Sashe 100
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muryar da take masa magana kaɗai a yan sakanni take hargitsa masa lissafi balle aje ga sauran lamura daga Haliman balle Zulaiha da take nan bagidajiya (a ganinsa 🤣🤣🤣) babu wacce ta kamo ƙafarta a iya kyau, iya kwalliya, gayu uwa uba kuma iya kula da namiji ta wannan fannin kam dole ma a karya mata ɗan kwali. Yana can zancen zuci ta ɗaga wayar tana ta Hello Hello harta gaji ta kashe ta kira ya zare wayar da sauri daga kunnensa saboda ƙara.
"Ina ka shige duk yau baka kirani ba" ta faɗa bayan daya amsa wayar. Kwanciya yayi akan gado ya kashe murya shima ya ce
"Kema baki kira ni ba"
"Yaushe muka fara haka? Idan ban kiraka ba kenan ba zaka kirani ba kake nufi?" Ta faɗa sai ya tashi zaune dan yaji sautin muryarta ba yanda ya zata ba ya kuma san halin kayarsa idan tana sama abu kaɗan zai tuzurata shi da yake so ya karɓi kuɗaɗe a hannunta kuma ina zai bari suyi faɗa?
Cikin kwantar da murya ya ce
"Ba haka nake nufi ba honey tsokanarki naso nayi ban san kuma baki cikin yanayi me daɗi ba, yanzu dai mai ya samu baby na?" Ya ƙarasa cikin sautin da ya san zai iya samun kanta. Tayi ƙaramin tsaki ta ce
"Ban san me yake damunka kwana biyu ba Bee kawai shiru nakeyi amma gaba ɗaya ka canza, kayi cancelling tafiyarka a die minute sannan kana sane yau ya kamata na tafi amma baka ko kirani ba balle kaji yaya nake ciki anya kuwa babu wani abu da kake ɓoye mun?"
Sai da yaji hanjin cikin sa ya kaɗa, duk ƙoƙarin da yakeyi na kada ya kuskure har ya bada ƙofar da zata zargi wani shiri ashe ya bar baya ba zani, da sauri ya ce
"Kiyi haƙuri Honey pot kin san na gaya miki yanda nake ciki da gurin aiki na gaba ɗaya sun taso ni a gaba gashi gida ma duk sai a hankali na gaya miki Halima ta tayar da rigima tunda taga chat ɗin mu yanzu haka ma kusan 1 week fa tana gidansu kin san mutanen mu kuma family kowa ya ɗora mun laifi ana ta cewa na fara wulaƙantata saboda zan kawo wata".
Tsaki ta sakeyi kafin tace
"Ta hutar da kanta ai sai ka aika mata da takardarta kawai dan dama ko bata tafi yanzu ba zata tafi idan na zo dan ka san dai ba zan zauna da kishiya ba"
"Amma Babe munyi maganar nan kin ce kin haƙura ke da ba gidan ku ɗaya ba dan Allah menene damuwar ki da ita kuma?" Ya faɗa kamar zai yi kuka, daga can tace
"Babu dole fa Bee, idan ita ka zaɓa sai kuyi zamanku ai ba cewa nayi ka saki matarka dole ka aureni ba. Ni dan Allah duk ba wannan ba kazo ka ɗauke ni, kawai sai yau Salis ya sake tura mun da flight ticket ɗin wai ashe ta Kano ya mun booking na zo kuma anyi shifting flight ɗin sai 8 na safe, duk raina a ɓace yake wlh kazo ka ɗauke ni na samu nayi wanka ko zan ɗan samu nutsuwa".
Idan da ya san dalilin kiran kenan da ba abinda zai zaka yabi bayan kiranta kai da kashe wayarsa ma zaiyi gaba ɗaya. A hankali ya ce
"Ayya sorry Babe shine baki kirani tun ɗazu ba kuma?"
"Ai gashi yanzu na kiraka dan Allah idan ba zaka zo ba na nemi taxi zaka cikani da surutunka da baya ƙarewa" ta faɗa a hasale. Kamar ya ce ta nemi taxi ɗin sai dai ya ce
"Toh mai zai hana ki kama lodge mana anan kawai tunda da safe ne kar kuma kiyi nisa sosai"
"Tun yaushe ka fara shirya mun abinda ya kamata nayi da wanda ba zanyi ba Bilal?" Ta faɗa kamar wata uwarsa, da sauri ya ce
"Kiyi haƙuri gani nan zuwa" tayi tsaki ta kashe wayar.
Tashi yayi ransa duk ba daɗi, kamar ya kirata yace ta hau taxi kawai sai dai kuma baya so ya ɓata rawarsa da tsalla gara dai su rabu lafiya idan buƙatarsa ta gama cika daga nan shima zai buɗe mata shafin nasa rashin mutunchin. Haka nan badan ya so ba ya kama hanyar Airport ɗin sha ɗaya harta gota bai yi nisa ba sai ga kiran Hafiz, sai da ya gangare gefen titi ya kashe motar kafin ya amsa cikin muryar bacci.
"Afuwan na tashe ka daga bacci" Hafiz ɗin ya faɗa, ya sake maƙale murya ya ce
"Ina zaune ne banma san baccin ya ɗauke ni ba". Daga can Hafiz ɗin ya ce
"Dama Jalilah ce ta shigo Kano, ka santa da hayyata ta kirani wai anyi shifting flight ɗin ta zuwa safiya in samo mata mai Taxi da na sani dare yayi tana jin tsoro ita bata san Kano sosai ba shine na kiraka ko zaka ma Abokinka me Uber ɗin nan magana idan bai tashi ba dan Allah yaje ya ɗauke ta ya sama mata hotel nan kusa da Airport ɗin".
"Wai Ammar? Ai ya samu aiki Lagos yana can kusan wata shida kenan ya dena Uber, amma bari akwai wani da ya ɗauke ni kwanaki nay saving number sa kuma ɗan nan kusa damu ne bari naji idan bai tashi ba ka tura mun number ta" cewar Bilal ɗin, yana aje wayar kuwa Hafiz ɗin ya turo masa number ya wani taɓe baki bayan daya kunna motar ya cigaba da tafiya. Rai ɓace ta zauna a motar bayan daya isa, haɗe fuska yayi shima yana kallonta ya ce
"Na ce miki ina hanya shine kuma kika wani kira Hafiz ya nemo miki Taxi ko?"
Harara ta balla masa tace
"Ai naga alamar wuyanka ya fara kauri ne har in ce kazo ka ɗauke ni ka ce wani na kwana a nan shiyasa na kirashi dan nasan ƙarshe kai ɗin dai zai turo ka ɗauke ni". Kallonta kawai yayi kafin ya ɗauke kai gefe yayi ƙwafa sannan ya ce
"Yanzu ina zan kaiki?"
"Gida na" ta bashi amsa tana danna kiran layin Hafiz. Fuzge wayar yayi da sauri ya katse kafin ya ce
"Me zaki gaya masa kuma?"
"Zan gaya masa kazo ne mana" ta bashi amsa tana karɓar wayar, ya zare ido ya ce
"Kinyi hauka amma? Karfe sha biyun zaki ce masa nazo ɗaukar ki me kike so yayi tunani?"
"Oho" ta bashi amsa kafin ya sake magana yaji muryar Hafiz ɗin a speaker yana cewa
"Jalilah sa'arki ɗaya matata bata gari amma ko dan gaba kada ki sake mun irin haka ya zaki ringa kirana tsakiyar dare?"
"Allah ya baka haƙuri dama ce maka zanyi me Taxi ɗin ya zo"
"Shikenan mu kwana lafiya ki kula da kanki" ya bata amsa bai jira tace wani abu ba ya katse kiran.
Bilal dake kallonta ya sauke ajiyar zuciya jin bata ambaci sunansa ba can cikin ransa kuma kishi ne ya taso masa jin yanda take yiwa Hafiz ɗin magana a nutse cikin ladabi kamar me tsoron sa shi kuma yana wani bata amsa a tsaye, ɗauke kai yayi ganin ta juyo ta kalle shi ta ɗan yi murmushi ta ce
"Akan Hafiz har Malamai na shiga amma shegen guy ɗin nan yanda kasan aljani na kasa samunsa"
"Bafa zan ɗauki wannan wulaƙancin ba ta yaya a gabana zaki ringa gaya mun kina son wani daban a hakan kike so na aureki?" Ya taso mata, wani shegen kallo ta masa tace
"In aureka dai, ai nice mijin kaine matar ko kai a haka da kake kana zaton ka isa ka aureni?
Banda ma so banzan abu ne Bee ai ka san ni ba tsararka bace ko shi ubangidan naka nafi ƙarfinsa kawai dai zuciya da baka da iko da ita tayi ta kwaso maka tarkace tana saka ka son su" ta ƙarasa tana soka earpiece a kunneta. Ya kusa minti biyar yana kallonta yama rasa mai zaiyi ko mai zaice, tunda yake ba'a taɓa masa zagi irin wanan ba, wato shine tarkace? Lallai Jalilah taga gadon baccin sa.
Haɗiye zuciya yayi ya tada motar, sai da suka fita daga Airport ɗin kafin a ƙufule ya sake tambayarta in da zai kaita
"Nace maka gidana ko kunnuwanka sun toshe ne kuma baka ji da kyau?" Ta bashi amsa, wlh ba dan ba sai ya gaggaya mata maganganu kuma ta fice masa a mota amma kuma yanzun dai bai isa ba amma lokaci na zuwa, daya tuna abinda ya shuka dole ya sauke fushi ya gyara murya ya ce
"Kin manta ana aiki a gidan ne?"
"Aikin da akeyi a waje meya shafi ciki kuma ina kace an gama fentin cikin tun last week?" Ta tambaya tana tsare shi da ido, titi ya mayar da idonsa kafin ya ce
"An gama amma ai kin san an kwashe kayan ni kuma da naji kince sababbi za'a zuba shiyasa ba'a mayar ba dan wasu abubuwan ma na kyautar dasu"
"Su kuma kayana ka kaimun su ina?" Ta faɗa tana tsare shi da ido, kashe mata ido ɗaya yayi ya ce
"Na kaiwa Matata ta ringa sakawa kinga se na ringa ganinta kamar ke"
"Har ta mutu ba zatayi kyauna ba" ta faɗa tana juya ido, ya ruƙo hannunta yace
"Ni shaida ne yar balarabiyata, yanzu dai ina zamuje kinga idanuwanki sun nuna a gajiye kike ki samu ki huta kar kiyi missing flight kuma goben"
"Muje gidanka toh tunda kace can babu gurin kwanciya" ta faɗa tana kallonsa.
"Gida na kuma?" Ya faɗa da sauri har yana sakin stirring, ta taɓe baki tace
"Eh mana ko ba zaka kaini ba?"
"Zan so in kaiki mana amma kin manta na gaya miki matar gidan bata nan kuma kinga dai unguwarmu ba kamar in da can gidan yake bane akwai yan sa ido yanzu a ganni na shiga gida da Mace ai na shiga uku a garin nan bama unguwar ba"
"Ina ka shige duk yau baka kirani ba" ta faɗa bayan daya amsa wayar. Kwanciya yayi akan gado ya kashe murya shima ya ce
"Kema baki kira ni ba"
"Yaushe muka fara haka? Idan ban kiraka ba kenan ba zaka kirani ba kake nufi?" Ta faɗa sai ya tashi zaune dan yaji sautin muryarta ba yanda ya zata ba ya kuma san halin kayarsa idan tana sama abu kaɗan zai tuzurata shi da yake so ya karɓi kuɗaɗe a hannunta kuma ina zai bari suyi faɗa?
Cikin kwantar da murya ya ce
"Ba haka nake nufi ba honey tsokanarki naso nayi ban san kuma baki cikin yanayi me daɗi ba, yanzu dai mai ya samu baby na?" Ya ƙarasa cikin sautin da ya san zai iya samun kanta. Tayi ƙaramin tsaki ta ce
"Ban san me yake damunka kwana biyu ba Bee kawai shiru nakeyi amma gaba ɗaya ka canza, kayi cancelling tafiyarka a die minute sannan kana sane yau ya kamata na tafi amma baka ko kirani ba balle kaji yaya nake ciki anya kuwa babu wani abu da kake ɓoye mun?"
Sai da yaji hanjin cikin sa ya kaɗa, duk ƙoƙarin da yakeyi na kada ya kuskure har ya bada ƙofar da zata zargi wani shiri ashe ya bar baya ba zani, da sauri ya ce
"Kiyi haƙuri Honey pot kin san na gaya miki yanda nake ciki da gurin aiki na gaba ɗaya sun taso ni a gaba gashi gida ma duk sai a hankali na gaya miki Halima ta tayar da rigima tunda taga chat ɗin mu yanzu haka ma kusan 1 week fa tana gidansu kin san mutanen mu kuma family kowa ya ɗora mun laifi ana ta cewa na fara wulaƙantata saboda zan kawo wata".
Tsaki ta sakeyi kafin tace
"Ta hutar da kanta ai sai ka aika mata da takardarta kawai dan dama ko bata tafi yanzu ba zata tafi idan na zo dan ka san dai ba zan zauna da kishiya ba"
"Amma Babe munyi maganar nan kin ce kin haƙura ke da ba gidan ku ɗaya ba dan Allah menene damuwar ki da ita kuma?" Ya faɗa kamar zai yi kuka, daga can tace
"Babu dole fa Bee, idan ita ka zaɓa sai kuyi zamanku ai ba cewa nayi ka saki matarka dole ka aureni ba. Ni dan Allah duk ba wannan ba kazo ka ɗauke ni, kawai sai yau Salis ya sake tura mun da flight ticket ɗin wai ashe ta Kano ya mun booking na zo kuma anyi shifting flight ɗin sai 8 na safe, duk raina a ɓace yake wlh kazo ka ɗauke ni na samu nayi wanka ko zan ɗan samu nutsuwa".
Idan da ya san dalilin kiran kenan da ba abinda zai zaka yabi bayan kiranta kai da kashe wayarsa ma zaiyi gaba ɗaya. A hankali ya ce
"Ayya sorry Babe shine baki kirani tun ɗazu ba kuma?"
"Ai gashi yanzu na kiraka dan Allah idan ba zaka zo ba na nemi taxi zaka cikani da surutunka da baya ƙarewa" ta faɗa a hasale. Kamar ya ce ta nemi taxi ɗin sai dai ya ce
"Toh mai zai hana ki kama lodge mana anan kawai tunda da safe ne kar kuma kiyi nisa sosai"
"Tun yaushe ka fara shirya mun abinda ya kamata nayi da wanda ba zanyi ba Bilal?" Ta faɗa kamar wata uwarsa, da sauri ya ce
"Kiyi haƙuri gani nan zuwa" tayi tsaki ta kashe wayar.
Tashi yayi ransa duk ba daɗi, kamar ya kirata yace ta hau taxi kawai sai dai kuma baya so ya ɓata rawarsa da tsalla gara dai su rabu lafiya idan buƙatarsa ta gama cika daga nan shima zai buɗe mata shafin nasa rashin mutunchin. Haka nan badan ya so ba ya kama hanyar Airport ɗin sha ɗaya harta gota bai yi nisa ba sai ga kiran Hafiz, sai da ya gangare gefen titi ya kashe motar kafin ya amsa cikin muryar bacci.
"Afuwan na tashe ka daga bacci" Hafiz ɗin ya faɗa, ya sake maƙale murya ya ce
"Ina zaune ne banma san baccin ya ɗauke ni ba". Daga can Hafiz ɗin ya ce
"Dama Jalilah ce ta shigo Kano, ka santa da hayyata ta kirani wai anyi shifting flight ɗin ta zuwa safiya in samo mata mai Taxi da na sani dare yayi tana jin tsoro ita bata san Kano sosai ba shine na kiraka ko zaka ma Abokinka me Uber ɗin nan magana idan bai tashi ba dan Allah yaje ya ɗauke ta ya sama mata hotel nan kusa da Airport ɗin".
"Wai Ammar? Ai ya samu aiki Lagos yana can kusan wata shida kenan ya dena Uber, amma bari akwai wani da ya ɗauke ni kwanaki nay saving number sa kuma ɗan nan kusa damu ne bari naji idan bai tashi ba ka tura mun number ta" cewar Bilal ɗin, yana aje wayar kuwa Hafiz ɗin ya turo masa number ya wani taɓe baki bayan daya kunna motar ya cigaba da tafiya. Rai ɓace ta zauna a motar bayan daya isa, haɗe fuska yayi shima yana kallonta ya ce
"Na ce miki ina hanya shine kuma kika wani kira Hafiz ya nemo miki Taxi ko?"
Harara ta balla masa tace
"Ai naga alamar wuyanka ya fara kauri ne har in ce kazo ka ɗauke ni ka ce wani na kwana a nan shiyasa na kirashi dan nasan ƙarshe kai ɗin dai zai turo ka ɗauke ni". Kallonta kawai yayi kafin ya ɗauke kai gefe yayi ƙwafa sannan ya ce
"Yanzu ina zan kaiki?"
"Gida na" ta bashi amsa tana danna kiran layin Hafiz. Fuzge wayar yayi da sauri ya katse kafin ya ce
"Me zaki gaya masa kuma?"
"Zan gaya masa kazo ne mana" ta bashi amsa tana karɓar wayar, ya zare ido ya ce
"Kinyi hauka amma? Karfe sha biyun zaki ce masa nazo ɗaukar ki me kike so yayi tunani?"
"Oho" ta bashi amsa kafin ya sake magana yaji muryar Hafiz ɗin a speaker yana cewa
"Jalilah sa'arki ɗaya matata bata gari amma ko dan gaba kada ki sake mun irin haka ya zaki ringa kirana tsakiyar dare?"
"Allah ya baka haƙuri dama ce maka zanyi me Taxi ɗin ya zo"
"Shikenan mu kwana lafiya ki kula da kanki" ya bata amsa bai jira tace wani abu ba ya katse kiran.
Bilal dake kallonta ya sauke ajiyar zuciya jin bata ambaci sunansa ba can cikin ransa kuma kishi ne ya taso masa jin yanda take yiwa Hafiz ɗin magana a nutse cikin ladabi kamar me tsoron sa shi kuma yana wani bata amsa a tsaye, ɗauke kai yayi ganin ta juyo ta kalle shi ta ɗan yi murmushi ta ce
"Akan Hafiz har Malamai na shiga amma shegen guy ɗin nan yanda kasan aljani na kasa samunsa"
"Bafa zan ɗauki wannan wulaƙancin ba ta yaya a gabana zaki ringa gaya mun kina son wani daban a hakan kike so na aureki?" Ya taso mata, wani shegen kallo ta masa tace
"In aureka dai, ai nice mijin kaine matar ko kai a haka da kake kana zaton ka isa ka aureni?
Banda ma so banzan abu ne Bee ai ka san ni ba tsararka bace ko shi ubangidan naka nafi ƙarfinsa kawai dai zuciya da baka da iko da ita tayi ta kwaso maka tarkace tana saka ka son su" ta ƙarasa tana soka earpiece a kunneta. Ya kusa minti biyar yana kallonta yama rasa mai zaiyi ko mai zaice, tunda yake ba'a taɓa masa zagi irin wanan ba, wato shine tarkace? Lallai Jalilah taga gadon baccin sa.
Haɗiye zuciya yayi ya tada motar, sai da suka fita daga Airport ɗin kafin a ƙufule ya sake tambayarta in da zai kaita
"Nace maka gidana ko kunnuwanka sun toshe ne kuma baka ji da kyau?" Ta bashi amsa, wlh ba dan ba sai ya gaggaya mata maganganu kuma ta fice masa a mota amma kuma yanzun dai bai isa ba amma lokaci na zuwa, daya tuna abinda ya shuka dole ya sauke fushi ya gyara murya ya ce
"Kin manta ana aiki a gidan ne?"
"Aikin da akeyi a waje meya shafi ciki kuma ina kace an gama fentin cikin tun last week?" Ta tambaya tana tsare shi da ido, titi ya mayar da idonsa kafin ya ce
"An gama amma ai kin san an kwashe kayan ni kuma da naji kince sababbi za'a zuba shiyasa ba'a mayar ba dan wasu abubuwan ma na kyautar dasu"
"Su kuma kayana ka kaimun su ina?" Ta faɗa tana tsare shi da ido, kashe mata ido ɗaya yayi ya ce
"Na kaiwa Matata ta ringa sakawa kinga se na ringa ganinta kamar ke"
"Har ta mutu ba zatayi kyauna ba" ta faɗa tana juya ido, ya ruƙo hannunta yace
"Ni shaida ne yar balarabiyata, yanzu dai ina zamuje kinga idanuwanki sun nuna a gajiye kike ki samu ki huta kar kiyi missing flight kuma goben"
"Muje gidanka toh tunda kace can babu gurin kwanciya" ta faɗa tana kallonsa.
"Gida na kuma?" Ya faɗa da sauri har yana sakin stirring, ta taɓe baki tace
"Eh mana ko ba zaka kaini ba?"
"Zan so in kaiki mana amma kin manta na gaya miki matar gidan bata nan kuma kinga dai unguwarmu ba kamar in da can gidan yake bane akwai yan sa ido yanzu a ganni na shiga gida da Mace ai na shiga uku a garin nan bama unguwar ba"