Sashe 89
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri na ruƙota ina juya kai lokaci ɗaya hawaye ya ɓalle mun nace
"Bazan iya gayawa Mama ba Hansa'u"
"Anty Labiba fa?" Ta faɗa sai nayi saurin girgiza kai nace
"Gara kowa akanta". Murmushi tayi ta koma ta zauna ta dafa kafaɗata tace
"Ban sani ba ko har yanzu kina ɗaukata a irin matsayin da kike dashi a gurina". Nayi shiru ina kokawa da muryar Bilal dake nanata mun kaina zan tozarta idan na tona asirinsa. Da hannu biyu na toshe kunne na kafin na fizgo maganar da ƙarfi nace
"Matan banza yake bi Hansa'u" wannan maganar kuma tasa naji tamkar na buɗe wata ƙofa cikin zuciyata dan haka tiryan tiryan na shiga koro mata bayani tun daga aurena da Bilal duk wani abu da na haɗiye saida ya samu hanya ya fito da kansa na furtawa Hansa'u shi harda furucin da yayi akan Mama ban rage ba saida na amayar mata. Haka muka rungume juna ni kuka ita kuka babu mai rarrashin wani, mun daɗe a cikin yanayin kafin ta miƙe tana cewa
"Zanje na dawo Halima idan na zauna yanzu ina kallonki bazan samu ƙarfin guiwar ce miki komai ba zanje gida amma komai dare zan dawo". Ban ɗago na kalleta ba na ɗaga mata kai alamar "Toh".
Bayan tafiyar ta ji na ringayi kamar an kwashe mun wani ɓangare na jikina, tsabar yanda nauyin da ƙirji na yake mun ya ragu ina tsaka da kukan bacci ya kwashe ni dana farka kuma sai na ringa ji kamar bani ba, babu wannan abun da nake ji yana mun yawo tsakanin ƙirji da maƙogaro, haka na ƙarasa yinin ranar, har na fitar da rai da dawowar Hansa'u sai gata lokacin ƙarfe tara harta gota. Fuskarta duk ta tashi da alama bayan tafiyarta kuka ta cigaba dayi, a ɗaki muka sake ƙulewa, ta faɗa mun maganganu da sukayi tasiri sosai cikin ƙwaƙwalwata. Abu uku da na fi riƙewa cikin maganganunta tunatarwar da tayi mun akan addu'a.
"Halima tun ba yau ba na sani kina da sakaci gurin addu'a. Ki sani Allah yana fushi da bawan da baya roƙonsa. Ko da ace ubangiji ya hore maka komai a rayuwa ka kasance mai godiya a gareshi kuma ka cigaba da yi masa naci da roƙon ya taya ka tattala abinda ya baka ba kuma shikenan idan buƙatarka ta biya sai kuma sanda ka sake faɗawa cikin wata damuwar ne sannan zaka tuna da Allah ka sake roƙon sa ba shiyasa sai ya barmu da iyawarmu muga idan zamu iya yiwa kanmu.
Abu na farko da zaki fara shine ki gyara tsakaninki da mahaliccinki, kinga addu'a Halima tasirinta yawa ne dashi. Addu'a ta kan canza ƙaddara daga mummuna zuwa kyakkyawa, hatta da Bilal addu'a zata iya canza miki shu. Ubangiji yana son bawa mai naci da ƙasƙantar da kai akan buƙatar sa. Wani kuka ko ajiye abu a rai ba zai ƙareki da komai ba abinda yafi miki shine ki dage kiyita roƙon Allah karki gaji lokaci ya wuce da zamu kwanta muyita bacci da cewar ai komai daga Allah ne haka ne amma kuma ba zaka taɓa haɗa nasarar rayuwarka data wanda ya hana idonsa bacci ya roƙi ubangiji ba tamkar ka kwanta a ɗaki ne kana tsammanin ayi ruwan sama abinci ya faɗo ka ɗauka kaci ba tareda ka fita kayi aikin da zai samar maka da kuɗin da zaka siyi abincin ba.
Kada kuma ki ɗauka a sanda kika so a lokacin addu'ar ki zata karɓu ko kuma idan baki samu biyan buƙatar ki ba a lokacin kice kin dena Aa, shi Allah ba haka yake ba. Ubangiji yafi mu sanin kawunanmu yafi mu sanin abinda yafi zama alkhairi a rayuwarmu.
Wani lokacin mu kan nacewa abinda ba alkhairi bane a tattare damu shi kuma Allah sai ya barmu dashi domin hakan ya zame mana izina idan kuma muka laƙanci kuskurenmu muka koma masa sai kiga ya canza mana da abinda tun farko yake shine alkhairinmu amma muka guje masa.
Kina son Bilal kuma ni ba zance ki rabu dashi ba dukda ba zan miki ƙarya ba har raina zanyi fatan hakan amma kuma bamu ke da rayuwarmu ba ba kuma mu isa mu kaucewa ƙaddara ba dan haka addu'ar dai ita zakiyi ki kuma yi ƙoƙarin gyara tsakaninki da mahaifanki domin fushinsu ba ƙaramin masifa bane a tattare dake shi kaɗai ya isa ya hana addu'ar ki yin tasiri ki nemi yardarsu sai kiga komai yazo miki cikin sauƙi.
Abu ma ƙarshe da zan gaya miki shine koda Allah ya ƙaddara cigaban zaman ki da Bilal, dukda dai kin rigada kin yi gini da tubalin toka amma lokaci bai ƙure ba da zaki iya rush ginin nan ki faro shi da sabon foundation. Idan kin fahimci abinda bake nufi duk abinda zakiyi kiyi shi bisa gaskiya, aure ibadah ne ba wai soyayya ba Halima sannan a cikin biyayyar auren kanta zaki iya kai kanki wuta a maimakon Aljanna dan haka dole ku saka Allah ku kuma ɗora aurenku bisa doron shari'a domin samun dacewa".
Haka ta tafi ta barni cikin tunani, Tabbas na yarda da sakaci na gurin addu'a, ina ƙoƙarin kiyaye sallolina na farilla idan na idar kuma zanyi yan gajerun addu'oina shikenan bana ɗorawa da nafila. Tun ina gida Mama tayi iya ƙoƙarin ta gurin ɗora mu a hanya a duk sanda zata tashi cikin dare zata zo ta tashe ni wani lokacin nayi sallar ido cike da bacci wani lokacin data fita zan maida kai na kwanta, haka azumin litinin da Alhamis haka nan tun ina kirawa kaina ulcer ƙarya dan kar inyi har ta gaske ta kamani, a hakan ina lallaɓawa da kuma na koma hannun Bilal sai komai ya sake taɓarɓarewa domin dai shima baya ga sallah biyar ta farilla ban ce yana wata nafila ba haka azumi nasha in ce masa mu tashi da azumi ranar Alhamis ko Juma'a yaƙi wani lokacin ma ni zan ɗauka ƙarshe sai ya saka na karya shi. Kai ko sallah nayi na zauna ina doguwar addu'a muddin yana kusa sai ya san yanda ya tayar dani har cewa yakeyi wai idan mace tana doguwar addu'a da wuya ba ƙarar mijinta take kaiwa gurin Allah ba, da sakaci irin nawa da rashin ƙarfafawa dana samu daga gareshi duk ya sake taɓarɓara komai nawa ya zama sai a hankali.
Lissafina, rayuwata gaba ɗaya Bilal nez ko addu'ar zanyi shine, bani da wani buri a koda yaushe sai yanda zanyi na burge Bilal na samu soyayyar ta yanda bani da wata addu'a sai tasa ban kuma taɓa banbacewa ba domin zuciyata ta rigada ta amince shi ɗin shine alkhairi gashi kuma ubangiji ya mallaka mun shi sai dai kuma mallakar tasa bata zamemin komai ba face fitina domin duk wani abu mata kyau da zai sameni yana da nasaba da Bilal, a tarayyata dashi baki ɗaya zan iya cewa Al'amin da Sharifa su kaɗai ne abun ƙwarai da zan ɗaga nace na samu a silar Bilal bayaga haka sai tarin nadama da dana sani.
Kwana nayi ina saƙa da warwarar mataki na gaba, barin Bilal ko kuwa cigaba da zama dashi? Kamar yanda tace zaɓi na ne duk kuma abinda na ɗauka babu mai ce mun saboda me domin ni nasan daɗi na kuma san wahalar dake tattare da zama dashi amma kuma dole na tsaya nayi tunani mai kyau ko saboda goben yayana.
BILAL
[4/20, 12:27 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 38*
Madallah da mutane masu karamci. Nagode ƙwarai dagaske, ina lafiya wani aiki ne ya ɗauke ni tsayin kwanaki amma Alhamdulillah mun kammala na kuma gode ƙwarai da haƙurinku ina fatan har mu kammala babu wani uzuri da zai sake gifta mana 🙏🏽🙏🏽🙏🏽
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne 800, yake mai jira nayi posting ki fitar kiji tsoron Allah dakw da wacce take jira ki turo ta karanta a bati ku guji haƙƙin komai ƙanƙantarsa. Duk wacce ta shirya sauke nauyi ta tura mun kuɗi na a asususun 7061838488 Opay Maryam Farouk. Nagode*
BIlal
Tun barin sa gidansu Zulaiha komai ya sake jagule masa, tunanin sa ya tsaya kwata kwata ya kasa tantance mai ya kamata yayi. Batun ace ya haƙura da Zulaiha ma bai taso ba domin kuwa hakan ba mai yuwuwa bane ba amma bai taɓa zaton za'a masa titsiyen aurenta irin haka ba musamman a wannan lokacin da yake cikin tsaka mai wuya tsakanin sa da Halima. Tabbas yana son Halima tana kuma da matsayi na daban a zuciyarsa domin yasan halacci ya san kuma a zamanin yanzu samun mace da zata so shi tsakani da Allah irinta ta kuma kyautata masa da jikinta da aljihunta abu ne mai matuƙar wahala.
Kawai shima bai san dalilin da ya saka ya kasa kwatanta mata kyautatawar da take masa ba, yanzun kuma wannan abun daya gifta duk ya sake lalata komai tunda har kuma ta iya tafiya gida da kanta ya san tabbas ta kai ƙarshe ne dan haka zai bata lokaci domin ya san fushin ta ba zai ɗore ba ƙila ko bai bi ta bama idan ta sakko da kanta ita zata nemeshi kamar yanda suka saba fatansa kawai shine ta rufa masa asiri kada ta furta wani abu da zai jawo zubewar mutunchin sa a idon yan gidansu musamman Abbanta. Haka ya shirya ya tafi Abuja saboda Jalilah da take ta kiran sa har tana iƙirarin idan bai zo ba ita zata taho. Satinsa biyu acan a tsayin kwanakin da yayi kuma har ita kanta saida ta fahimci baya cikin nutsuwarsa.
"Bazan iya gayawa Mama ba Hansa'u"
"Anty Labiba fa?" Ta faɗa sai nayi saurin girgiza kai nace
"Gara kowa akanta". Murmushi tayi ta koma ta zauna ta dafa kafaɗata tace
"Ban sani ba ko har yanzu kina ɗaukata a irin matsayin da kike dashi a gurina". Nayi shiru ina kokawa da muryar Bilal dake nanata mun kaina zan tozarta idan na tona asirinsa. Da hannu biyu na toshe kunne na kafin na fizgo maganar da ƙarfi nace
"Matan banza yake bi Hansa'u" wannan maganar kuma tasa naji tamkar na buɗe wata ƙofa cikin zuciyata dan haka tiryan tiryan na shiga koro mata bayani tun daga aurena da Bilal duk wani abu da na haɗiye saida ya samu hanya ya fito da kansa na furtawa Hansa'u shi harda furucin da yayi akan Mama ban rage ba saida na amayar mata. Haka muka rungume juna ni kuka ita kuka babu mai rarrashin wani, mun daɗe a cikin yanayin kafin ta miƙe tana cewa
"Zanje na dawo Halima idan na zauna yanzu ina kallonki bazan samu ƙarfin guiwar ce miki komai ba zanje gida amma komai dare zan dawo". Ban ɗago na kalleta ba na ɗaga mata kai alamar "Toh".
Bayan tafiyar ta ji na ringayi kamar an kwashe mun wani ɓangare na jikina, tsabar yanda nauyin da ƙirji na yake mun ya ragu ina tsaka da kukan bacci ya kwashe ni dana farka kuma sai na ringa ji kamar bani ba, babu wannan abun da nake ji yana mun yawo tsakanin ƙirji da maƙogaro, haka na ƙarasa yinin ranar, har na fitar da rai da dawowar Hansa'u sai gata lokacin ƙarfe tara harta gota. Fuskarta duk ta tashi da alama bayan tafiyarta kuka ta cigaba dayi, a ɗaki muka sake ƙulewa, ta faɗa mun maganganu da sukayi tasiri sosai cikin ƙwaƙwalwata. Abu uku da na fi riƙewa cikin maganganunta tunatarwar da tayi mun akan addu'a.
"Halima tun ba yau ba na sani kina da sakaci gurin addu'a. Ki sani Allah yana fushi da bawan da baya roƙonsa. Ko da ace ubangiji ya hore maka komai a rayuwa ka kasance mai godiya a gareshi kuma ka cigaba da yi masa naci da roƙon ya taya ka tattala abinda ya baka ba kuma shikenan idan buƙatarka ta biya sai kuma sanda ka sake faɗawa cikin wata damuwar ne sannan zaka tuna da Allah ka sake roƙon sa ba shiyasa sai ya barmu da iyawarmu muga idan zamu iya yiwa kanmu.
Abu na farko da zaki fara shine ki gyara tsakaninki da mahaliccinki, kinga addu'a Halima tasirinta yawa ne dashi. Addu'a ta kan canza ƙaddara daga mummuna zuwa kyakkyawa, hatta da Bilal addu'a zata iya canza miki shu. Ubangiji yana son bawa mai naci da ƙasƙantar da kai akan buƙatar sa. Wani kuka ko ajiye abu a rai ba zai ƙareki da komai ba abinda yafi miki shine ki dage kiyita roƙon Allah karki gaji lokaci ya wuce da zamu kwanta muyita bacci da cewar ai komai daga Allah ne haka ne amma kuma ba zaka taɓa haɗa nasarar rayuwarka data wanda ya hana idonsa bacci ya roƙi ubangiji ba tamkar ka kwanta a ɗaki ne kana tsammanin ayi ruwan sama abinci ya faɗo ka ɗauka kaci ba tareda ka fita kayi aikin da zai samar maka da kuɗin da zaka siyi abincin ba.
Kada kuma ki ɗauka a sanda kika so a lokacin addu'ar ki zata karɓu ko kuma idan baki samu biyan buƙatar ki ba a lokacin kice kin dena Aa, shi Allah ba haka yake ba. Ubangiji yafi mu sanin kawunanmu yafi mu sanin abinda yafi zama alkhairi a rayuwarmu.
Wani lokacin mu kan nacewa abinda ba alkhairi bane a tattare damu shi kuma Allah sai ya barmu dashi domin hakan ya zame mana izina idan kuma muka laƙanci kuskurenmu muka koma masa sai kiga ya canza mana da abinda tun farko yake shine alkhairinmu amma muka guje masa.
Kina son Bilal kuma ni ba zance ki rabu dashi ba dukda ba zan miki ƙarya ba har raina zanyi fatan hakan amma kuma bamu ke da rayuwarmu ba ba kuma mu isa mu kaucewa ƙaddara ba dan haka addu'ar dai ita zakiyi ki kuma yi ƙoƙarin gyara tsakaninki da mahaifanki domin fushinsu ba ƙaramin masifa bane a tattare dake shi kaɗai ya isa ya hana addu'ar ki yin tasiri ki nemi yardarsu sai kiga komai yazo miki cikin sauƙi.
Abu ma ƙarshe da zan gaya miki shine koda Allah ya ƙaddara cigaban zaman ki da Bilal, dukda dai kin rigada kin yi gini da tubalin toka amma lokaci bai ƙure ba da zaki iya rush ginin nan ki faro shi da sabon foundation. Idan kin fahimci abinda bake nufi duk abinda zakiyi kiyi shi bisa gaskiya, aure ibadah ne ba wai soyayya ba Halima sannan a cikin biyayyar auren kanta zaki iya kai kanki wuta a maimakon Aljanna dan haka dole ku saka Allah ku kuma ɗora aurenku bisa doron shari'a domin samun dacewa".
Haka ta tafi ta barni cikin tunani, Tabbas na yarda da sakaci na gurin addu'a, ina ƙoƙarin kiyaye sallolina na farilla idan na idar kuma zanyi yan gajerun addu'oina shikenan bana ɗorawa da nafila. Tun ina gida Mama tayi iya ƙoƙarin ta gurin ɗora mu a hanya a duk sanda zata tashi cikin dare zata zo ta tashe ni wani lokacin nayi sallar ido cike da bacci wani lokacin data fita zan maida kai na kwanta, haka azumin litinin da Alhamis haka nan tun ina kirawa kaina ulcer ƙarya dan kar inyi har ta gaske ta kamani, a hakan ina lallaɓawa da kuma na koma hannun Bilal sai komai ya sake taɓarɓarewa domin dai shima baya ga sallah biyar ta farilla ban ce yana wata nafila ba haka azumi nasha in ce masa mu tashi da azumi ranar Alhamis ko Juma'a yaƙi wani lokacin ma ni zan ɗauka ƙarshe sai ya saka na karya shi. Kai ko sallah nayi na zauna ina doguwar addu'a muddin yana kusa sai ya san yanda ya tayar dani har cewa yakeyi wai idan mace tana doguwar addu'a da wuya ba ƙarar mijinta take kaiwa gurin Allah ba, da sakaci irin nawa da rashin ƙarfafawa dana samu daga gareshi duk ya sake taɓarɓara komai nawa ya zama sai a hankali.
Lissafina, rayuwata gaba ɗaya Bilal nez ko addu'ar zanyi shine, bani da wani buri a koda yaushe sai yanda zanyi na burge Bilal na samu soyayyar ta yanda bani da wata addu'a sai tasa ban kuma taɓa banbacewa ba domin zuciyata ta rigada ta amince shi ɗin shine alkhairi gashi kuma ubangiji ya mallaka mun shi sai dai kuma mallakar tasa bata zamemin komai ba face fitina domin duk wani abu mata kyau da zai sameni yana da nasaba da Bilal, a tarayyata dashi baki ɗaya zan iya cewa Al'amin da Sharifa su kaɗai ne abun ƙwarai da zan ɗaga nace na samu a silar Bilal bayaga haka sai tarin nadama da dana sani.
Kwana nayi ina saƙa da warwarar mataki na gaba, barin Bilal ko kuwa cigaba da zama dashi? Kamar yanda tace zaɓi na ne duk kuma abinda na ɗauka babu mai ce mun saboda me domin ni nasan daɗi na kuma san wahalar dake tattare da zama dashi amma kuma dole na tsaya nayi tunani mai kyau ko saboda goben yayana.
BILAL
[4/20, 12:27 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 38*
Madallah da mutane masu karamci. Nagode ƙwarai dagaske, ina lafiya wani aiki ne ya ɗauke ni tsayin kwanaki amma Alhamdulillah mun kammala na kuma gode ƙwarai da haƙurinku ina fatan har mu kammala babu wani uzuri da zai sake gifta mana 🙏🏽🙏🏽🙏🏽
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne 800, yake mai jira nayi posting ki fitar kiji tsoron Allah dakw da wacce take jira ki turo ta karanta a bati ku guji haƙƙin komai ƙanƙantarsa. Duk wacce ta shirya sauke nauyi ta tura mun kuɗi na a asususun 7061838488 Opay Maryam Farouk. Nagode*
BIlal
Tun barin sa gidansu Zulaiha komai ya sake jagule masa, tunanin sa ya tsaya kwata kwata ya kasa tantance mai ya kamata yayi. Batun ace ya haƙura da Zulaiha ma bai taso ba domin kuwa hakan ba mai yuwuwa bane ba amma bai taɓa zaton za'a masa titsiyen aurenta irin haka ba musamman a wannan lokacin da yake cikin tsaka mai wuya tsakanin sa da Halima. Tabbas yana son Halima tana kuma da matsayi na daban a zuciyarsa domin yasan halacci ya san kuma a zamanin yanzu samun mace da zata so shi tsakani da Allah irinta ta kuma kyautata masa da jikinta da aljihunta abu ne mai matuƙar wahala.
Kawai shima bai san dalilin da ya saka ya kasa kwatanta mata kyautatawar da take masa ba, yanzun kuma wannan abun daya gifta duk ya sake lalata komai tunda har kuma ta iya tafiya gida da kanta ya san tabbas ta kai ƙarshe ne dan haka zai bata lokaci domin ya san fushin ta ba zai ɗore ba ƙila ko bai bi ta bama idan ta sakko da kanta ita zata nemeshi kamar yanda suka saba fatansa kawai shine ta rufa masa asiri kada ta furta wani abu da zai jawo zubewar mutunchin sa a idon yan gidansu musamman Abbanta. Haka ya shirya ya tafi Abuja saboda Jalilah da take ta kiran sa har tana iƙirarin idan bai zo ba ita zata taho. Satinsa biyu acan a tsayin kwanakin da yayi kuma har ita kanta saida ta fahimci baya cikin nutsuwarsa.