Sashe 67
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ƙasa na yi da kai dan bani da bakin kare kai na ina jin Mama ta na cewa
"Au da kika ce idan aka miki zani bayar da kayan zaki yi ashe da gaske kike yi? To yanzu ina sauran ko su ma duk kin bayar da su?"
"Aa suna nan wlh duk ban ma taɓa sakawa ba, shima wancan ɗin ba fa bata na yi ba iya zanin ne shi ma zuwa ta yi ta manto zanin goyo a gida shi ne na bata aro kuma ban san da shi ta tafi ba" na faɗa jin Mama zata balbaleni da faɗa, ashe da na yi shiru ya fiye mun alkhairi ma nan kuwa ta shiga faɗan ta na cewa
"Saboda ba da kuɗin ki kika siya ba ai dole ki ce baki san ta tafi da shi ba, meye amfanin rigar da ɗankwalin toh yanzu? Da kin haɗa kin bata ko banza ta mora tun da sun fi ki sanin darajar sutura. Shashsha, naga uban da zai sake siya miki kayan balle har ki wulaƙanta su" ta tattare waɗanda su Hafiz suka kawo ta ce
"Waɗannan zan riƙe kuwa" na fashe da dariya ina cewa
"Wlh bari na gidan nan duk yan uba sun shiga sun fita sun gurɓata mun ke Mama gaba ɗaya kin koyi faɗa bayan ba halin ki ba ne" bata kula ni ba ta wuce ɗaki ta bar mu da Anty Labiba. Sai bayan isha'i da Anty Labiban zata ta fi ta ke cemun
"Yau ɗin zamu tafi ko se daga baya zaki zo?"
Na bi ta da kallon rashin fahimta, Mama da ta shigo ɗakin ta ce
"Gidan ta zaki je ki zauna kafin mu dawo tun da kin ce ba zaki koma gidan ki ba". Na yi rau da ido na ce
"Amma Abba ya ce na zauna a nan ai"
"To ba zaki zauna ba idan kuma kika cika mun ciki wlh yanzu zaki tattara ki koma gidan ki. Ina dama kin zaɓe shi sama da nan ɗin? Da ya kore ki ya ce ki taho ba share guri kika yi kika zauna ba? Tun da haka kika zaɓawa kan ki ai shikenan, shi dai mutunchi mutum shi yake siyawa kan sa tunda ke kin saryar da naki ai shikenan" Mama ta faɗa cikin fushi tana gamawa kuma ta fice daga ɗakin ta barmu.
Anty Labiba da ke tsaye ta koma ta zauna kusa da ni haɗi da dafa kafaɗa ta, kamar ina jira na fashe da kuka na faɗa jikin ta, ta ce
"Bazan ɓoye miki ba ran Mama a ɓace ya ke da ke Halima amma na lura rashin hankali sam bai bari kin fahimci haka ba"
"Toh ai bata faɗa mun ba" na faɗa cikin kuka. Ta ɗago ni daga jikin ta ta ce
"Ke baki da tunani kenan, baki san abinda kika yi zai ɓata mata rai ba sai ta buɗe baki ta gaya miki? Halima har sai yaushe zaki fara tunani daidai da shekarunki ne?
Yanzu bayan duk rashin mutunchin da Mijinki ya yi kin san kuma labari ya zo kunnuwan su, baki yi tunanin ya kamata ko a waya ne ki kira ki bada haƙuri ba sannan sai yanzu ki iya ɗakko ƙafa ki zo gidan ki ce zaki zauna. Na jinjinawa ƙarfin hali irin naki".
"Ke fa kika ce ko me zai yi mun na yi haƙuri na shanye, kuma na san idan na zo na faɗi wani abu akan Bilal ke zaki fara cewa dama ai kin faɗa" na sake faɗa ina ƙoƙarin tsaida kuka na. Ta yi murmushin da kana kallo zaka san na takaici ne kafin ta ce
"Yanzu ai kin gani da idon ki abin da na faɗa ɗin ko? Kuma saboda kar muyi magana shiyasa kika zaɓi ki nuna masa iyayen ki ba su da mutunchi a idonki zai iya zagin su kuma ki iya cigaba da zama da shi ko?"
"Bilal bai zage ni ba Hajjan su ce, kuma wlh bayan sun tafi ya dawo ya bani haƙuri kuma ko cewa da yayi na taho gida ya gaya mun saboda Hajja ne amma ba har ransa yayi maganar ba" na faɗa, sai ta sake ni ta ce
"Ni wlh yanzu abubuwan da kike yi sun daina bani haushi tausayi kawai kike bani saboda baki san me kike yi ba. Wannan haukan da kike yi ya wuce So Halima you are obsessed with him idan kuma baki yiwa kanki faɗa kin fahimci zahiri ba zaki haukace a banza ranar da kika fahimci Son ma So wani kike yi. Yanzu ke kin yarda da wasan da miji zai fututtuke ya ci miki mutunchi sannan ya dawo daga baya ya ce miki wasa ya ke yi wasan ma kuma ya haɗa har da iyaye a ina ake haka?
Ke ki gwada yi masa irin wasan ki gani idan zaku kwashe lafiya, ba zagi ba, ki gwada ɗaga masa murya ko kuma cikin wasan ki ce masa BANZA kawai ki gani a ranar idan bai sauya miki kamanni kafin ya kawo mana ke ba.
A soyayya akwai sanin ciwon kai Halima, a soyayya akwai sanin martabar kai, a soyayya akwai mutunta kai, akwai aji. So is not do or die affair Halima duk muna soyayya muna da waɗanda muke so amma hakan ba shi ya saka muke banzatar da kanmu duk da sunan So ba zaman ki da ni bai amfana miki komai ba domin babu abinda kika koya. Ba alfahari ba ni na yarda da kaina kuma na san na isa mace. Kin sani da ace sakarya ce ni irin ki da ban kai labari a gidan Saleh ba. Na goga da dangin miji na goga da matan bariki da na riƙe Allah na kuma yi amfani da baiwar da ubangiji ya mun a matsayi na na mace a gaban idonki komai ya zama labari. In da na bari soyayyar sa ta rufe mun ido yanda kike yi a yanzu na bishi a yanda na tarar da shi ƙila yanzu idan ban mutu da baƙin ciki ba da tuni na daɗe da zarewa sai ke akan Bilal da bai wuci jariri a makarantar tantiran Maza ba.
Yau da ace Bilal is reciprocating, yana maida miki martanin abin da kike yi masa tare kuka zauce kuke haukan ku babu mai ce miki dan me? Babu mai ganin baiken ki domin dama ai Hausawa suka ce ka gaida mai gaishe ka amma a nan, ke kaɗai kike kiɗan ki kina rawar ki. Ya mayar da ke wawiya, sai idan buƙatar sa ta tashi yana so ya cuceki ya miki wayo a lokacin ya ke gwada miki kina da amfani a gurin sa da zarar kuma ya samu biyan buƙata shikenan da ke da babu duk ɗaya kuke a wajen sa.
Kalle ki, aure kusan shekara biyu amma kullum jiya i yau babu wani canji a tattare da ke wanda za'a ce kin tsinci wani abu cikin auren soyayyar da kika na ce sai kinyi. Ki kalli ƙawayen ki da kike musu dariya kina ganin sun auri waɗanda basu da ce da su ba, hatta da Hansa'u da kike cewa zata auri sa'an Babanta idan akajera ku dake da kika auri yaro sabon jinin sai an ɗauke ta sau dubu ba'a ɗauki ki ba saboda ta fiki walwala, ta fiki kyan gani da ka kalle ta baka buƙatar a faɗa maka tana cikin farin ciki a gidan auren ta ko ita kaɗai ta ishe ki ishara da ki gane ƙuruciya ba ita bace soyayya a gidan aure, dacen abokin zama shi ne kan gaba.
Yanzu ko sati biyu baki rufa ba haihuwar fari amma tun kina gadon Asibiti yake watangaririya da ke. Mazan kirki ana roƙon su basa so ake ɗauke matan su a tafi da su gida wanka amma me tun yana miki hannun ka mai sanda har ta kai ya fito ƙiri ƙiri ya kore ki wannan wane irin rashin daraja ne?
Yanda mata muke so mu auri miji mai aji haka kowanne namiji yake son samun macen da ta san kanta, kisan kanki a sanda miji ya miki abin farin ciki haka ki san kanki a sanda ya ɓata miki rai amma ba ki zama ballagaza ke son miji duk in da ya ja ki ya watsar nan zaki yi a lissafi na hankali ma kin san dole wata rana ya ƙosa da halin ki. Wallahi idan baki shiga hankalin ba Halima akwai ranar da sai kin ɗora hannu aka kin yi ihu a sanda Bilal ze gwada miki ke ɗin ba komai ba ce a gurin sa, a kan idon ki ze ɗakko mace mai aji da ta san kanta ya riritata a sannan kowa zai zage shi ace ya wulaƙanta ki amma gaskiyar magana ke kika fara wulaƙanta kanki ba wani ba".
Maganganun ta na ƙarshe suka tsaya mun a ƙahon zuci, Bilal ya auri wata mace bayan ni, ina addu'ar idan akwai ƙaddarar auren wata mace a rayuwar sa bayan ni ubangiji ya ɗauki raina kafin na ga lokacin domin ko ban mutu ba na tabbatar sai na kamu da ciwon da zai nakasta ni. Ta yaya ma za'a yi Bilal ya so wata bayan ni? Wane irin mugun fata Anty Labiba take mun haka? Mai ya sa a koda yaushe ita bakin ta baya taɓa faɗar alkhairi sai aka sin haka?
Ita ta mun baki akan Bilal, ita ta fara faɗin ko xa na aure shi bazan samu farin cikin da nake kwaɗayi ba gashi da wasa wasa bakin ta ya na neman kamani.
Nayi juyi haɗi da ƙara toshe kunnuwana saboda yanda kukan Al'amin yake neman ya hanani yin tunani mai kyau. Yau da wuri ya fara dan yanzu haka ƙarfe goma da minti biyar na dare. Tashi na yi jin kukan na sa yana ƙaruwa, tun magriba na shiga ɗaki na kwanta da sunan kaina yana mun ciwo amma a zahiri maganganun Anty Labiba na shiga ɗaki na ke ta tusawa a ƙwaƙwalwa ta. Ina buɗe ƙofa Mu'azzam na turowa da Al'amin ɗin a hannun sa ya miƙo mun shi yana cewa
"Au da kika ce idan aka miki zani bayar da kayan zaki yi ashe da gaske kike yi? To yanzu ina sauran ko su ma duk kin bayar da su?"
"Aa suna nan wlh duk ban ma taɓa sakawa ba, shima wancan ɗin ba fa bata na yi ba iya zanin ne shi ma zuwa ta yi ta manto zanin goyo a gida shi ne na bata aro kuma ban san da shi ta tafi ba" na faɗa jin Mama zata balbaleni da faɗa, ashe da na yi shiru ya fiye mun alkhairi ma nan kuwa ta shiga faɗan ta na cewa
"Saboda ba da kuɗin ki kika siya ba ai dole ki ce baki san ta tafi da shi ba, meye amfanin rigar da ɗankwalin toh yanzu? Da kin haɗa kin bata ko banza ta mora tun da sun fi ki sanin darajar sutura. Shashsha, naga uban da zai sake siya miki kayan balle har ki wulaƙanta su" ta tattare waɗanda su Hafiz suka kawo ta ce
"Waɗannan zan riƙe kuwa" na fashe da dariya ina cewa
"Wlh bari na gidan nan duk yan uba sun shiga sun fita sun gurɓata mun ke Mama gaba ɗaya kin koyi faɗa bayan ba halin ki ba ne" bata kula ni ba ta wuce ɗaki ta bar mu da Anty Labiba. Sai bayan isha'i da Anty Labiban zata ta fi ta ke cemun
"Yau ɗin zamu tafi ko se daga baya zaki zo?"
Na bi ta da kallon rashin fahimta, Mama da ta shigo ɗakin ta ce
"Gidan ta zaki je ki zauna kafin mu dawo tun da kin ce ba zaki koma gidan ki ba". Na yi rau da ido na ce
"Amma Abba ya ce na zauna a nan ai"
"To ba zaki zauna ba idan kuma kika cika mun ciki wlh yanzu zaki tattara ki koma gidan ki. Ina dama kin zaɓe shi sama da nan ɗin? Da ya kore ki ya ce ki taho ba share guri kika yi kika zauna ba? Tun da haka kika zaɓawa kan ki ai shikenan, shi dai mutunchi mutum shi yake siyawa kan sa tunda ke kin saryar da naki ai shikenan" Mama ta faɗa cikin fushi tana gamawa kuma ta fice daga ɗakin ta barmu.
Anty Labiba da ke tsaye ta koma ta zauna kusa da ni haɗi da dafa kafaɗa ta, kamar ina jira na fashe da kuka na faɗa jikin ta, ta ce
"Bazan ɓoye miki ba ran Mama a ɓace ya ke da ke Halima amma na lura rashin hankali sam bai bari kin fahimci haka ba"
"Toh ai bata faɗa mun ba" na faɗa cikin kuka. Ta ɗago ni daga jikin ta ta ce
"Ke baki da tunani kenan, baki san abinda kika yi zai ɓata mata rai ba sai ta buɗe baki ta gaya miki? Halima har sai yaushe zaki fara tunani daidai da shekarunki ne?
Yanzu bayan duk rashin mutunchin da Mijinki ya yi kin san kuma labari ya zo kunnuwan su, baki yi tunanin ya kamata ko a waya ne ki kira ki bada haƙuri ba sannan sai yanzu ki iya ɗakko ƙafa ki zo gidan ki ce zaki zauna. Na jinjinawa ƙarfin hali irin naki".
"Ke fa kika ce ko me zai yi mun na yi haƙuri na shanye, kuma na san idan na zo na faɗi wani abu akan Bilal ke zaki fara cewa dama ai kin faɗa" na sake faɗa ina ƙoƙarin tsaida kuka na. Ta yi murmushin da kana kallo zaka san na takaici ne kafin ta ce
"Yanzu ai kin gani da idon ki abin da na faɗa ɗin ko? Kuma saboda kar muyi magana shiyasa kika zaɓi ki nuna masa iyayen ki ba su da mutunchi a idonki zai iya zagin su kuma ki iya cigaba da zama da shi ko?"
"Bilal bai zage ni ba Hajjan su ce, kuma wlh bayan sun tafi ya dawo ya bani haƙuri kuma ko cewa da yayi na taho gida ya gaya mun saboda Hajja ne amma ba har ransa yayi maganar ba" na faɗa, sai ta sake ni ta ce
"Ni wlh yanzu abubuwan da kike yi sun daina bani haushi tausayi kawai kike bani saboda baki san me kike yi ba. Wannan haukan da kike yi ya wuce So Halima you are obsessed with him idan kuma baki yiwa kanki faɗa kin fahimci zahiri ba zaki haukace a banza ranar da kika fahimci Son ma So wani kike yi. Yanzu ke kin yarda da wasan da miji zai fututtuke ya ci miki mutunchi sannan ya dawo daga baya ya ce miki wasa ya ke yi wasan ma kuma ya haɗa har da iyaye a ina ake haka?
Ke ki gwada yi masa irin wasan ki gani idan zaku kwashe lafiya, ba zagi ba, ki gwada ɗaga masa murya ko kuma cikin wasan ki ce masa BANZA kawai ki gani a ranar idan bai sauya miki kamanni kafin ya kawo mana ke ba.
A soyayya akwai sanin ciwon kai Halima, a soyayya akwai sanin martabar kai, a soyayya akwai mutunta kai, akwai aji. So is not do or die affair Halima duk muna soyayya muna da waɗanda muke so amma hakan ba shi ya saka muke banzatar da kanmu duk da sunan So ba zaman ki da ni bai amfana miki komai ba domin babu abinda kika koya. Ba alfahari ba ni na yarda da kaina kuma na san na isa mace. Kin sani da ace sakarya ce ni irin ki da ban kai labari a gidan Saleh ba. Na goga da dangin miji na goga da matan bariki da na riƙe Allah na kuma yi amfani da baiwar da ubangiji ya mun a matsayi na na mace a gaban idonki komai ya zama labari. In da na bari soyayyar sa ta rufe mun ido yanda kike yi a yanzu na bishi a yanda na tarar da shi ƙila yanzu idan ban mutu da baƙin ciki ba da tuni na daɗe da zarewa sai ke akan Bilal da bai wuci jariri a makarantar tantiran Maza ba.
Yau da ace Bilal is reciprocating, yana maida miki martanin abin da kike yi masa tare kuka zauce kuke haukan ku babu mai ce miki dan me? Babu mai ganin baiken ki domin dama ai Hausawa suka ce ka gaida mai gaishe ka amma a nan, ke kaɗai kike kiɗan ki kina rawar ki. Ya mayar da ke wawiya, sai idan buƙatar sa ta tashi yana so ya cuceki ya miki wayo a lokacin ya ke gwada miki kina da amfani a gurin sa da zarar kuma ya samu biyan buƙata shikenan da ke da babu duk ɗaya kuke a wajen sa.
Kalle ki, aure kusan shekara biyu amma kullum jiya i yau babu wani canji a tattare da ke wanda za'a ce kin tsinci wani abu cikin auren soyayyar da kika na ce sai kinyi. Ki kalli ƙawayen ki da kike musu dariya kina ganin sun auri waɗanda basu da ce da su ba, hatta da Hansa'u da kike cewa zata auri sa'an Babanta idan akajera ku dake da kika auri yaro sabon jinin sai an ɗauke ta sau dubu ba'a ɗauki ki ba saboda ta fiki walwala, ta fiki kyan gani da ka kalle ta baka buƙatar a faɗa maka tana cikin farin ciki a gidan auren ta ko ita kaɗai ta ishe ki ishara da ki gane ƙuruciya ba ita bace soyayya a gidan aure, dacen abokin zama shi ne kan gaba.
Yanzu ko sati biyu baki rufa ba haihuwar fari amma tun kina gadon Asibiti yake watangaririya da ke. Mazan kirki ana roƙon su basa so ake ɗauke matan su a tafi da su gida wanka amma me tun yana miki hannun ka mai sanda har ta kai ya fito ƙiri ƙiri ya kore ki wannan wane irin rashin daraja ne?
Yanda mata muke so mu auri miji mai aji haka kowanne namiji yake son samun macen da ta san kanta, kisan kanki a sanda miji ya miki abin farin ciki haka ki san kanki a sanda ya ɓata miki rai amma ba ki zama ballagaza ke son miji duk in da ya ja ki ya watsar nan zaki yi a lissafi na hankali ma kin san dole wata rana ya ƙosa da halin ki. Wallahi idan baki shiga hankalin ba Halima akwai ranar da sai kin ɗora hannu aka kin yi ihu a sanda Bilal ze gwada miki ke ɗin ba komai ba ce a gurin sa, a kan idon ki ze ɗakko mace mai aji da ta san kanta ya riritata a sannan kowa zai zage shi ace ya wulaƙanta ki amma gaskiyar magana ke kika fara wulaƙanta kanki ba wani ba".
Maganganun ta na ƙarshe suka tsaya mun a ƙahon zuci, Bilal ya auri wata mace bayan ni, ina addu'ar idan akwai ƙaddarar auren wata mace a rayuwar sa bayan ni ubangiji ya ɗauki raina kafin na ga lokacin domin ko ban mutu ba na tabbatar sai na kamu da ciwon da zai nakasta ni. Ta yaya ma za'a yi Bilal ya so wata bayan ni? Wane irin mugun fata Anty Labiba take mun haka? Mai ya sa a koda yaushe ita bakin ta baya taɓa faɗar alkhairi sai aka sin haka?
Ita ta mun baki akan Bilal, ita ta fara faɗin ko xa na aure shi bazan samu farin cikin da nake kwaɗayi ba gashi da wasa wasa bakin ta ya na neman kamani.
Nayi juyi haɗi da ƙara toshe kunnuwana saboda yanda kukan Al'amin yake neman ya hanani yin tunani mai kyau. Yau da wuri ya fara dan yanzu haka ƙarfe goma da minti biyar na dare. Tashi na yi jin kukan na sa yana ƙaruwa, tun magriba na shiga ɗaki na kwanta da sunan kaina yana mun ciwo amma a zahiri maganganun Anty Labiba na shiga ɗaki na ke ta tusawa a ƙwaƙwalwa ta. Ina buɗe ƙofa Mu'azzam na turowa da Al'amin ɗin a hannun sa ya miƙo mun shi yana cewa