Sashe 81
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kanki ƙalau kuwa Halims yau ni kike faɗin baki son gani na naki son jin muryata ko dai gamo kikayi da Aljanu?" Ya faɗa yana ƙoƙarin kama fuskata. Cikin zafin nama na fizge take kuma na ɗaga hannu na sauke masa mari a kuncinsa kafin na miƙe tsaye cikin kuka da hargagi nace
"La fitar mun daga ɗaki Bilal ka fita idan ba haka zan maka abinda har duniya ta naɗe na zaka manta da ni ba".
Ya miƙe tsaye cikin tsananin mamakin abinda na aikata masa yana dafe da gurin da na mare shin yayi taku biyu yaja baya yana kallona amma ya kasa cewa komai. Hargagina ya farkar da Sharifa ta ƙwala ihu sai ya nufeta nayi saurin bangaje shi na ɗauke ta ina cewa
"Koda wasa kada ka kuskura ƙaramin hannunka ya taɓa mun ya, iya zunubin daka ɗiba ya ƙare a kanka Allah ya isa tsakani na da kai Bilal kuma wlh har idan mugun halinka ya shafi yayana bazan taɓa ƙyale ka ba" na ƙarasa ina kaiwa ƙasa dan gaba ɗaya jikina babu sauran kuzari. Har ya buɗe baki zai sake mun magana idon sa ya sauke akan wayar sa dake ajiye a ƙasa dan haka ya tsugunna ya ɗakko, ina kallonsa ya buɗe, a cikin chat ɗin nasu na barta kan wani video da ta turo masa ina kallo ya runtse idonsa haɗi da dunƙule hannun sa kamar zai kai naushi kafin ya saci kallona.
Nayi murmushin takaici na ce
"Kaji kunya Bilal wlh kaji kunya. Mumini a fuska ashe a zuciya tantirin ɗan is...."
"Ya ishe ki Halima kada ki kurkura ki furta abinda yake kan harshen ki idan ba haka ba sai kinyi nadama wlh, kar kiga kin mareni na rabu dake na ɗauka bakya cikin hayyacin ki ne amma yanzu tunda na lura kina sane kada kiyi gigin kawo mun wani hauka dan zanyi maganinki ne" ya dakatar dani cikin tsawa sai dai duk maganar da yayi bai bari mun haɗa ido ba yayi ta ne yana kallon wani guri daban.
[4/4, 9:17 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 34*
Kwanaki biyu da suka biyo baya nayi su ne cikin taimakon ubangiji domin a kowacce daƙiƙa ji nakeyi tamkar numfashi na zai iya yankewa. Babu abinda yake shiga cikina banda ruwa da paracetamol da nake ta banka saboda azababben ciwon da kaina kama, ikon Allah kaɗai yake riƙe dani akan ƙafafuna hatta yaran ma game game kawai nake musu duk abinda hannu ya kai nake haɗawa na basu su ci.
Nayi kuka har hawayena sun ƙafe ya zama sai na zuci nakeyi, a duk sanda na tuna abinda naji kuma na gani dangane da Bilal sai inji na tsani kaina. Ban san ta inda na gaza ba, ba yabon kai ba na sani ko a cikin mata samun irina mai kula da tsaftar jikinta ciki da waje sai an tona. A koda yaushe na kanyi ƙoƙarin na kasance a yanda idonsa ba zai taɓa ganin wani abu da bazai so ba a tareda ni. Bana wasa da kyaran jikina a duk sanda na samu kuɗi kafin nayi komai sai na ware wanda zan siyi duk abubuwan da nake buƙata na amfanin kaina kuma saboda shi. Ina ɗaukar last kwabo na na siya abun daɗi naci saboda jikina ya samar da ni'imar da zata gamsar dashi, ban taɓa damuwa da rashin yi biyamun buƙatu na yau da kullum da yakeyi ba ni dai burina a kullum nayi abunda zan faranta masa amma ace ya rasa abinda zai saka mun da shi sai wannan?
Wai tun yaushe ma yake aikata hakan ba tareda na sani ba? Tun kafin muyi aure dama haka yake ko kuwa daga baya ne ya fara? Bani da mai bani amsa amma abinda nafi ƙarfafawa shine bayan aurenmu ko ma in ce bayan na haihu tunda shine lokacin daya fara zaryar zuwa Abuja da sunan aiki ashe abinda yake kai shi kenan. Na tuna lokacin da na tafi gida wankan Al'amin sanda yazo ganinmu bai ko nuna ɗoki ko alamar yayi kewata ba har naji haushi a lokacin ashe dalili kenan. Tun bayan sannan dama ya koma part ɗin sa gaba ɗaya da kwana kuma daga lokacin ya auri chat koda yaushe ya zauna wayarsa na hannu yana danne danne ashe dalilin kenan.
Babban abinda ya sake bani mamaki dashi ta yanda tunda ya fita daga ɗakina wancen daren tsayin kwana biyun bai sake tako ko da kan barander ta ba balle ya shigo yayi mun magana ko yayi mun wani bayani da zai kare kansa balle har ya rarrasheni ko ya nuna nadama akan abinda ya aikata ɗin. Ko da yake ni kaina bansan zaman me nakeyi a cikin gidan ba domin a yanda bake jin zuciyata bai kamata ace na ƙara kwana a ƙarƙashin inuwa ɗaya da shi ba amma kuma na rasa ƙwarin guiwar yin hakan. Allah ya sani ina Son Bilal irin Son da zuwa yanzu na yarda jarabawa ce a tattare dani a kusa ko a nesa kuma bana fatan wani abu da zai rabani dashi amma a yanzu ban san me nakeji akan sa ba.
Da azahar ina kwance a tsakiyar falo ina juyi saboda azabar ciwon da cikina ya tasar mun da nasan yana da alaƙa da horon yunwar da nake yiwa kaina. Al'amin dana aika ya kirawo mun Maman Yusuf suka shigo tare, tana ganina ta ƙaraso da sauri tana salati haɗi da cewa
"Na shiga uku mai ya sameki Halima?" Da hannu na nuna mata cikina, ta ɗago ni zaune sai ta sake ɗaukar salatin daya fi na farko tace
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un kin ganki kuwa Halima? Kwananki nawa a kwance? Ina shi Baban nasu da ya barki haka sai kin mutu sannan zai kira iyayenki ya basu gawa ko me?"
Jin ta tsaya kwakwazo ya saka na kamo hannunta daƙyar na ɗora akan cikina da muryata da bata fita nace
"Cikina mutuwa zanyi". Sai ta miƙe jik na rawa tana cewa
"Ba zaki mutu ba in sha Allahu bari na kira Sadi mu tafi asibiti" ta fita kusan da gudu, ni dai ba zan ga sanda ta dawo ba haka dishi dishi naji sanda aka kwasheni aka fita dani daga lokacin ban sake sanin komai ba sai farkawa nayi na ganni a gadon asibiti Bilal na zaune a gefena. Mayar da ido na nayi na runtse bayan dana fahimci a inda nake, ya miƙe tsaye haɗi da kamo hannuna yana cewa
"Kin tashi Halima?" Ban amsa ba sai janye hannun da nayi daga nasa na yunƙura na gyara kwanciya ta ta hanyar bashi baya, ina jin sa ya sauke ajiyar zuciya kafin ya fita daga ɗakin ba'a daɗe ba suka dawo tareda likita. Likitan ne ya kira sunana dan haka na gyara kwanciya ta ba tareda na amsa ba ya sake maimaitawa yana cewa
"Halima bakya ji nane?"
"Ina jinka" na bashi amsa cikin muryar da bata fita sosai. Yace
"Masha Allah sannu kinji, ina ne yake miki ciwo yanzu?" Sai na girgiza masa kai alamar babu. Matsowa yayi ya saka abun awon bugun zuciya a ƙirji na kafin ya cire ya ɗauki abun auna Bp ya saka mun a hannu sai da ya gama sannan ya kalli Bilal yace
"Jinin ya sauka sosai yanda ya kamata bata cikin kowanne haɗari yanzu". Bansan sanda na saki tsaki ba jin Bilal ɗin yana cewa
"Alhamdulillah har hankalina ya kwanta" duk su biyun suka kalleni ni ko dama basu nake kallo ba, likitan ya sake cewa
"Bari naje idan ruwan ya ƙare sai kayiwa Nurse magana tazo ta cire mata ina ganin za'a sallame ku ma ba sai ta kwana ba tunda jikin yayi sauƙi, ni zan shiga wata theater yanzu idan mun gama zan sake zagayowa sai kayi mata bayani kuma" ya faɗa yana dafa kafaɗar Bilal ɗin. Bayan fitar Dr ya koma ya zauna kan kujerar daya tashi cikin lafazin da a baya nake so yake kuma jefani cikin shauƙi da begen sa ya ce
"Faɗuwar da kikayi ɗazu kafin muzo Asibiti kika fara bleeding, toh bayan mun iso da suka gwada suka ce kina da ciki kusan wata uku" sai yayi shiru. Na gyara kwanciya ta na zuba masa ido ina so naji ƙarshen maganar tasa, wai ina da ciki, a yaushe nake da cikin har kusan wata uku amma ban sani ba? Jin yayi shiru ya sunkuyar da kai yasa nayi ƙarfin halin cewa
"Sai me ya faru daga nan toh?" Ya kamo hannun na fizge haɗi da jefa masa wani kallo sai ya matsa ya ce
"Dr yace a yanayin da kike barin cikin zai iya zame miki matsala shine na saka hannu aka ƙarasa fitar dashi dan dama ya rigada ya lalace". Ban san sanda na yi dariyar da kana ji zaka san ta zallar takaici da baƙin ciki bace na ce
"Ai dama na saba rainon cikin cikin ƙunci da rashin lafiya ko ka manta? Gara dai ka faɗa mun gaskiya baka buƙatar cikin shiyasa kace a cire shi kuma hakan da kayi ba laifi bane domin ko ba'a cire yanzu ba nima idan na sani ba zan barshi ba dan ba zan sake yarda na haɗa zuri'a da Maƙaryaciya, Maha'inci kuma Mazinaci mara tsoron Allah irinka ba" na ƙarasa ina kallon cikin idon sa. Take idanunsa suka canza launi, ya nuna kansa da yatsa ya ce
"Ni kike jifa da kalmar Zina Halima?"
"Karya nayi ba halinka bane?" Na faɗa ina kallon sa tar babu alamar tsoro ko nadamar hakan, sai ya miƙe tsaye, da fari na ɗauka zai rufeni da duka ne ko kuma ya mareni amma sai naga yaja da baya yana huci kamar wanda kunama ta harba, hakan ya bani damar cigaba da cewa
"La fitar mun daga ɗaki Bilal ka fita idan ba haka zan maka abinda har duniya ta naɗe na zaka manta da ni ba".
Ya miƙe tsaye cikin tsananin mamakin abinda na aikata masa yana dafe da gurin da na mare shin yayi taku biyu yaja baya yana kallona amma ya kasa cewa komai. Hargagina ya farkar da Sharifa ta ƙwala ihu sai ya nufeta nayi saurin bangaje shi na ɗauke ta ina cewa
"Koda wasa kada ka kuskura ƙaramin hannunka ya taɓa mun ya, iya zunubin daka ɗiba ya ƙare a kanka Allah ya isa tsakani na da kai Bilal kuma wlh har idan mugun halinka ya shafi yayana bazan taɓa ƙyale ka ba" na ƙarasa ina kaiwa ƙasa dan gaba ɗaya jikina babu sauran kuzari. Har ya buɗe baki zai sake mun magana idon sa ya sauke akan wayar sa dake ajiye a ƙasa dan haka ya tsugunna ya ɗakko, ina kallonsa ya buɗe, a cikin chat ɗin nasu na barta kan wani video da ta turo masa ina kallo ya runtse idonsa haɗi da dunƙule hannun sa kamar zai kai naushi kafin ya saci kallona.
Nayi murmushin takaici na ce
"Kaji kunya Bilal wlh kaji kunya. Mumini a fuska ashe a zuciya tantirin ɗan is...."
"Ya ishe ki Halima kada ki kurkura ki furta abinda yake kan harshen ki idan ba haka ba sai kinyi nadama wlh, kar kiga kin mareni na rabu dake na ɗauka bakya cikin hayyacin ki ne amma yanzu tunda na lura kina sane kada kiyi gigin kawo mun wani hauka dan zanyi maganinki ne" ya dakatar dani cikin tsawa sai dai duk maganar da yayi bai bari mun haɗa ido ba yayi ta ne yana kallon wani guri daban.
[4/4, 9:17 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 34*
Kwanaki biyu da suka biyo baya nayi su ne cikin taimakon ubangiji domin a kowacce daƙiƙa ji nakeyi tamkar numfashi na zai iya yankewa. Babu abinda yake shiga cikina banda ruwa da paracetamol da nake ta banka saboda azababben ciwon da kaina kama, ikon Allah kaɗai yake riƙe dani akan ƙafafuna hatta yaran ma game game kawai nake musu duk abinda hannu ya kai nake haɗawa na basu su ci.
Nayi kuka har hawayena sun ƙafe ya zama sai na zuci nakeyi, a duk sanda na tuna abinda naji kuma na gani dangane da Bilal sai inji na tsani kaina. Ban san ta inda na gaza ba, ba yabon kai ba na sani ko a cikin mata samun irina mai kula da tsaftar jikinta ciki da waje sai an tona. A koda yaushe na kanyi ƙoƙarin na kasance a yanda idonsa ba zai taɓa ganin wani abu da bazai so ba a tareda ni. Bana wasa da kyaran jikina a duk sanda na samu kuɗi kafin nayi komai sai na ware wanda zan siyi duk abubuwan da nake buƙata na amfanin kaina kuma saboda shi. Ina ɗaukar last kwabo na na siya abun daɗi naci saboda jikina ya samar da ni'imar da zata gamsar dashi, ban taɓa damuwa da rashin yi biyamun buƙatu na yau da kullum da yakeyi ba ni dai burina a kullum nayi abunda zan faranta masa amma ace ya rasa abinda zai saka mun da shi sai wannan?
Wai tun yaushe ma yake aikata hakan ba tareda na sani ba? Tun kafin muyi aure dama haka yake ko kuwa daga baya ne ya fara? Bani da mai bani amsa amma abinda nafi ƙarfafawa shine bayan aurenmu ko ma in ce bayan na haihu tunda shine lokacin daya fara zaryar zuwa Abuja da sunan aiki ashe abinda yake kai shi kenan. Na tuna lokacin da na tafi gida wankan Al'amin sanda yazo ganinmu bai ko nuna ɗoki ko alamar yayi kewata ba har naji haushi a lokacin ashe dalili kenan. Tun bayan sannan dama ya koma part ɗin sa gaba ɗaya da kwana kuma daga lokacin ya auri chat koda yaushe ya zauna wayarsa na hannu yana danne danne ashe dalilin kenan.
Babban abinda ya sake bani mamaki dashi ta yanda tunda ya fita daga ɗakina wancen daren tsayin kwana biyun bai sake tako ko da kan barander ta ba balle ya shigo yayi mun magana ko yayi mun wani bayani da zai kare kansa balle har ya rarrasheni ko ya nuna nadama akan abinda ya aikata ɗin. Ko da yake ni kaina bansan zaman me nakeyi a cikin gidan ba domin a yanda bake jin zuciyata bai kamata ace na ƙara kwana a ƙarƙashin inuwa ɗaya da shi ba amma kuma na rasa ƙwarin guiwar yin hakan. Allah ya sani ina Son Bilal irin Son da zuwa yanzu na yarda jarabawa ce a tattare dani a kusa ko a nesa kuma bana fatan wani abu da zai rabani dashi amma a yanzu ban san me nakeji akan sa ba.
Da azahar ina kwance a tsakiyar falo ina juyi saboda azabar ciwon da cikina ya tasar mun da nasan yana da alaƙa da horon yunwar da nake yiwa kaina. Al'amin dana aika ya kirawo mun Maman Yusuf suka shigo tare, tana ganina ta ƙaraso da sauri tana salati haɗi da cewa
"Na shiga uku mai ya sameki Halima?" Da hannu na nuna mata cikina, ta ɗago ni zaune sai ta sake ɗaukar salatin daya fi na farko tace
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un kin ganki kuwa Halima? Kwananki nawa a kwance? Ina shi Baban nasu da ya barki haka sai kin mutu sannan zai kira iyayenki ya basu gawa ko me?"
Jin ta tsaya kwakwazo ya saka na kamo hannunta daƙyar na ɗora akan cikina da muryata da bata fita nace
"Cikina mutuwa zanyi". Sai ta miƙe jik na rawa tana cewa
"Ba zaki mutu ba in sha Allahu bari na kira Sadi mu tafi asibiti" ta fita kusan da gudu, ni dai ba zan ga sanda ta dawo ba haka dishi dishi naji sanda aka kwasheni aka fita dani daga lokacin ban sake sanin komai ba sai farkawa nayi na ganni a gadon asibiti Bilal na zaune a gefena. Mayar da ido na nayi na runtse bayan dana fahimci a inda nake, ya miƙe tsaye haɗi da kamo hannuna yana cewa
"Kin tashi Halima?" Ban amsa ba sai janye hannun da nayi daga nasa na yunƙura na gyara kwanciya ta ta hanyar bashi baya, ina jin sa ya sauke ajiyar zuciya kafin ya fita daga ɗakin ba'a daɗe ba suka dawo tareda likita. Likitan ne ya kira sunana dan haka na gyara kwanciya ta ba tareda na amsa ba ya sake maimaitawa yana cewa
"Halima bakya ji nane?"
"Ina jinka" na bashi amsa cikin muryar da bata fita sosai. Yace
"Masha Allah sannu kinji, ina ne yake miki ciwo yanzu?" Sai na girgiza masa kai alamar babu. Matsowa yayi ya saka abun awon bugun zuciya a ƙirji na kafin ya cire ya ɗauki abun auna Bp ya saka mun a hannu sai da ya gama sannan ya kalli Bilal yace
"Jinin ya sauka sosai yanda ya kamata bata cikin kowanne haɗari yanzu". Bansan sanda na saki tsaki ba jin Bilal ɗin yana cewa
"Alhamdulillah har hankalina ya kwanta" duk su biyun suka kalleni ni ko dama basu nake kallo ba, likitan ya sake cewa
"Bari naje idan ruwan ya ƙare sai kayiwa Nurse magana tazo ta cire mata ina ganin za'a sallame ku ma ba sai ta kwana ba tunda jikin yayi sauƙi, ni zan shiga wata theater yanzu idan mun gama zan sake zagayowa sai kayi mata bayani kuma" ya faɗa yana dafa kafaɗar Bilal ɗin. Bayan fitar Dr ya koma ya zauna kan kujerar daya tashi cikin lafazin da a baya nake so yake kuma jefani cikin shauƙi da begen sa ya ce
"Faɗuwar da kikayi ɗazu kafin muzo Asibiti kika fara bleeding, toh bayan mun iso da suka gwada suka ce kina da ciki kusan wata uku" sai yayi shiru. Na gyara kwanciya ta na zuba masa ido ina so naji ƙarshen maganar tasa, wai ina da ciki, a yaushe nake da cikin har kusan wata uku amma ban sani ba? Jin yayi shiru ya sunkuyar da kai yasa nayi ƙarfin halin cewa
"Sai me ya faru daga nan toh?" Ya kamo hannun na fizge haɗi da jefa masa wani kallo sai ya matsa ya ce
"Dr yace a yanayin da kike barin cikin zai iya zame miki matsala shine na saka hannu aka ƙarasa fitar dashi dan dama ya rigada ya lalace". Ban san sanda na yi dariyar da kana ji zaka san ta zallar takaici da baƙin ciki bace na ce
"Ai dama na saba rainon cikin cikin ƙunci da rashin lafiya ko ka manta? Gara dai ka faɗa mun gaskiya baka buƙatar cikin shiyasa kace a cire shi kuma hakan da kayi ba laifi bane domin ko ba'a cire yanzu ba nima idan na sani ba zan barshi ba dan ba zan sake yarda na haɗa zuri'a da Maƙaryaciya, Maha'inci kuma Mazinaci mara tsoron Allah irinka ba" na ƙarasa ina kallon cikin idon sa. Take idanunsa suka canza launi, ya nuna kansa da yatsa ya ce
"Ni kike jifa da kalmar Zina Halima?"
"Karya nayi ba halinka bane?" Na faɗa ina kallon sa tar babu alamar tsoro ko nadamar hakan, sai ya miƙe tsaye, da fari na ɗauka zai rufeni da duka ne ko kuma ya mareni amma sai naga yaja da baya yana huci kamar wanda kunama ta harba, hakan ya bani damar cigaba da cewa