Sashe 105
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin gidan ya koma bayan yace ta tafi zai zo kafin ya mayar da ƙofar ya rufe Wallet ɗin sa ya ɗauka da key ɗin mota, sai da ya leƙa Jalilah dake bacci kamar a gadon Mamanta kafin ya fita daga gida bai ɗauki motar ba ma gudun kar ƙarar ta ta tashi Jalilar.
A baki titi ya tarar da Fadila tana jiran abin hawa fuskar nan da ta sha mai tayi jajir saboda rana shi sai lokacin ma ya lura, cikin sa'a yana zuwa suka samu Adaidaita. Bayan ya zauna ya kunna wayarsa tamkar Zulaiha na jira kuwa ko gama kamawa batayi ba kiranta ya shigo.
Ya ɗaga, mita ta dasa masa akan katse wayar da sukeyi ɗazu da yayi kuma ya kashe gaba ɗaya daya sake kira bata same shi ba ya bata haƙuri kafin ta faɗa masa ainihin dalilin kiran wai taji shiru cikon kuɗi.
"Ina ganin 2m da yawa sai da muka shiga kasuwa sai kaga yan kayan da muka siyo da ita. Ni wlh da na san haka ne gara ka haɗa mun lefena da kanka na san sai ka fi sakin jiki ka zuba mun kaya masu kyau da tsada" ta faɗa cikin shagwaɓa.
Mamakin maganarta ya kamashi amma dai bai nuna ba ya ce zai aika mata da saƙon kawai saboda Fadila data baza kunnuwa dukda tayi kamar bata sauraronsa amma yasan hankalinta yana kansa. Suna sauka daga Adaidaitan kiran Jalilah ya shigo wayarsa, sai da gaban sa ya faɗi dan bai zaci zata farka da wuri ba.
Waje ya tsaya ya amsa, cike da izza da kuma muryar bacci kamar wata uwarsa ta ce
"Ina ka tafi?"
"Na ɗan fita ne daga nan zan biya na siyo miki lunch" ya bata amsa, shiru tayi kamar na zata sake magana ba kafin ta ce
"Karka zauna, Chinese rice nake so da grilled chicken kuma ka san ta inda nake so"
"Na sani ranki ya daɗe ai dama can zan je" ya faɗa cikin lallashi, tayi gajeran tsaki kafin ta kashe wayar. Ajiyar zuciya ya sauke a ransa yana ayyana kalar rashin mutunchin da zai mata daga sanda ya kammala shirinsa akanta.
Tun da ya ga takalma da yawa a ƙofar ɗakin Hajjan hankalinsa ya sake tashi amma haka ya daure ya shiga da sallama, gaba ɗaya yayan ɗakin su su shidda shi na bakwai suna zaune sai kuma Hajja. Idanuwa suka zuba masa kamar sunga bakuwar halitta hakan ya sake jefa shi cikin tashin hankali amma yayi namijin ƙoƙari gurin ɓoye firgicinsa ya samu guri can nesa ya zauna kai a ƙasa saboda harar da Hajja take aika masa.
Daƙyar ya buɗe baki ya fara gaisar da Hajjan ta dakatar da shi tana cewa
"Ni na isa? Riƙe gaisuwarka yau kwananka nawa rabon da ka tako gidan nan balle ka kira ni a su wa Bilal?"
Ƙasa ya sakeyi da kai bugun da zuciyarsa take yi kuma ya ragu dan ya ɗan samu nutsuwa daga maganar Hajjan ya fahimci wani abun daban ya saka ta kirashi ba wanda yake tunani ba. Anty Amina ce ta ce
"Amma dai koma menene tunda ya gaishe shi da kin amsa Hajja" ai kuwa ta taso mata tana cewa
"Ba zan amsa ba uwata Amina na ce bazan amsa ba idan ya so ki tsine mun in bi duniya saboda ban amsa gaisuwar Bilal ba"
"Allah ya baki haƙuri" Aminar ta faɗa tana gyara zama, Hajja tayi ƙwafa ta ce
"Ba tareda ɓata lokaci ba zan gabatar da abinda ya saka na taraku, ba kuma wani abu bane illah ku zame mana shaida tsakani na da Bilal". Da sauri ya ɗaga kai ya kalleta cikin rashin sanin mai yayi mata da har zata kawo shaidu kuma?
Ta zaro takarda da biro daga saƙon kujerar da take zaune ta jefa masa tana cewa
"Gashi nan ka rubuta komai da zan faɗa maka". Gabansa ne ya yanke ya faɗi, tsakanin Halima da Zulaiha gaskiya babu wacce zai iya saki a yanzu idan ma abinda Hajjan take buƙata kenan sai dai tayi haƙuri.
"Na ɗauki cikinka tsayin wata goma dan sai da ka haura wata tara a ciki na ka samu guri ka bararraje. Duk yayan dana haifa babu wanda na sha wahalar laulayi da naƙudar haihuwarsa kamar kai. Faɗar hidimar da nayi ta sunanka kuwa ɓata lokaci ne saboda akanka na fara haifar ɗa namiji. Tun da ka fara taka ƙafarka ban huta saboda jaye jayen jidali, ka shiga ɗakin Saude kayi mata ɓarna haka zata yi ta surfa bala'i tana mun gori banida kayan jere irin nata shiyasa nake turaka san ka lalata mata.
Sai da na daina gaisawa da kowa a unguwar nan saboda kai dan baka da aiki sai neman tsokanar yara a unguwa ko a makaranta kai ko kallon banza yaro ya maka ka faɗa mun har gaban uwarsa nake takawa naje na rama maka balle kuma mutum ya taɓa ka" ta fyace majina tana cewa
"Ai na san Amina da Ladi ba ku manta ba har a cell ɗin yan sanda sai da na taɓa kwana saboda Bilal, kaje ka daki wani yaro ashe Babansa ɗansanda ne suka zo zasu tafi da kai na hana ƙarshe ni suka tafi dani. Ban huta da jidalinka ba saida ka tafi Jami'a. Duk wani tanadi na da abinda nake dashi sai da ya ƙare akanka bayan rasuwar mahaifinku saboda yanda ka ɗauki rayuwar jin daɗi da ƙyale ƙyale, daga sanda ka gama makaranta ka samu aikinyi a maimakon ni da na sha wahalar ka ace ni zan mori samunka sai labari ya sha banban" ta ƙarasa tana fashewa da kuka kamar wacce aka daka.
Kallonta ya ringayi cikin rashin fahimta kafin ya juya yana kallon sauran yan uwansa kowanne da kalar yanayin da fuskarsa take ciki. A kan Hajja ya tsaida idonsa ganin yanda take kuka hankalinsa ya sake tashi, shi sam bai fahimci in da waɗannan maganganun suka dosa ba kuma ta yaya ma Hajja zata ce wai bata morar samun sa tsakani da Allah?
"Dan Allah Hajja kiyi haƙuri kiyi mun magana da yaren da fahimta duk mai ya kawo waɗannan maganganun har kina kuka haka?" Ya faɗa yana matsawa gabanta. Ta fyace hanci da gefen ɗankwalinta kafin ta ce
"Tun ina yar shekara goma sha huɗu aka saka mun lalle da ubanku kuma wannan ɗakin cikinsa aka kawo ni yau shekarata arba'in da biyar kenan a cikin har ubanku ya mutu aka raba gado a nan ɗin dai nake zaune kuma ginin shine tun na usuli babu abinda aka canza sai yan toshe toshe da manne manne da akayi,
Ina zaune anan ɗin nan ace ɗan da na haifa na sha wahalar sa ya tafi can duniya ya samu wata uwar da yan uwan daban yana bauta musu har ka siya musu gida kuma kai kake riƙe da su kan jiki kan ƙarfi, nan da Fadila da Abubakar suka gama sakandire zasu tafi Jami'a cewa kayi sai sai ɗaya daga cikinsu ya haƙura dan ba zaka iya ɗaukar nauyin su duka biyun ba amma can ba dangin iya ba na Baba a duniya ka ɗauki nauyinsu har gaban abinda ya fi Jami'a ma to wlh cikin biyu dole ayi ɗaya, ko dai ka saketa ko kuma daga yau ka nemi wata wacce zaka ringa kira da uwarka amma ba ni ba" ta sake rushewa da kuka.
Ƙasa ya sauke kai, shi kam yau tazo masa ba'a yadda ya tsammata ba wane irin bala'i ne haka wani na bin wani?
Yana ji Anty Habiba tayi caraf ta ce
"Ai wlh tallahi Hajja ba dan Bilal yana kama da mu ba ni zan ce canza miki shi akayi a Asibiti ba ɗanki bane. Ai ko ɗan ruƙo ba zai yi abinda Bilal yayi ba caɓ" ta kyaɓe baki tana rufe baki Anty Ladi da Hadiza ma suka ɗauka. Fadila ce ta ce
"Taɓ, to ai baki ji komai ba ma Hajja yanzu haka in kinji miliyoyin kuɗin ya basu wai kuɗin lefe sai kun riƙe baki a haka ma kiransa take wai na zai isa ba ya ƙara musu" su ukun suka haɗa baki suna cewa
"Kinji ko, ai wlh ba haka suka barshi ba. Ba'a fita daga masifar Halima ba shine zai sake jajubo mana wata"
"Ku dai ba zaku taɓa iya zama ku tashi ba tareda kun sako Halima a ciki ba? Yanzu kuma menene nata a maganar da kukeyi?" Anty Amina da bata tsoma musu baki ba sai yanzun ta faɗa. Hajja ta ce
"Ai duk ita ce silar komai, tunda ya auri yarinyar nan kamar wanda aka sakawa hannu shikenan al'amuransa suka taɓarɓare ni dai aurenta babu abinda ya tsinana mun idan ba ɓacin rai da baƙin ciki ba, wannan auren da yayi ai da saninta amma da yake muguwa ce mai baƙar zuciya taja bakinta tayi gum idan da ta faɗa mun tun farko ta ina zan bari haka ta faru?"
"Yanzun ma ai bata ɓaci ba Hajja yanda kikace dole ya saketa in dai yana so yaga haske a rayuwarsa. Matar da tun babu aure yake musu wannan uwar hidimar idan ta tare kuma ai wlh janye shi zatayi ba zaki sake ganinsa ba.
Ta bakin naki mugunta ta saka Halima yin shiru bata faɗa ba tunda ai ba zata ce bata san duk tsayin lokacin nan mijinta na tareda wata ba shine saboda tsabar munafunci ta bar gidan ai in sha Allahu itama ta tafi kenan itama wannan kuma ka sallameta ga mace har mace irin arziƙi na binka soko ka tsaya kana bin wanda ba zasu tsinana maka komai ba" cewar Anty Habiba.
Sai lokacin Abubakar da yayi kamar baya gurin ya ce
"Wlh tallahi ku kuka da kanku sanda haƙƙin Anty Halima zai tambayeku amma duk ba laifin kowa bane laifinki ne Hajja saboda a gidan nan yanda kika dama haka ake sha.
A baki titi ya tarar da Fadila tana jiran abin hawa fuskar nan da ta sha mai tayi jajir saboda rana shi sai lokacin ma ya lura, cikin sa'a yana zuwa suka samu Adaidaita. Bayan ya zauna ya kunna wayarsa tamkar Zulaiha na jira kuwa ko gama kamawa batayi ba kiranta ya shigo.
Ya ɗaga, mita ta dasa masa akan katse wayar da sukeyi ɗazu da yayi kuma ya kashe gaba ɗaya daya sake kira bata same shi ba ya bata haƙuri kafin ta faɗa masa ainihin dalilin kiran wai taji shiru cikon kuɗi.
"Ina ganin 2m da yawa sai da muka shiga kasuwa sai kaga yan kayan da muka siyo da ita. Ni wlh da na san haka ne gara ka haɗa mun lefena da kanka na san sai ka fi sakin jiki ka zuba mun kaya masu kyau da tsada" ta faɗa cikin shagwaɓa.
Mamakin maganarta ya kamashi amma dai bai nuna ba ya ce zai aika mata da saƙon kawai saboda Fadila data baza kunnuwa dukda tayi kamar bata sauraronsa amma yasan hankalinta yana kansa. Suna sauka daga Adaidaitan kiran Jalilah ya shigo wayarsa, sai da gaban sa ya faɗi dan bai zaci zata farka da wuri ba.
Waje ya tsaya ya amsa, cike da izza da kuma muryar bacci kamar wata uwarsa ta ce
"Ina ka tafi?"
"Na ɗan fita ne daga nan zan biya na siyo miki lunch" ya bata amsa, shiru tayi kamar na zata sake magana ba kafin ta ce
"Karka zauna, Chinese rice nake so da grilled chicken kuma ka san ta inda nake so"
"Na sani ranki ya daɗe ai dama can zan je" ya faɗa cikin lallashi, tayi gajeran tsaki kafin ta kashe wayar. Ajiyar zuciya ya sauke a ransa yana ayyana kalar rashin mutunchin da zai mata daga sanda ya kammala shirinsa akanta.
Tun da ya ga takalma da yawa a ƙofar ɗakin Hajjan hankalinsa ya sake tashi amma haka ya daure ya shiga da sallama, gaba ɗaya yayan ɗakin su su shidda shi na bakwai suna zaune sai kuma Hajja. Idanuwa suka zuba masa kamar sunga bakuwar halitta hakan ya sake jefa shi cikin tashin hankali amma yayi namijin ƙoƙari gurin ɓoye firgicinsa ya samu guri can nesa ya zauna kai a ƙasa saboda harar da Hajja take aika masa.
Daƙyar ya buɗe baki ya fara gaisar da Hajjan ta dakatar da shi tana cewa
"Ni na isa? Riƙe gaisuwarka yau kwananka nawa rabon da ka tako gidan nan balle ka kira ni a su wa Bilal?"
Ƙasa ya sakeyi da kai bugun da zuciyarsa take yi kuma ya ragu dan ya ɗan samu nutsuwa daga maganar Hajjan ya fahimci wani abun daban ya saka ta kirashi ba wanda yake tunani ba. Anty Amina ce ta ce
"Amma dai koma menene tunda ya gaishe shi da kin amsa Hajja" ai kuwa ta taso mata tana cewa
"Ba zan amsa ba uwata Amina na ce bazan amsa ba idan ya so ki tsine mun in bi duniya saboda ban amsa gaisuwar Bilal ba"
"Allah ya baki haƙuri" Aminar ta faɗa tana gyara zama, Hajja tayi ƙwafa ta ce
"Ba tareda ɓata lokaci ba zan gabatar da abinda ya saka na taraku, ba kuma wani abu bane illah ku zame mana shaida tsakani na da Bilal". Da sauri ya ɗaga kai ya kalleta cikin rashin sanin mai yayi mata da har zata kawo shaidu kuma?
Ta zaro takarda da biro daga saƙon kujerar da take zaune ta jefa masa tana cewa
"Gashi nan ka rubuta komai da zan faɗa maka". Gabansa ne ya yanke ya faɗi, tsakanin Halima da Zulaiha gaskiya babu wacce zai iya saki a yanzu idan ma abinda Hajjan take buƙata kenan sai dai tayi haƙuri.
"Na ɗauki cikinka tsayin wata goma dan sai da ka haura wata tara a ciki na ka samu guri ka bararraje. Duk yayan dana haifa babu wanda na sha wahalar laulayi da naƙudar haihuwarsa kamar kai. Faɗar hidimar da nayi ta sunanka kuwa ɓata lokaci ne saboda akanka na fara haifar ɗa namiji. Tun da ka fara taka ƙafarka ban huta saboda jaye jayen jidali, ka shiga ɗakin Saude kayi mata ɓarna haka zata yi ta surfa bala'i tana mun gori banida kayan jere irin nata shiyasa nake turaka san ka lalata mata.
Sai da na daina gaisawa da kowa a unguwar nan saboda kai dan baka da aiki sai neman tsokanar yara a unguwa ko a makaranta kai ko kallon banza yaro ya maka ka faɗa mun har gaban uwarsa nake takawa naje na rama maka balle kuma mutum ya taɓa ka" ta fyace majina tana cewa
"Ai na san Amina da Ladi ba ku manta ba har a cell ɗin yan sanda sai da na taɓa kwana saboda Bilal, kaje ka daki wani yaro ashe Babansa ɗansanda ne suka zo zasu tafi da kai na hana ƙarshe ni suka tafi dani. Ban huta da jidalinka ba saida ka tafi Jami'a. Duk wani tanadi na da abinda nake dashi sai da ya ƙare akanka bayan rasuwar mahaifinku saboda yanda ka ɗauki rayuwar jin daɗi da ƙyale ƙyale, daga sanda ka gama makaranta ka samu aikinyi a maimakon ni da na sha wahalar ka ace ni zan mori samunka sai labari ya sha banban" ta ƙarasa tana fashewa da kuka kamar wacce aka daka.
Kallonta ya ringayi cikin rashin fahimta kafin ya juya yana kallon sauran yan uwansa kowanne da kalar yanayin da fuskarsa take ciki. A kan Hajja ya tsaida idonsa ganin yanda take kuka hankalinsa ya sake tashi, shi sam bai fahimci in da waɗannan maganganun suka dosa ba kuma ta yaya ma Hajja zata ce wai bata morar samun sa tsakani da Allah?
"Dan Allah Hajja kiyi haƙuri kiyi mun magana da yaren da fahimta duk mai ya kawo waɗannan maganganun har kina kuka haka?" Ya faɗa yana matsawa gabanta. Ta fyace hanci da gefen ɗankwalinta kafin ta ce
"Tun ina yar shekara goma sha huɗu aka saka mun lalle da ubanku kuma wannan ɗakin cikinsa aka kawo ni yau shekarata arba'in da biyar kenan a cikin har ubanku ya mutu aka raba gado a nan ɗin dai nake zaune kuma ginin shine tun na usuli babu abinda aka canza sai yan toshe toshe da manne manne da akayi,
Ina zaune anan ɗin nan ace ɗan da na haifa na sha wahalar sa ya tafi can duniya ya samu wata uwar da yan uwan daban yana bauta musu har ka siya musu gida kuma kai kake riƙe da su kan jiki kan ƙarfi, nan da Fadila da Abubakar suka gama sakandire zasu tafi Jami'a cewa kayi sai sai ɗaya daga cikinsu ya haƙura dan ba zaka iya ɗaukar nauyin su duka biyun ba amma can ba dangin iya ba na Baba a duniya ka ɗauki nauyinsu har gaban abinda ya fi Jami'a ma to wlh cikin biyu dole ayi ɗaya, ko dai ka saketa ko kuma daga yau ka nemi wata wacce zaka ringa kira da uwarka amma ba ni ba" ta sake rushewa da kuka.
Ƙasa ya sauke kai, shi kam yau tazo masa ba'a yadda ya tsammata ba wane irin bala'i ne haka wani na bin wani?
Yana ji Anty Habiba tayi caraf ta ce
"Ai wlh tallahi Hajja ba dan Bilal yana kama da mu ba ni zan ce canza miki shi akayi a Asibiti ba ɗanki bane. Ai ko ɗan ruƙo ba zai yi abinda Bilal yayi ba caɓ" ta kyaɓe baki tana rufe baki Anty Ladi da Hadiza ma suka ɗauka. Fadila ce ta ce
"Taɓ, to ai baki ji komai ba ma Hajja yanzu haka in kinji miliyoyin kuɗin ya basu wai kuɗin lefe sai kun riƙe baki a haka ma kiransa take wai na zai isa ba ya ƙara musu" su ukun suka haɗa baki suna cewa
"Kinji ko, ai wlh ba haka suka barshi ba. Ba'a fita daga masifar Halima ba shine zai sake jajubo mana wata"
"Ku dai ba zaku taɓa iya zama ku tashi ba tareda kun sako Halima a ciki ba? Yanzu kuma menene nata a maganar da kukeyi?" Anty Amina da bata tsoma musu baki ba sai yanzun ta faɗa. Hajja ta ce
"Ai duk ita ce silar komai, tunda ya auri yarinyar nan kamar wanda aka sakawa hannu shikenan al'amuransa suka taɓarɓare ni dai aurenta babu abinda ya tsinana mun idan ba ɓacin rai da baƙin ciki ba, wannan auren da yayi ai da saninta amma da yake muguwa ce mai baƙar zuciya taja bakinta tayi gum idan da ta faɗa mun tun farko ta ina zan bari haka ta faru?"
"Yanzun ma ai bata ɓaci ba Hajja yanda kikace dole ya saketa in dai yana so yaga haske a rayuwarsa. Matar da tun babu aure yake musu wannan uwar hidimar idan ta tare kuma ai wlh janye shi zatayi ba zaki sake ganinsa ba.
Ta bakin naki mugunta ta saka Halima yin shiru bata faɗa ba tunda ai ba zata ce bata san duk tsayin lokacin nan mijinta na tareda wata ba shine saboda tsabar munafunci ta bar gidan ai in sha Allahu itama ta tafi kenan itama wannan kuma ka sallameta ga mace har mace irin arziƙi na binka soko ka tsaya kana bin wanda ba zasu tsinana maka komai ba" cewar Anty Habiba.
Sai lokacin Abubakar da yayi kamar baya gurin ya ce
"Wlh tallahi ku kuka da kanku sanda haƙƙin Anty Halima zai tambayeku amma duk ba laifin kowa bane laifinki ne Hajja saboda a gidan nan yanda kika dama haka ake sha.