kanawa mutane haukar ƙarya, waye bai san ka saki matar gidan ba?
Ta zo ta kwashe kayanta, kawai ka ce yanzu ka rasa in d zaka ringa kawo matan banza ne shine zaka fiti kana wani ƙaramin hauka"
"Kai, dan abu ta kazanka ni kake faɗawa haka?" Bilal ya zaburo kamar zai kama shi da kokawa. Alhaji Bashir, mijin Maman Yusuf da mai gidan da yake jikin nasa Alhaji Sharif suka ƙaraso gurin da sauri dukda tun daga nesa duk sun ji abinda Bilal ɗin da kuma masu gadin suke tattaunawa. Su suka shiga tsakani ganin Basiru ya tattare hannun riga yana jira Bilal dake hargagi kamar zai kai masa duka Ilyas yana riƙeshi.
"Haba Alhaji Bashir, wane irin abu ne haka da girmanka zaka tsaya kana irin wannan abun da yara?" Alhaji Sharif da ya shiga tsakani ya faɗa. Bilal yayi tsaki yana kallon masu gadin ya ce
"Sata suka mun a gida na tambayi ba'asi kuma shine zasu mun rashin kunya".
"Me aka satar maka?" Alhaji Bashir ya tambaya kafin Bilal ya bashi amsa Ilyas yayi saurin cewa
"Ranka ya daɗe tabarmar kunya kawai yake naɗewa da hauka, dama kusan wata biyu kenan ai matar gidan bata nan to shine yau suka zo suka kwashe kaya da alama aure ya ƙare shikenan fa zai sauke fushinsa akanmu sai kace mu muka saka ya saketa".
"Yanzu menene amfanin haka saboda Allah? Sanda aka kwashe kayan nan babu kowa ma a layin sai su, ni kaina ba dan yar uwarta data shiga gidana neman abu ba ba zan san meya faru ba amma yanzu ka fito kana hayagaga a layi har masu wucewa ka sanar musu da kun rabu da matarka" Alhaji Bashir ya faɗa kafin ya juya kan masu gadin ya ce su wuce bakin aikinsu kowa ya fashe suka barshi shi kaɗai yana muzurai da zare ido. Sai da ya gaji da tsayuwa kafin ya koma ciki ya tsaya cike da tunanin mai ya kamata ya yi yanzu? Ko bargo baya tunanin akwai da zai shimfiɗa ya kwanta akai kafin wayewar gari, haka ya ɗauki tsintsiya a daren sai da ya share compound ɗin tas ya watsa sharar waje yanayi yana tsinewa yan uwan Halima da suka masa wannan abun.
Ɗakin sa ya shiga ya tsinci kaya kala biyu ya saka a leda dan yana ayyana abinda zaiyiwa Halima akan wannan tozarcin da ta saka aka masa, hatta takardunsa da suke cikin jakunkunanta sai da suka zazzage masa balle kayan sa na cikin akwati tunda dama ai ba shi ya siya mata ba suke nufi. Kulle gidan yayi bayan ya saukw wutar gaba ɗaya dan ba ƙaramin baƙin ciki ke kama zuciyarsa idan yaga kangon da aka bar masa ba.
Hotel ya tafi ya kama ya kwana yana Allah Allah washe gari tayi yaje ya saukewa Halima kwandon rashin mutunchi, banda dai su sun gaji tsiya sai kace wasu kayan Gwal ne aka saka mata da dan an saketa zasuce zasu kwashe kaya ya tabbatar masu arziƙin gaske ba haka sukeyi ba kuma tsabar rashin mutunchi har ajiye ajiyen sa na cikin fridge da freezer suka tattara suka tafi kamar ubansu ya siya masa.
Haka ya kwana saƙe saƙe, washe gari da wuri ya fita gurin kafinta dan ya samo kayan da za'a jerawa Zulaihan. Ya rigada ya karɓi kuɗin sa na kayan daya fara aka farayi tuni ƙarya kawai yayi mata, ya je ya samu ready made kaya kuwa na wata amarya da akayi sai kuma aka fasa auren, dake yana tsaye suka gama magana da kafintan daya karya wa kayan farashi saboda tsabar mugunta tamkar ba'a gurinsa sukayi ba wai ai tunda an rigada an ɗauka kaya sun zama second sai kuma da Bilal ɗin ya nuna yana son su ya nemi raina masa wayo zai siyar masa a sababbi daƙyar dai ciniki ya faɗa ya ɗaukar mata su set ɗin gado da kujera masu kyau harda dining ya ƙara wani set ɗin gadon ɗaya da zai saka a can ɗakinsa, har kujera ya so ya siya sai dai kuma abinda yake account ɗin sa ba zai ishe shi ba dan akawai sauran abubuwan da yake so yayi bayan nan.
A gurin ya bar musu akan gobe Alhamis za'a je a ɗauka dan yana so a ɗan sake fentin gidan yau dukda ba abinda gurin yayi amma dai amarya ce zata shiga ya kamata a gyara mata. Daga nan ya wuce gidan Hajja ya faɗa mata Halima tazo ta kwashe kaya,
"Matsitana banza da wofi, ka rabu da ita taje tayi ta yawo da aurenka a kanta ba kaya ba koma me ta kwashe a banza dan wlh ba zaka saketa ba" Hajjan ta sake jaddada masa. Shi dai bai ce komai ba dukda yayi niyyar ya gaya mata ya saki Haliman amma yanda ta haƙiƙance tana jaddada ba za'a saketa ba shiyasa yayi shiru dan ba laifi yau ɗin ya samu ta sake masa fuska dan a gidan ya tarar da Anty Habiba ya san kuma ba zai wuce zancen tariyar Zulaiha sukeyi ba tunda ya tura mata kuɗin da tace zasuyi yinin biki da shi tun jiya.
"Yanzu ina kuka tsaya da ita waccen shaiɗaniyar kuma?" Hajja ta dakatar dashi ganin yana shirin tashi, bai fahimci wa take nufi ba gane hakan ya saka ta ce
"Jalilah mana, ka san dai kamar da ƙasa aurenka da ita dan bata isa ta iskanta mun kai ta zubar mana da mutunchi sannan kuma ta ce ba zata aureka ba" cewar Hajjan. Abun sai ya ma bashi dariya, sai kace shine macen irin saurayi ya yaudareshi Hajjan take cewa dole sai an aure shi kuma. Anty Habiba ce ta ce
"Yanzu Hajja ba zaki bar maganar nan na har sai ta fita inda ba zamu so ba ko? Abinda ya faru ya faru sai mu lulluɓe magana ta wuce amma so kike sai kin ɗaga ta, tsakani da Allah yanzu ko ce miki yayi zai aureta sai ki yarda? Mai za'ayi da mace irinta? Bayan shi kika san maza nawa take ta'ammali dasu da har zaki ce kina so ki haɗa zuri'a da ita bayan abinda ya faru? Toh Allah ya rufa mana asiri gaskiya ba zaki bankaɗa mana ba kuma babu wannan maganar kai Bilal babu kai babu ita ka kama matanka ka riƙe Allah ya yafe maka abinda ya faru a baya kawai".
Haka ya lallaɓa ya fice, anan unguwar ya samu wanda zasu masa aikin fenti suka tafi tare suka duba ya basu kuɗin da suka buƙata na abinda zasu siya daga nan ya wuce gidan Hafiz wanda ya kira shi akan idan babu damuwa yana so ya ganshi.
Shi kam yanzu idan ba Hafiz ɗin ne ya kirashi ba mantawa ma yakeyi da wnazuwarsa a duniyar nan baki ɗaya. To dama dalilin bibiyar Hafiz ɗin ai saboda abun hannunsa ne da bajintar da yakeyi masa yanzu kuwa da ya fara kama ƙasa shima gani yake Hafiz ɗin ba komai bane dan sai ya ga kamar Jalilah ma tafi Hafiz ɗin kuɗi saboda irin kyautar da takeyi masa a dunƙule tashi ɗaya sai Hafiz ya rabata gida goma ko fiye da haka.