Sashe 94
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BILAL
Tsabar mamaki daskarewa yayi a tsaye lokacin da sautin tsakin Halima ya isa kunnuwansa. Ko a mafarki bai taɓa kawo haka ba, Halimar da ya sani bata taɓa yi masa ko kallon banza ba balle ta jefe shi da irin wannan tsaki da yake tafe da ma'anar tsana da kuma raini. Ya raya ya tafi kawai yabi unarnin Hajja ya rabu da ita amma kuma ya kasa dan idan ya ce baya son Halima ko kuma yana da burin rabuwa da ita shi kansa ya san ƙarya yakeyi, kai ko baya son ta a karon kanta zai so ta saboda zuri'ar dake tsakaninsa da ita ballantana kuma yana son Matar sa, a duniyar nan kuma ya sani bashi da kamarta domin ita ta so shi ba dan komai na sa ba ta juri duk wani wulaƙanci da tozarcinsa ba dan ta rasa yanda zatayi ba sannan ta rufa masa asiri ta haɗiyi baƙin cikin sa ita kaɗai domin ta kare masa martabar sa.
Amma a yanda ya san tana son sa bai zaci za taji muryarsa tayi masa shiru ba, yayi amfani da salon da ya san duk fushin da takeyi zai saka ta sakko amma a maimaikon haka sai tsaki ta biyo shi da shi.
"Ba ita kaɗai ba har mahaifiyar ta ka haɗa ka zaga" zuciyarsa ta raya masa. Ya runtse ido, wlh yayi nadamar furucinsa idan da yana kuma da halin dawo da abinda ya wuce da ya goge waccen ranar ko komai ba zai canzu ba kuwa da ya goge mummunan furucin da yayi shi da kansa ya san bai kyauta ba. Sake kiranta yayi har sau biyu amma bata ɗaga ba, yana tsayen motar Abba ta iso ƙofar gidan maigadi ya buɗe masa ya shiga ya san ya ganshi amma bai ko nuna alamar hakan wannan tasa ya koma cikin mota ya zauna ya tura mata saƙo, jiran minti goma sha biyar yayi kafin ya sake kiran layin amma rashin sa'a ya ji shi a kashe. Ba yanda ya iya yaja mota ya tafi a zuwan gobe zai dawo.
A karo na babu adadi Zulaiha ta sake kiransa, guri ya samu ya gangare ya kashe motar kafin ya kirata dan tun da yamma da sukayi waya ya ce mata idan ya fito zaije amma ya manta dalilin hankalinsa da gaba ɗaya ya tafi gurin Halima.
Kukan kissa ta fashe masa dashi bayan data amsa wayar nan da nan kuwa hankalinsa ya tashi ya shiga rarrashinta, sai da yayi kamar zai yi yaya kafin tayi shiru ta shiga jero masa ƙorafin shikenan daga an ɗaura musu aure yana ganin ta zama mallakinsa zai fara wulaƙanta ta dama ashe duk alƙawarin da ya mata a baya ba gaskiya bane yanzu ne zai bayyana mata asalin halinsa. Ya ringa rantse rantse akan ba haka bane tun safe yana office da gargaɗin da aka masa akan rashin zuwa aikin da bayayi.
"Amma na ɗauka kace can Headquartern ku na Abuja aka mayar da kai meye kuma haɗin ka da nan da har zasu baka query?" Ta faɗa, sai yayi shiru dan ya manta abinda ya gaya mata kenan ya koma Abuja da aiki data tambaye shi yawan zuwan da yakeyi. Sai ya ce
"Kin san wani aiki ne daban na samu a can ɗin kawai bana faɗa ne saboda ba na gomnati bane ba zanyi saurin sakin wannan aikin ba sai naga wancan ɗin ya gama dai dai ta shiyasa kawai nake cewa headquarter aka mayar dani". Hira suka cigaba bayan ya bata uzurin ba zai samu zuwa yau ɗin ba kamar yanda ya mata alƙawari da farko.
"Amma wlh banji daɗi ba na gama saka ran zan kwanta a jikinka na ɗan yi bacci irin na jiya" ta faɗa kai tsaye bayan da ta gama zagaye zagaye taga yana ta kaucew irin hirar da take so suyi. Shiru yayi kafin ya ce
"Nima na so haka amma na faɗa miki uzuri na". Shikenan ta ɓallo hira, ta kuma sake goge masa hadda domin yau ya gane ashe jiya ba komai ya gani ba. Duk yanda ya ringa danne maganar a ransa sai da ya amayar ya ce mata
"Wai Zully ina kika koyi waɗannan abubuwan?" Kuma wai sai a lokacin ne taji kunya ta ce masa
"Gurin ƙanwar Umma Anty Sadiya tunda Baba ya tsayar da ranar ɗaurin aurenmu ba na gaya maka na koma can gidan ba ita ce ta ringa koya mana".
Ji yayi maganar bata kama masa hankali ba amma kuma ta wani ɓangaren ya ɗan samu nutsuwa akan abunda yake masa yawo a rai sai ya ce
"Tayi ƙoƙari amma a ɗan lokacin nan Zullyn da na sani ko ido bata iya haɗawa dani tayi wannan gogewar lallai wannan Antyn tamu ba ƙaramar Malama bace"
"To kuma kunyar me zanji yanzu bayan na rigada na zama mallakinka ko so kake na tsaya wasa Maman Al'amin ta ƙwace mun kai?" Ta bashi amsa, a ransa ya ayyana
"Halima baiwar Allah ita kam bata wannan rashin kunyar a sunnance take tata". A fili kuma sai ya ce
"Kin san kuwa gwana ce a wannan fannin"
"Ai kuwa duk ƙwarewar ta zan nuna maka na fita" ta faɗa ya ce
"Anya kuwa?"
"Idan kana musu yanzu kazo ka ɗauke ni mu tafi gida wlh yau sai na goge maka hadda dama ni a matse nake".
Zuwa yanzu kam ko yaƙi Allah dole tsoron Zulaihan ya ɗarsu a ransa, budurqa fa wacce bata taɓa sanin namiji ba take irin wannan sakin zancen, tattara nutsuwar sa yayi guri guda zuciyarsa na bugawa ya ce
"Kina da hankali kuwa Zulaiha? Duk ina kunyarki da na sanki da ita a da zaki iya ringa furta waɗannan maganganun? Ko da an ɗaura mana aure har yanzu ba banbancin dake tsakanin da da yanzu fa kaɗan ne domin bamu rigada mun zama ɗaya ba ya kamata ace har yanzu kina jin nauyina"
"Yanzu saboda ina ƙoƙarin faranta maka shine har kake nema ka faɗa mun magana? A fakaice ba so kake kace mun yar iska ko mara tarbiyya kenan" ta faɗa cikin hasalar da bai taɓa saninta da ita ba, dake shima zuciyar sa a kusa take sai ya ce
"Ki bawa kanki amsa ya kamata budurwar da bata taɓa sanin namiji ba ta ringa irin wannan abinda kikeyi?"
"Zargina kake yi Bilal? Ƙazafin zina kake so kayi mun?" Ta faɗa cikin ɗaga murya kamar yana gabanta, sai kawai ya zare wayar daga kunennsa ya katse kiran haɗi da kasheta gaba ɗaya dan ya lura idan ya biye mata zasu iya yin ɓatacciya. Mamaki ya rufeshi yanda lokaci ɗaya halayen da bai santa da su ba suke fitowa ɗaya bayan ɗaya. Zulaihar da ko haɗa ido batayi dashi ko zai yi me kuwa kanta na ƙasa duk maganar da zasuyi har gara gara a waya ta kan ɗan sake dashi suyi hira har ta faɗa masa kalaman soyayya amma ko tsareta yayi a zahiri yace ta maimaita sai dai tayi kamar zata saka masa kuka ya haƙura ya ƙyaleta ladabi da biyya kuwa kamar zata kwanta masa idan ya faɗa mata magana ba zata tsallake ba yanda take gudun ɓacin ransa kuwa wani lokacin har ji yakeyi kamar abun yayi yawa ya zama kamar tsoronsa takeji amma yau ita ce ta kama sunan sa katsal abinda bata taɓa yi ba tana ɗaga masa murya kamar zata rufeshi da duka?
"Gaskiya akwai matsala" ya furta a fili kafin ya tayar da mota ya nufi gidan Hajja.
[4/26, 9:17 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 40*
Tunda yaga babur ɗin Kawu Sani a ƙofar gidan gabansa ya shiga faɗuwa domin ya san abinda akw ɓoyewa ya rigada ya bayyana. Sai dai kuma shima yana buƙatar hakan ko dan ya samu a wuce gurin Zulaiha ta tare amma kuma ya san da wahala su kwasheta da daɗi da Hajja. Tun daga tsakar gida yake jiyo maganganun Hajjan tamkar zata ari baki tsabar masifar da take zazzagawa, yana ɗaga labule suka haɗa ido kallon data jefa masa sai da yaji yan cikin sa sun juya, ta ce
"Yawwa gara da kazo, dama Bilal idan har ni na haifeka ba canza mun kai akayi a Asibiti ba, bana buƙatar jin kowacce magana daga bakinka a yanzu har sai bayan ka rubuta takardar saki yanzu an kaiwa waccen kaskar da kuka munafurceni aka ɗaura maka aure da ita." Sai kuma ta fashe da kuka tana cewa
"Allah ya isa tsakanina da kai Sani dan nasan wannan abun shirinka ne Bilal ba zai taɓa mun haka ba, dama shi ɗan uba duk in da yake ai ba zai taɓa sonka tsakani da Allah ba sai in yana da wata manufa, to ka sani haƙƙin marigayi ba zai barka ba wlh tallahi domin ya ƙaunace ka tsakani da Allah in ba an faɗa ba ma waye zai ce ba ciki ɗaya kuka fito dashi ba amma shine saboda zuciyarka cike take da mugun abu ka rasa kuma akan wa zaka juye shi sai akan ɗan da yafi so tir da kai Sani" ta sake rushewa da kuka harda fyace hanci.
Daƙyar ya ƙarasa cikin ya samu guri kusa da Kawu Sani da ya zabga tagumi yana kallon Hajja, murya a dace kamar wanda ya tashi daga ciwo ya ce
"Kiyi haƙuri Hajja amma babul laifin Kawu Sani a cikin maganar nan domin ni na saka shi ya nema mun aure ba wai gaban kansa yayi ba". Kamar an yi ruwan sama an ɗauke kuwa ta dakata da kukan da takeyi ta kafe shi da ido alamun sauraron ƙarin bayani, ƙasa yayi da kai kafin ya cigaba da cewa
Tsabar mamaki daskarewa yayi a tsaye lokacin da sautin tsakin Halima ya isa kunnuwansa. Ko a mafarki bai taɓa kawo haka ba, Halimar da ya sani bata taɓa yi masa ko kallon banza ba balle ta jefe shi da irin wannan tsaki da yake tafe da ma'anar tsana da kuma raini. Ya raya ya tafi kawai yabi unarnin Hajja ya rabu da ita amma kuma ya kasa dan idan ya ce baya son Halima ko kuma yana da burin rabuwa da ita shi kansa ya san ƙarya yakeyi, kai ko baya son ta a karon kanta zai so ta saboda zuri'ar dake tsakaninsa da ita ballantana kuma yana son Matar sa, a duniyar nan kuma ya sani bashi da kamarta domin ita ta so shi ba dan komai na sa ba ta juri duk wani wulaƙanci da tozarcinsa ba dan ta rasa yanda zatayi ba sannan ta rufa masa asiri ta haɗiyi baƙin cikin sa ita kaɗai domin ta kare masa martabar sa.
Amma a yanda ya san tana son sa bai zaci za taji muryarsa tayi masa shiru ba, yayi amfani da salon da ya san duk fushin da takeyi zai saka ta sakko amma a maimaikon haka sai tsaki ta biyo shi da shi.
"Ba ita kaɗai ba har mahaifiyar ta ka haɗa ka zaga" zuciyarsa ta raya masa. Ya runtse ido, wlh yayi nadamar furucinsa idan da yana kuma da halin dawo da abinda ya wuce da ya goge waccen ranar ko komai ba zai canzu ba kuwa da ya goge mummunan furucin da yayi shi da kansa ya san bai kyauta ba. Sake kiranta yayi har sau biyu amma bata ɗaga ba, yana tsayen motar Abba ta iso ƙofar gidan maigadi ya buɗe masa ya shiga ya san ya ganshi amma bai ko nuna alamar hakan wannan tasa ya koma cikin mota ya zauna ya tura mata saƙo, jiran minti goma sha biyar yayi kafin ya sake kiran layin amma rashin sa'a ya ji shi a kashe. Ba yanda ya iya yaja mota ya tafi a zuwan gobe zai dawo.
A karo na babu adadi Zulaiha ta sake kiransa, guri ya samu ya gangare ya kashe motar kafin ya kirata dan tun da yamma da sukayi waya ya ce mata idan ya fito zaije amma ya manta dalilin hankalinsa da gaba ɗaya ya tafi gurin Halima.
Kukan kissa ta fashe masa dashi bayan data amsa wayar nan da nan kuwa hankalinsa ya tashi ya shiga rarrashinta, sai da yayi kamar zai yi yaya kafin tayi shiru ta shiga jero masa ƙorafin shikenan daga an ɗaura musu aure yana ganin ta zama mallakinsa zai fara wulaƙanta ta dama ashe duk alƙawarin da ya mata a baya ba gaskiya bane yanzu ne zai bayyana mata asalin halinsa. Ya ringa rantse rantse akan ba haka bane tun safe yana office da gargaɗin da aka masa akan rashin zuwa aikin da bayayi.
"Amma na ɗauka kace can Headquartern ku na Abuja aka mayar da kai meye kuma haɗin ka da nan da har zasu baka query?" Ta faɗa, sai yayi shiru dan ya manta abinda ya gaya mata kenan ya koma Abuja da aiki data tambaye shi yawan zuwan da yakeyi. Sai ya ce
"Kin san wani aiki ne daban na samu a can ɗin kawai bana faɗa ne saboda ba na gomnati bane ba zanyi saurin sakin wannan aikin ba sai naga wancan ɗin ya gama dai dai ta shiyasa kawai nake cewa headquarter aka mayar dani". Hira suka cigaba bayan ya bata uzurin ba zai samu zuwa yau ɗin ba kamar yanda ya mata alƙawari da farko.
"Amma wlh banji daɗi ba na gama saka ran zan kwanta a jikinka na ɗan yi bacci irin na jiya" ta faɗa kai tsaye bayan da ta gama zagaye zagaye taga yana ta kaucew irin hirar da take so suyi. Shiru yayi kafin ya ce
"Nima na so haka amma na faɗa miki uzuri na". Shikenan ta ɓallo hira, ta kuma sake goge masa hadda domin yau ya gane ashe jiya ba komai ya gani ba. Duk yanda ya ringa danne maganar a ransa sai da ya amayar ya ce mata
"Wai Zully ina kika koyi waɗannan abubuwan?" Kuma wai sai a lokacin ne taji kunya ta ce masa
"Gurin ƙanwar Umma Anty Sadiya tunda Baba ya tsayar da ranar ɗaurin aurenmu ba na gaya maka na koma can gidan ba ita ce ta ringa koya mana".
Ji yayi maganar bata kama masa hankali ba amma kuma ta wani ɓangaren ya ɗan samu nutsuwa akan abunda yake masa yawo a rai sai ya ce
"Tayi ƙoƙari amma a ɗan lokacin nan Zullyn da na sani ko ido bata iya haɗawa dani tayi wannan gogewar lallai wannan Antyn tamu ba ƙaramar Malama bace"
"To kuma kunyar me zanji yanzu bayan na rigada na zama mallakinka ko so kake na tsaya wasa Maman Al'amin ta ƙwace mun kai?" Ta bashi amsa, a ransa ya ayyana
"Halima baiwar Allah ita kam bata wannan rashin kunyar a sunnance take tata". A fili kuma sai ya ce
"Kin san kuwa gwana ce a wannan fannin"
"Ai kuwa duk ƙwarewar ta zan nuna maka na fita" ta faɗa ya ce
"Anya kuwa?"
"Idan kana musu yanzu kazo ka ɗauke ni mu tafi gida wlh yau sai na goge maka hadda dama ni a matse nake".
Zuwa yanzu kam ko yaƙi Allah dole tsoron Zulaihan ya ɗarsu a ransa, budurqa fa wacce bata taɓa sanin namiji ba take irin wannan sakin zancen, tattara nutsuwar sa yayi guri guda zuciyarsa na bugawa ya ce
"Kina da hankali kuwa Zulaiha? Duk ina kunyarki da na sanki da ita a da zaki iya ringa furta waɗannan maganganun? Ko da an ɗaura mana aure har yanzu ba banbancin dake tsakanin da da yanzu fa kaɗan ne domin bamu rigada mun zama ɗaya ba ya kamata ace har yanzu kina jin nauyina"
"Yanzu saboda ina ƙoƙarin faranta maka shine har kake nema ka faɗa mun magana? A fakaice ba so kake kace mun yar iska ko mara tarbiyya kenan" ta faɗa cikin hasalar da bai taɓa saninta da ita ba, dake shima zuciyar sa a kusa take sai ya ce
"Ki bawa kanki amsa ya kamata budurwar da bata taɓa sanin namiji ba ta ringa irin wannan abinda kikeyi?"
"Zargina kake yi Bilal? Ƙazafin zina kake so kayi mun?" Ta faɗa cikin ɗaga murya kamar yana gabanta, sai kawai ya zare wayar daga kunennsa ya katse kiran haɗi da kasheta gaba ɗaya dan ya lura idan ya biye mata zasu iya yin ɓatacciya. Mamaki ya rufeshi yanda lokaci ɗaya halayen da bai santa da su ba suke fitowa ɗaya bayan ɗaya. Zulaihar da ko haɗa ido batayi dashi ko zai yi me kuwa kanta na ƙasa duk maganar da zasuyi har gara gara a waya ta kan ɗan sake dashi suyi hira har ta faɗa masa kalaman soyayya amma ko tsareta yayi a zahiri yace ta maimaita sai dai tayi kamar zata saka masa kuka ya haƙura ya ƙyaleta ladabi da biyya kuwa kamar zata kwanta masa idan ya faɗa mata magana ba zata tsallake ba yanda take gudun ɓacin ransa kuwa wani lokacin har ji yakeyi kamar abun yayi yawa ya zama kamar tsoronsa takeji amma yau ita ce ta kama sunan sa katsal abinda bata taɓa yi ba tana ɗaga masa murya kamar zata rufeshi da duka?
"Gaskiya akwai matsala" ya furta a fili kafin ya tayar da mota ya nufi gidan Hajja.
[4/26, 9:17 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 40*
Tunda yaga babur ɗin Kawu Sani a ƙofar gidan gabansa ya shiga faɗuwa domin ya san abinda akw ɓoyewa ya rigada ya bayyana. Sai dai kuma shima yana buƙatar hakan ko dan ya samu a wuce gurin Zulaiha ta tare amma kuma ya san da wahala su kwasheta da daɗi da Hajja. Tun daga tsakar gida yake jiyo maganganun Hajjan tamkar zata ari baki tsabar masifar da take zazzagawa, yana ɗaga labule suka haɗa ido kallon data jefa masa sai da yaji yan cikin sa sun juya, ta ce
"Yawwa gara da kazo, dama Bilal idan har ni na haifeka ba canza mun kai akayi a Asibiti ba, bana buƙatar jin kowacce magana daga bakinka a yanzu har sai bayan ka rubuta takardar saki yanzu an kaiwa waccen kaskar da kuka munafurceni aka ɗaura maka aure da ita." Sai kuma ta fashe da kuka tana cewa
"Allah ya isa tsakanina da kai Sani dan nasan wannan abun shirinka ne Bilal ba zai taɓa mun haka ba, dama shi ɗan uba duk in da yake ai ba zai taɓa sonka tsakani da Allah ba sai in yana da wata manufa, to ka sani haƙƙin marigayi ba zai barka ba wlh tallahi domin ya ƙaunace ka tsakani da Allah in ba an faɗa ba ma waye zai ce ba ciki ɗaya kuka fito dashi ba amma shine saboda zuciyarka cike take da mugun abu ka rasa kuma akan wa zaka juye shi sai akan ɗan da yafi so tir da kai Sani" ta sake rushewa da kuka harda fyace hanci.
Daƙyar ya ƙarasa cikin ya samu guri kusa da Kawu Sani da ya zabga tagumi yana kallon Hajja, murya a dace kamar wanda ya tashi daga ciwo ya ce
"Kiyi haƙuri Hajja amma babul laifin Kawu Sani a cikin maganar nan domin ni na saka shi ya nema mun aure ba wai gaban kansa yayi ba". Kamar an yi ruwan sama an ɗauke kuwa ta dakata da kukan da takeyi ta kafe shi da ido alamun sauraron ƙarin bayani, ƙasa yayi da kai kafin ya cigaba da cewa