Sashe 35
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wallahi kawai in na tuna zumunchin da Fadila ta mun shiyasa nake tsaye akan sabgoginta. Yarinyar nan bata ji ƙyashin bani rabon ta na gado nayi sabgogin karatu ba shiyasa ko miliyan nawa zan samu a rayuwa ta nima ba zan ji takaicin kashe mata ba dan ta mun abinda kowa be mun ba cikin yan uwana" Bilal ya sake faɗa, a raina na raya
"Ashe dai kasan me maka" yawan zancen Fadila da irin yanda ya ɗaukaki halaccin da ta masa yasa a kullum nake kyautata masa zaton baze taɓa wofantar dani ko ya manta tawa sadaukarwar a rayuwar sa ba kamar yanda da yawa suke tunanin ze bani kunya.
"Kinga a duniya bayan Hajja, ke da Fadila kune mata biyu da suke da ƙima da daraja a ido na. Har gaban abada ba zan manta hallacin ku ba a kullum kuma ina roƙon Allah daya hore mun abin da zan kamanta muku dan nasan bazan biya ku ba" ya sake faɗa yana matso ni jikin sa. Kaina ya fasu, ban san sanda na fara murmushi ba kamar gaula. Ban taɓa wa Bilal wani abu da fatan ya biya ni wata rana ba. Komai ina masa ne saboda son sa da nakeyi tsakani da Allah amma bazanyi ƙarya ba ina jin matuƙar daɗi a duk sanda ya nuna mun jin daɗin sa kan wani abu da nake masa irin wannan tunasarwar kuma tana sakawa na cire kokonton dake damun zuciya ta na Bilal ya canza daga bigiren dana san shi saboda sababbin ɗabi'un da yake gwada mun a yanzu.
Tuni na watsar da ƙudurin motsa kambu na nuna masa ɓacin raina akan rikicin gangan ɗin da yake mun na biye masa muka shiga filin baje kolin ƙauna. Bayan la'asar ina kwance a falo zazzaɓi na namen dawo mun, Bilal ya shigo daga masallaci gani na a kwance yace
"Ya haka kuma ke da nace ki shirya da an idar da sallah zamu tafi?"
Na yunƙura na zauna ina dafe kaina dake sara mun nace
"Gaskiya ba yau ba, jiya fa cewa Mama nayi bani da lafiya shiyasa muka fasa zuwa kaga ma ƙaryar da nayi ciwon gaske na neman kwantar dani". Zama yayi a gefe na ya ɗora hannun sa a wuya na yace
"Jikin ki yayi zafi, dubaki Anty Labiba tazo yi jiya kenan? Dama nayi mamakin ganin ta haka kawai ita da tun da mukayi aure bata taɓa zuwa ba"
"Allah ne be kawo dalilin zuwan bane ba" na faɗa ina gyara zamana. Ya ɗan ɓata fuska yace
"Ba wani nan nine bata so kika aura ba shiyasa ba zata zo gida na ba" se nayi saurin katse shi da cewa
"Kaima da kake hanani zuwa gidan ta saboda baka son ta ne kenan?"
Ya mun kallo me kama da harara kafin yace
"Ya zanyi nace bana son ƙanwar mahaifiyar ki? Kawai bana jin daɗin yanda bata mun kara ƙarara take nuna bata ra'ayin kasancewar mu tare tun ina neman auren ki. Sannan nasan har yanzu bata yada makamanta ba, zuga ki zata cigaba dayi idan kika je gidan".
"Lallai Bilal, ita kuma Anty Labiba saboda bata da abinyi se ta zauna tana zugani. To ta zugani na kashe aure na ko me? Ribar me zata ci?"
"Ita kuwa zata ci riba tun da wannan soloɓiyon ƙanin mijin nata na sonki kinga burin ta se ya cika ki aure shi" ya faɗa yana wani zare ido. Kallon sa kawai nayi na koma na kwanta dan maganar ta fara hawar mun kai. Beyi shiru ba yaci gaba da cewa
"Yanzu Allah kaɗai yasan me zata je ta faɗa jiya, tun da na gaishe ta naga bata amsa ba nasan ta ƙudurce wani abun ne a ranta". Jin na masa banza ban tanka yasa ya miƙe yana cewa
"Ni bari na tafi toh dan na kira Nasir nace ya shirya ze raka ni mu gaida su Mama zuwa gobe idan kinga zaki iya daga gidan sunan se kije".
Ban amsa ba na da naji shiru ma na zata ya fita duk da banji motsin buɗe ƙofa ba,
"Halims" ya kira ni, na juya ba tare da na amsa ba. Irin kallon daya yaudare ni dashi nayi kaca kaca a ƙaunar sa ya watso mun kafin ya tsugunna gaba na ya ruƙo hannu na yace
"In nemi wata alfarma mana"
"Ta me?" Na faɗa a ƙasan maƙoshi saboda kallon da yake mun duk yasa naji wani iri se yace
"Kin san rigimar Hajja, wai dubu hamsin take nema a hannu na daga yanzu zuwa dare ni kuma wlh account ɗina kaf babu dubu ashirin ma balle ashirin. Gurin Nasir kaɗai nake iya zuwa rancen kuɗi shima kuma cikin buƙatar su yake. Nace mata bani da kuɗi amma bata yarda ba har tana cewa wai bayarwa ne kawai bazanyi ba bata ko dubi kuɗin dana kashe na aikin Fadila ba amma dan nace bani da dubu ashirin take nema tayi fushi"ya ƙarasa kamar zeyi kuka dan har idon sa ya canza.
Har raina naji tausayin sa, na karanci halin Hajjan su maganar Allah mace ce me son abin duniya kuma bata da uzuri akan babu tafi so a duk sanda a buƙaci abu kawai ayi kusan yana daga abun da yasa nake ɗagawa Bilal ƙafa dan nasan yana da nauyin daya fi samun sa akansa.
"Ki agaza mun ki samo mun aron dubu hamsin zuwa ƙarshen wata ayi albashi, akwai ma kuɗin da na rantawa Abubakar satin da za'a shiga ze fitar da kajin sa idan ya bani se ki mayar musu" ya sake faɗa yana matsa hannu na. Kallon sa nayi nace
"Ni yanzu a gurin wa zan ranto maka kuɗi?"
"Haba Halims mutane da yawa mana ga yan uwanki ga ƙawayen ki ko gurin Hansa'u ai ba zaki rasa" se na harare shi nace
"Kuma kawai se na tafi cikin yan uwana ko ƙawaye neman rancen kuɗi kaga ma se a samu nayi dani ace wahala nake sha a gidan ka har na fara yawon neman rance". Se yayi shiru kamar me nazari kafin yace
"Kuma haka ne. Wlh kaina ya kulle sam na rasa mafita shi yasa ma wannan tunanin be zo mun ba. Ni kaina akwai gurin waɗan da idan na tambaya zan samu amma kin san bana son raini ba kowa ne ze fahimci buƙatar matsuwa ta saka ka neman taimako ba se a samu abin gulmar ka a unguwa. Barshi kawai bari naje na bata abin da nake dashi idan yaso su Yaya Amina sa cika mata sauran tun da dama su suka ƙirƙiro bidi'ar yin sunan ba wani ba" ya ƙarasa yana miƙewa tsaye.
Kamar wani maraya ya fara tafiya yana waige na, na koma na kwanta ina danne zuciya ta kar tausayin sa yayi tasiri ya sakani yin abinda banyi niyya na amma ina na kasa. Har ya kai bakin ƙofa na tashi zaune na kira sunan sa, tsayawa yayi. Na yamutsa fuska. Dubu goman da Abba ya bayar aka kawo mun sa wadda Uncle Saleh ya bani jiya har ga Allah na gama lissafin me zanyi dasu wasu kayan jarirai irin na turkey Hansa'u ta turo mun har na zaɓi waɗanda nake ao jira nakeyi na fita na samu wanda zan bawa kuɗin ya tura mun a account na aika mata ga wata lalukar ta faɗo musu dukda a zahiri abin be shafe ni ba amma bazan so ran miji na ya ɓaci akan abin da nake da halin fitar dashi ba. Ba dai zan tambayi kowa ba amma zan masa komai da abinda nake dashi.
Ina dafe kai na shiga ɗaki na fito da rafar sababbin yan ɗari da yan hamsin biyu na haɗa na miƙa masa, karɓa yayi yana kallo na da sigar neman ƙarin baya ni. Na yamutsa fuska nace
"Jiya Abba ya aiko mun da barka da sallah wannan kuma Uncle Saleh ne ya bani, kayi maneji dasu dan gaskiya ni babu wanda zan iya tambaya wasu kuɗi yanzu"
"Allah sarki My Halims da kin barsu ma kawai zanje nace mata ban samu ba faɗa ne kawai zata tayi amma dole ta haƙura tun da dai bazanyi sata na basu ba" ya faɗa yana dawo mun da kuɗin. Ban karɓa ba na juya na zauna ina cewa
"Ka taho mun da mangwaro ko guava idan zaka dawo"
"Allah ya maida miki da dubun su Halims, bari naje ba daɗewa ma zanyi ba zan dawo naji ba'asin wannan ƙyallin goshin da faɗin kwankwason da kika ƙara kwana biyu. Yana yinki dai kamar akwai wani abu da kike ɓoye mun" ya faɗa yana kashe mun ido ɗaya. Murmushi nayi tare da zamewa na kwanta ina ɗaga masa hannu. Yana fita bacci ya kwashe ni ban farka ba kuma se da aka fara kiraye kirayen sallar magriba. A kan center table naga leda da mangwaro harda yalo fari da kore a ciki se farar takarda a ninke na buɗe ta 'i might be late, amma karkiyi bacci ki jira ni please' abin da aka rubuta kenan.
Murmushi na saki wani daɗi ya ratsani dan nasan daren yau kam ze zama na daban ne, kasala da zazzaɓin da nake ji ma duk se na neme su na rasa na tashi ina idar da sallah na shiga shiri dukda bansan da me ze zo ba.
"Ashe dai kasan me maka" yawan zancen Fadila da irin yanda ya ɗaukaki halaccin da ta masa yasa a kullum nake kyautata masa zaton baze taɓa wofantar dani ko ya manta tawa sadaukarwar a rayuwar sa ba kamar yanda da yawa suke tunanin ze bani kunya.
"Kinga a duniya bayan Hajja, ke da Fadila kune mata biyu da suke da ƙima da daraja a ido na. Har gaban abada ba zan manta hallacin ku ba a kullum kuma ina roƙon Allah daya hore mun abin da zan kamanta muku dan nasan bazan biya ku ba" ya sake faɗa yana matso ni jikin sa. Kaina ya fasu, ban san sanda na fara murmushi ba kamar gaula. Ban taɓa wa Bilal wani abu da fatan ya biya ni wata rana ba. Komai ina masa ne saboda son sa da nakeyi tsakani da Allah amma bazanyi ƙarya ba ina jin matuƙar daɗi a duk sanda ya nuna mun jin daɗin sa kan wani abu da nake masa irin wannan tunasarwar kuma tana sakawa na cire kokonton dake damun zuciya ta na Bilal ya canza daga bigiren dana san shi saboda sababbin ɗabi'un da yake gwada mun a yanzu.
Tuni na watsar da ƙudurin motsa kambu na nuna masa ɓacin raina akan rikicin gangan ɗin da yake mun na biye masa muka shiga filin baje kolin ƙauna. Bayan la'asar ina kwance a falo zazzaɓi na namen dawo mun, Bilal ya shigo daga masallaci gani na a kwance yace
"Ya haka kuma ke da nace ki shirya da an idar da sallah zamu tafi?"
Na yunƙura na zauna ina dafe kaina dake sara mun nace
"Gaskiya ba yau ba, jiya fa cewa Mama nayi bani da lafiya shiyasa muka fasa zuwa kaga ma ƙaryar da nayi ciwon gaske na neman kwantar dani". Zama yayi a gefe na ya ɗora hannun sa a wuya na yace
"Jikin ki yayi zafi, dubaki Anty Labiba tazo yi jiya kenan? Dama nayi mamakin ganin ta haka kawai ita da tun da mukayi aure bata taɓa zuwa ba"
"Allah ne be kawo dalilin zuwan bane ba" na faɗa ina gyara zamana. Ya ɗan ɓata fuska yace
"Ba wani nan nine bata so kika aura ba shiyasa ba zata zo gida na ba" se nayi saurin katse shi da cewa
"Kaima da kake hanani zuwa gidan ta saboda baka son ta ne kenan?"
Ya mun kallo me kama da harara kafin yace
"Ya zanyi nace bana son ƙanwar mahaifiyar ki? Kawai bana jin daɗin yanda bata mun kara ƙarara take nuna bata ra'ayin kasancewar mu tare tun ina neman auren ki. Sannan nasan har yanzu bata yada makamanta ba, zuga ki zata cigaba dayi idan kika je gidan".
"Lallai Bilal, ita kuma Anty Labiba saboda bata da abinyi se ta zauna tana zugani. To ta zugani na kashe aure na ko me? Ribar me zata ci?"
"Ita kuwa zata ci riba tun da wannan soloɓiyon ƙanin mijin nata na sonki kinga burin ta se ya cika ki aure shi" ya faɗa yana wani zare ido. Kallon sa kawai nayi na koma na kwanta dan maganar ta fara hawar mun kai. Beyi shiru ba yaci gaba da cewa
"Yanzu Allah kaɗai yasan me zata je ta faɗa jiya, tun da na gaishe ta naga bata amsa ba nasan ta ƙudurce wani abun ne a ranta". Jin na masa banza ban tanka yasa ya miƙe yana cewa
"Ni bari na tafi toh dan na kira Nasir nace ya shirya ze raka ni mu gaida su Mama zuwa gobe idan kinga zaki iya daga gidan sunan se kije".
Ban amsa ba na da naji shiru ma na zata ya fita duk da banji motsin buɗe ƙofa ba,
"Halims" ya kira ni, na juya ba tare da na amsa ba. Irin kallon daya yaudare ni dashi nayi kaca kaca a ƙaunar sa ya watso mun kafin ya tsugunna gaba na ya ruƙo hannu na yace
"In nemi wata alfarma mana"
"Ta me?" Na faɗa a ƙasan maƙoshi saboda kallon da yake mun duk yasa naji wani iri se yace
"Kin san rigimar Hajja, wai dubu hamsin take nema a hannu na daga yanzu zuwa dare ni kuma wlh account ɗina kaf babu dubu ashirin ma balle ashirin. Gurin Nasir kaɗai nake iya zuwa rancen kuɗi shima kuma cikin buƙatar su yake. Nace mata bani da kuɗi amma bata yarda ba har tana cewa wai bayarwa ne kawai bazanyi ba bata ko dubi kuɗin dana kashe na aikin Fadila ba amma dan nace bani da dubu ashirin take nema tayi fushi"ya ƙarasa kamar zeyi kuka dan har idon sa ya canza.
Har raina naji tausayin sa, na karanci halin Hajjan su maganar Allah mace ce me son abin duniya kuma bata da uzuri akan babu tafi so a duk sanda a buƙaci abu kawai ayi kusan yana daga abun da yasa nake ɗagawa Bilal ƙafa dan nasan yana da nauyin daya fi samun sa akansa.
"Ki agaza mun ki samo mun aron dubu hamsin zuwa ƙarshen wata ayi albashi, akwai ma kuɗin da na rantawa Abubakar satin da za'a shiga ze fitar da kajin sa idan ya bani se ki mayar musu" ya sake faɗa yana matsa hannu na. Kallon sa nayi nace
"Ni yanzu a gurin wa zan ranto maka kuɗi?"
"Haba Halims mutane da yawa mana ga yan uwanki ga ƙawayen ki ko gurin Hansa'u ai ba zaki rasa" se na harare shi nace
"Kuma kawai se na tafi cikin yan uwana ko ƙawaye neman rancen kuɗi kaga ma se a samu nayi dani ace wahala nake sha a gidan ka har na fara yawon neman rance". Se yayi shiru kamar me nazari kafin yace
"Kuma haka ne. Wlh kaina ya kulle sam na rasa mafita shi yasa ma wannan tunanin be zo mun ba. Ni kaina akwai gurin waɗan da idan na tambaya zan samu amma kin san bana son raini ba kowa ne ze fahimci buƙatar matsuwa ta saka ka neman taimako ba se a samu abin gulmar ka a unguwa. Barshi kawai bari naje na bata abin da nake dashi idan yaso su Yaya Amina sa cika mata sauran tun da dama su suka ƙirƙiro bidi'ar yin sunan ba wani ba" ya ƙarasa yana miƙewa tsaye.
Kamar wani maraya ya fara tafiya yana waige na, na koma na kwanta ina danne zuciya ta kar tausayin sa yayi tasiri ya sakani yin abinda banyi niyya na amma ina na kasa. Har ya kai bakin ƙofa na tashi zaune na kira sunan sa, tsayawa yayi. Na yamutsa fuska. Dubu goman da Abba ya bayar aka kawo mun sa wadda Uncle Saleh ya bani jiya har ga Allah na gama lissafin me zanyi dasu wasu kayan jarirai irin na turkey Hansa'u ta turo mun har na zaɓi waɗanda nake ao jira nakeyi na fita na samu wanda zan bawa kuɗin ya tura mun a account na aika mata ga wata lalukar ta faɗo musu dukda a zahiri abin be shafe ni ba amma bazan so ran miji na ya ɓaci akan abin da nake da halin fitar dashi ba. Ba dai zan tambayi kowa ba amma zan masa komai da abinda nake dashi.
Ina dafe kai na shiga ɗaki na fito da rafar sababbin yan ɗari da yan hamsin biyu na haɗa na miƙa masa, karɓa yayi yana kallo na da sigar neman ƙarin baya ni. Na yamutsa fuska nace
"Jiya Abba ya aiko mun da barka da sallah wannan kuma Uncle Saleh ne ya bani, kayi maneji dasu dan gaskiya ni babu wanda zan iya tambaya wasu kuɗi yanzu"
"Allah sarki My Halims da kin barsu ma kawai zanje nace mata ban samu ba faɗa ne kawai zata tayi amma dole ta haƙura tun da dai bazanyi sata na basu ba" ya faɗa yana dawo mun da kuɗin. Ban karɓa ba na juya na zauna ina cewa
"Ka taho mun da mangwaro ko guava idan zaka dawo"
"Allah ya maida miki da dubun su Halims, bari naje ba daɗewa ma zanyi ba zan dawo naji ba'asin wannan ƙyallin goshin da faɗin kwankwason da kika ƙara kwana biyu. Yana yinki dai kamar akwai wani abu da kike ɓoye mun" ya faɗa yana kashe mun ido ɗaya. Murmushi nayi tare da zamewa na kwanta ina ɗaga masa hannu. Yana fita bacci ya kwashe ni ban farka ba kuma se da aka fara kiraye kirayen sallar magriba. A kan center table naga leda da mangwaro harda yalo fari da kore a ciki se farar takarda a ninke na buɗe ta 'i might be late, amma karkiyi bacci ki jira ni please' abin da aka rubuta kenan.
Murmushi na saki wani daɗi ya ratsani dan nasan daren yau kam ze zama na daban ne, kasala da zazzaɓin da nake ji ma duk se na neme su na rasa na tashi ina idar da sallah na shiga shiri dukda bansan da me ze zo ba.