Sashe 31
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar da aka kai azumi na goma tun yamma dama yace mun idan an sha ruwa zamu je gidan su mu gaishe su haka yasa dana tashi yin abin shan ruwa nayi da ɗan yawa zan ɗibar wa Hajjansu. A raina na raya se yayi magana dan kullum ne se yayi mitar ina dafa abinci yana yin yawa da zarar yaga kwanuka ze fara buɗe buɗe yana mitar duk cikin mu zamu cinye wannan a hakan ma ba wani abin kirki nakeyi ba saboda bana jin daɗi baya wuce abu biyu me dan sauƙin saraffawa na buɗa baki se kuma abinci da za'a sake ci da kuma lokacin sahur amma haka ze yi ta surutun nayi da yawa kuma a hakan ze cinye tas har ya ringa cewa beyi sahur me kyau ba. Dama ƙiri ƙiri ya hanani yin kunu da ƙosai na sadakar da nayi niyya wai da me zanji?
A kwando na jera kwanukan abincin dana zuba, ina jin kamar zazzaɓi ze rufe ni amma na daure, a sabon mashin ɗin daya buɗe shekaran jiya muka fita. Tun lokacin biki yace mun ya siyar da mashin ɗin sa se yanzu ya sake siyan wani. Muna tafe muna hira gwanin sha'awa har muka isa gidan a raina nayi gulmar yanda bece komai ba daya ga basket ɗin abincin,
kamar Hajiyar su zata goya ni haka ta ringa nan nan da ni. Taji daɗin abincin dana kai mata, ina zaune ta soya mun ƙosai tace tasan da yawan mutane sun fi son ƙosai da an sauke daga mai shiyasa da yace zamu zo ta ajiye ƙullin. Sosai kuwa naci ƙosan da kunun tsakiya a nan take gaya mun ai geron da waken ma daga gidan mu aka kawo musu harda buhun shinkafa dana sugar da pastar mangyaɗa. Se gurin goma saura muka bar gidan, a hanya naga gurin gasa tsire tun daga nesa naji raina ya biya dan haka nace masa dan Allah ya tsaya ya mu siya ba musu kuwa ya tsaya ya siya muka wuce gida.
A haka aka ƙara azumi biyar, tun washe garin da muka je gidan su nake jira naji yace na shirya muje gaida nawa iyayen amma shiru. Har Mama se da ta gaji ta mun magana akan yaushe zamu zo? Na ce mata bani da lafiya ne amma zamu zo, Allah sarki uwa washe garin da mukayi maganar kuwa se ga Imam da Amira da Nabila yar ƙanwar Abbanmu Anty Surayya da tazo hutu gidan Mama tace su zo su dubani. Ran da aka kai azumi na sha biyar ɗin tun asuba na masa zancen se yaushe zamu je gidan mu ne?
"Akwai abin da nake jira ne kin ga ai ba daɗi muje musu hannu haka babu wata tsaraba" amsar daya bani kenan. Se nace masa
"Yanzu ita Hajja ba haka muka je muka gaishe ta ba bamu kai mata komai ba suma gaisuwa ce ai ba wani abu aka ce dole se an kawo ba". Kamar baze yarda ba har na fitar da rai kuma bayan la'asar ina ƙoƙarin ɗora abin shan ruwa yace na shirya kawai ya kaini gidan. Sosai naji daɗi, da muka je be shiga ba ya ce mun se ya dawo ɗauka ta tukunna yanzu sauri yake ana jiran sa a wani guri. Mama na kitchen da Nabila suna aiki ta ringa kallo na da mamaki na rungumeta cikin jin daɗin ganin ta dan rabo na da gidan tun zuwan da nayi akan registration ɗin NYSC. Abba kansa se da ya tsokane ni yace dama gobe suke shirin zuwa ban haƙuri ace azumi har ya raba basu ga ido na ba gara suzo suji wane laifi sukayi haka.
Ina rufe fuska nace
"Ai kullum ina kiran ku a waya Abba"
"Haka ne, amma muga juna ɗin ma ai da daɗi ko Halimatu? Ko da yake ke fa tunda kika samu Bilal shikenan kika manta da kowa" Abban ya sake tsokanota se kawai na tashi na koma ɗaki dan duk se naji ban kyauta ba na kuma ƙudire a raina zan gyara hakan ba zata sake faruwa ba. Cikin farin ciki nasha ruwa da yan uwana, can ƙasan raina ina tunanin ko Bilal ya ci abinci? Ko dame ya karya azumin sa oho? Ana idar da sallar asham Mu'azzam yace mun
"Ga matsolon mijinki can a waje". Na galla masa harara kawai ba tare da nace komai ba. Tare suka shigo da Abba, a can falon ya zauna bayan sun gaisa da Mama na shiga kitchen na haɗa masa abinci na bawa Amirah ta kai masa, se da ya gama kafin mukayi sallama muka tafi kunya duk ta dabaibayeni jin Mama ta fahimci ina da ciki har tana tambayata wata nawa ne nace mata ban sani ba tun da bamu je asibiti ba pt test kawai nayi naga positive dan ko Bilal ma ban gayawa ba.
"Ya dai kamata kije gidan Labiba tunda kalar naki hankalin be nuna miki ba har yanzu" Mama ta faɗa sanda ta rako ni bakin ƙofa. Tunda nayi aure ko sau ɗaya banje gidan Anty Labiba ba ita ma kuma tun washe garin da aka kaini bata sake komawa ba wata tara kenan muna waya muna chat. Har ga Allah kawai ina jin kunyar abin da na mata akan zancen aure na da Bilal ne, duk da ko a fuska bata nuna mun komai ba amma nasan Anty Labibar da na sani babu yanda za'a yi nayi aure ta ɗauki wata tara bata tako gida na ba har idan ba da wani abu data riƙe a ranta ba ni kuma bana son naje ta tayar da maganar shiyasa kawai nake gudun zuwa gidan nata. Kuma muna haɗuwa a gida yaranta ma kusan duk sanda su Amira zasuje mun tare su ke zuwa dasu.
Amsawa Mama nayi da zanje in sha Allah na wuce tana sake jaddada mun na tabbata naje asibiti bata son sakarci. Washe gari nayiwa Bilal zancen zanje gidan Anty Labiba, be musa yanda ya saba ba yace duk sanda na shirya na je, take na kirata wayarta a kashe ina hawa whatsapp na ganta online dan haka na ce mata gobe zanzo in Allah ya kaimu. Amsar data bani
"Bana nan" na ringa juya maganar, bata ma tambayi ƙarfe nawa zanzo ba ko wani abu kawai tace bata nan. Da take cewa in har na auri Bilal zata yanke zumunta dani ashe dagaske take kenan? Take shaiɗan ya shiga mun famfo, na watsa hannye a fili nace
"Kin huta ai. Bilal dai da bakya ƙaunar gani na dashi shi ɗin Allah ya zaɓa mun muyi rayuwa tare se haƙuri". Shikenan naci gaba da sabgogina. Ganin har an kai azumi na ashirin da uku Bilal be bani ko ƙyalle da sunan na siyi kayan sallah ba na cire rai da zeyi mun ban kuma tambaye shi ba saboda hidimar daya zo masa katsahan ƙanwar sa da akayi bikin mu tare ta haihu haihuwar kuma tazo mata da matsala ƙarshe se CS aka mata mijin dake bashi da mutunchi tunda ta kwana ta wuni tana labor washe garin ya tattaro ta ya kawo ta gida su suka yi duk wata ɗawainiyar asibiti har aka ciro mata babyn kwana uku kenan ko zuwa ganin su beyi ba. Bilal ne ya biya kuɗin aikin yayyen sa mata kuma suka haɗa mata kayan barka da sauran abubuwan buƙata da suka tashi suka yiwa yaron huɗu ba da sunan Babban Yayansu da suke uba ɗaya shine ya bada ragon da aka yanka masa.
Cikin kuɗin da Abba ya tura mun tun washe garin da naje gida na siyi lace guda biyu na haɗa da atamfofi biyu cikin na lefe da ban taɓa komai a ciki ba na bada ɗinki. Na san Mama bata san ya bani kuɗin ba dan haka ni ma ban mata zancen ba, da sauran kuɗin nayi sauran buƙatun da nake dasu ciki harda zuwa asibiti na buɗe file na anti natal dan da na yiwa Bilal magana ina so naje asibiti cewa yayi me zanje yi bayan ga magunguna nan an bani kuma na samu sauƙi tun da a zahiri babu abinda yake damu na banda amai se zazzaɓin dare gari na waye wa kuma zan shiga sabgogi na idan naji garau nayi azumi idan naji bazan iya ba na sauke. Saboda ina so nayi masa ba zata akan cikin se kawai nace masa ulcer se ta tasar mun ya siyo mun Omeprazole da gestid a chemist yace na ringa sha.
Cikin ikon Allah azumi ya ƙare anyi sanarwar ganin watan sallah ya tsaya, kasancewar sallah ta ta farko a gidan aure yasa naji ina sha'awar nayi abincin sallah nima yanda naga anayi. Dake tunda Fadila ta haihu Bilal suke ta zirga zirga tsakanin gida da asibiti wata ran se tara yake dawowa yau ɗin ma yana gida aka kira shi jikin yaron ya rikice dake da jundice aka haife shi shine ya fita suka mayar dashi asibiti. Har mamaki nakeyi yanda ya damu sosai da lafiyar ƙanwar tasa ba kuma ya ƙyashin kashe kuɗi, da na tambaye shi ina mijin ta da suke ta ɗawainiya da ita haka ma cewa yayi shi ba ta mijinta su keyi yanzu ba dan idan ta mutu su suke da asara ba mijin ba jira sukeyi ma a ƙare azumi suyi ƙarar sa ya saketa ba zata koma ba. Ban tsawwala da jin dalili ba nace Allah ya rufa asiri kawai muka bar zancen.
A kwando na jera kwanukan abincin dana zuba, ina jin kamar zazzaɓi ze rufe ni amma na daure, a sabon mashin ɗin daya buɗe shekaran jiya muka fita. Tun lokacin biki yace mun ya siyar da mashin ɗin sa se yanzu ya sake siyan wani. Muna tafe muna hira gwanin sha'awa har muka isa gidan a raina nayi gulmar yanda bece komai ba daya ga basket ɗin abincin,
kamar Hajiyar su zata goya ni haka ta ringa nan nan da ni. Taji daɗin abincin dana kai mata, ina zaune ta soya mun ƙosai tace tasan da yawan mutane sun fi son ƙosai da an sauke daga mai shiyasa da yace zamu zo ta ajiye ƙullin. Sosai kuwa naci ƙosan da kunun tsakiya a nan take gaya mun ai geron da waken ma daga gidan mu aka kawo musu harda buhun shinkafa dana sugar da pastar mangyaɗa. Se gurin goma saura muka bar gidan, a hanya naga gurin gasa tsire tun daga nesa naji raina ya biya dan haka nace masa dan Allah ya tsaya ya mu siya ba musu kuwa ya tsaya ya siya muka wuce gida.
A haka aka ƙara azumi biyar, tun washe garin da muka je gidan su nake jira naji yace na shirya muje gaida nawa iyayen amma shiru. Har Mama se da ta gaji ta mun magana akan yaushe zamu zo? Na ce mata bani da lafiya ne amma zamu zo, Allah sarki uwa washe garin da mukayi maganar kuwa se ga Imam da Amira da Nabila yar ƙanwar Abbanmu Anty Surayya da tazo hutu gidan Mama tace su zo su dubani. Ran da aka kai azumi na sha biyar ɗin tun asuba na masa zancen se yaushe zamu je gidan mu ne?
"Akwai abin da nake jira ne kin ga ai ba daɗi muje musu hannu haka babu wata tsaraba" amsar daya bani kenan. Se nace masa
"Yanzu ita Hajja ba haka muka je muka gaishe ta ba bamu kai mata komai ba suma gaisuwa ce ai ba wani abu aka ce dole se an kawo ba". Kamar baze yarda ba har na fitar da rai kuma bayan la'asar ina ƙoƙarin ɗora abin shan ruwa yace na shirya kawai ya kaini gidan. Sosai naji daɗi, da muka je be shiga ba ya ce mun se ya dawo ɗauka ta tukunna yanzu sauri yake ana jiran sa a wani guri. Mama na kitchen da Nabila suna aiki ta ringa kallo na da mamaki na rungumeta cikin jin daɗin ganin ta dan rabo na da gidan tun zuwan da nayi akan registration ɗin NYSC. Abba kansa se da ya tsokane ni yace dama gobe suke shirin zuwa ban haƙuri ace azumi har ya raba basu ga ido na ba gara suzo suji wane laifi sukayi haka.
Ina rufe fuska nace
"Ai kullum ina kiran ku a waya Abba"
"Haka ne, amma muga juna ɗin ma ai da daɗi ko Halimatu? Ko da yake ke fa tunda kika samu Bilal shikenan kika manta da kowa" Abban ya sake tsokanota se kawai na tashi na koma ɗaki dan duk se naji ban kyauta ba na kuma ƙudire a raina zan gyara hakan ba zata sake faruwa ba. Cikin farin ciki nasha ruwa da yan uwana, can ƙasan raina ina tunanin ko Bilal ya ci abinci? Ko dame ya karya azumin sa oho? Ana idar da sallar asham Mu'azzam yace mun
"Ga matsolon mijinki can a waje". Na galla masa harara kawai ba tare da nace komai ba. Tare suka shigo da Abba, a can falon ya zauna bayan sun gaisa da Mama na shiga kitchen na haɗa masa abinci na bawa Amirah ta kai masa, se da ya gama kafin mukayi sallama muka tafi kunya duk ta dabaibayeni jin Mama ta fahimci ina da ciki har tana tambayata wata nawa ne nace mata ban sani ba tun da bamu je asibiti ba pt test kawai nayi naga positive dan ko Bilal ma ban gayawa ba.
"Ya dai kamata kije gidan Labiba tunda kalar naki hankalin be nuna miki ba har yanzu" Mama ta faɗa sanda ta rako ni bakin ƙofa. Tunda nayi aure ko sau ɗaya banje gidan Anty Labiba ba ita ma kuma tun washe garin da aka kaini bata sake komawa ba wata tara kenan muna waya muna chat. Har ga Allah kawai ina jin kunyar abin da na mata akan zancen aure na da Bilal ne, duk da ko a fuska bata nuna mun komai ba amma nasan Anty Labibar da na sani babu yanda za'a yi nayi aure ta ɗauki wata tara bata tako gida na ba har idan ba da wani abu data riƙe a ranta ba ni kuma bana son naje ta tayar da maganar shiyasa kawai nake gudun zuwa gidan nata. Kuma muna haɗuwa a gida yaranta ma kusan duk sanda su Amira zasuje mun tare su ke zuwa dasu.
Amsawa Mama nayi da zanje in sha Allah na wuce tana sake jaddada mun na tabbata naje asibiti bata son sakarci. Washe gari nayiwa Bilal zancen zanje gidan Anty Labiba, be musa yanda ya saba ba yace duk sanda na shirya na je, take na kirata wayarta a kashe ina hawa whatsapp na ganta online dan haka na ce mata gobe zanzo in Allah ya kaimu. Amsar data bani
"Bana nan" na ringa juya maganar, bata ma tambayi ƙarfe nawa zanzo ba ko wani abu kawai tace bata nan. Da take cewa in har na auri Bilal zata yanke zumunta dani ashe dagaske take kenan? Take shaiɗan ya shiga mun famfo, na watsa hannye a fili nace
"Kin huta ai. Bilal dai da bakya ƙaunar gani na dashi shi ɗin Allah ya zaɓa mun muyi rayuwa tare se haƙuri". Shikenan naci gaba da sabgogina. Ganin har an kai azumi na ashirin da uku Bilal be bani ko ƙyalle da sunan na siyi kayan sallah ba na cire rai da zeyi mun ban kuma tambaye shi ba saboda hidimar daya zo masa katsahan ƙanwar sa da akayi bikin mu tare ta haihu haihuwar kuma tazo mata da matsala ƙarshe se CS aka mata mijin dake bashi da mutunchi tunda ta kwana ta wuni tana labor washe garin ya tattaro ta ya kawo ta gida su suka yi duk wata ɗawainiyar asibiti har aka ciro mata babyn kwana uku kenan ko zuwa ganin su beyi ba. Bilal ne ya biya kuɗin aikin yayyen sa mata kuma suka haɗa mata kayan barka da sauran abubuwan buƙata da suka tashi suka yiwa yaron huɗu ba da sunan Babban Yayansu da suke uba ɗaya shine ya bada ragon da aka yanka masa.
Cikin kuɗin da Abba ya tura mun tun washe garin da naje gida na siyi lace guda biyu na haɗa da atamfofi biyu cikin na lefe da ban taɓa komai a ciki ba na bada ɗinki. Na san Mama bata san ya bani kuɗin ba dan haka ni ma ban mata zancen ba, da sauran kuɗin nayi sauran buƙatun da nake dasu ciki harda zuwa asibiti na buɗe file na anti natal dan da na yiwa Bilal magana ina so naje asibiti cewa yayi me zanje yi bayan ga magunguna nan an bani kuma na samu sauƙi tun da a zahiri babu abinda yake damu na banda amai se zazzaɓin dare gari na waye wa kuma zan shiga sabgogi na idan naji garau nayi azumi idan naji bazan iya ba na sauke. Saboda ina so nayi masa ba zata akan cikin se kawai nace masa ulcer se ta tasar mun ya siyo mun Omeprazole da gestid a chemist yace na ringa sha.
Cikin ikon Allah azumi ya ƙare anyi sanarwar ganin watan sallah ya tsaya, kasancewar sallah ta ta farko a gidan aure yasa naji ina sha'awar nayi abincin sallah nima yanda naga anayi. Dake tunda Fadila ta haihu Bilal suke ta zirga zirga tsakanin gida da asibiti wata ran se tara yake dawowa yau ɗin ma yana gida aka kira shi jikin yaron ya rikice dake da jundice aka haife shi shine ya fita suka mayar dashi asibiti. Har mamaki nakeyi yanda ya damu sosai da lafiyar ƙanwar tasa ba kuma ya ƙyashin kashe kuɗi, da na tambaye shi ina mijin ta da suke ta ɗawainiya da ita haka ma cewa yayi shi ba ta mijinta su keyi yanzu ba dan idan ta mutu su suke da asara ba mijin ba jira sukeyi ma a ƙare azumi suyi ƙarar sa ya saketa ba zata koma ba. Ban tsawwala da jin dalili ba nace Allah ya rufa asiri kawai muka bar zancen.