← Book details Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 158

Sashe 45

Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tun daren jiya nake ji na ba yanda na saba ba; yau ɗin mun tashi da walwala a gidan dan a ɗakin Bilal na kwana kusan kwana goma kenan tun bayan dawowar sa ya ƙaurace mun duk saboda Amirah. Se da ya fita aiki sannan koma na kwanta ina jin ciwon marar dake tsikarata idan ya tsinka sakan biyu uku kuma se ya sake ni shikenan se wani lokaci. Tunani nayi ko didimar da muka sha ce ta janyo dan daman nasan dole zanji jiki saboda yanda dani dashi ɗin duk muka manta da cikin gashi yanzu ni nake ji a jiki na.

Sanin se yamma ze dawo da Amirah ta tambaye ni me nake so naci nace ta mana taliya da manja; yar murji ce da jiya ta taho mana da ita daga gida. Ina bacci naji kamar ana shafa fuskata, hankali na buɗe ido naci karo da Bilal dake durƙushe kaina yana mun murmushi. Hanci na yaja yana cewa
"Sleepy head; tunda na tafi kike bacci har ƙarfe uku".
Yunƙurawa nayi na tashi ya taimaka mun nace
"Yau ka dawo da wuri" yana cire maɓallin rigar sa yace
"Gudowa nayi, duk kin tara mun gajiya so kawai nake na kwanta na huta" ya faɗa yana kashe mun ido ɗaya. Kasa nayi da kaina ina murmushi kafin na sauke ƙafafu na ƙasa ina cije leɓe saboda wani sharp ciwo daya ziyarce ni lokaci ɗaya kuma ya baje.

"Yunwa nake ji Halims me kuka dafa?" Ya faɗa yana shafa cikin sa. Na kalle shi, kamar in ce masa ai yasan cefanen mu ya ƙare be siyo ba kuma be bada kuɗin siyowa ba amma bana so nayi ruining ɗan farincikin da muka samu jiya zuwa yau se kawai nace
"Taliyar Hausa ce; bari nayi sallah lokaci na tafiya se na zuba maka" na ƙarasa ina nufar banɗaki. Yamutsa fuska yayi kafin yace
"Bazan iya jira ba gaskiya yunwa nake ji sosai"
"To bari nayi fitsari" na sake faɗa ina shigewa ciki. Daƙyar na miƙe bayan nayi fitsarin saboda yanda naji ɗan ciki na ya takure mun a mara kamar yana danno ni. Alwala nayi na fito ina dafa bango, ganin baya falo yasa na ƙwalawa Amirah kira ta fito daga ɗaya ɗakin da alama bacci ma takeyi se nace mata ta haɗawa Bilal abinci zanyi sallah na koma ciki.

A zaune na tada sallar dan bazan iya tsayuwa ba, ina raka'a ta uku na jiyo hargagin Bilal; bana jin me yake cewa se tashin muryar sa kawai kafin na jiyo ƙarar buga ƙofa bam. Ban ko tsaya addu'a ba ina sallamewa na miƙe daƙyar ina dafe baya na da ya ɗauki ciwo na fita falon; da fasasshen tangaran na fara cin karo se taliya da manja sunyi kaca kaca akan milk ɗin center carpet ɗina. Na buɗe baki zan kira Amirah se gata ta fito daga ɗaki tana jan akwatin ta fuska shaɓe shaɓe da hawaye kafin nace wani abu ta riga ni da cewa
"Wallahi tallahi darajarki kawai yaci, badai ya zagi ubana a cikin gidan sa yana ganin yaci banza ba? Allah yasa yayi gigin zuwa gidanmu wallahi se na nuna masa nima na iya rashin kunya" ta faɗa cikin kuka.

"Ke Amirah baki da hankali har tinƙaho ma kike da kin iya rashin kunya kamar wata me faɗar abin arziƙi wai ma tukunna dawa kike?" Na dakatar da ita. Ba tare da shakkar komai ba tace
"Dawannan butulun mijin naki da be dan halacci ba mana. Wai saboda na kawo masa taliya shine ya jefe ni da farantin ba dan Allah ya saka na goce ba ƙila da yanzu shirin jana'izata ake ya yanka mun wuya har yana zagin Abban mu yana ce masa matsiyaci mun zo zamu shafa masa tsiya a gida bayan shine babban matsiya ci..." Kafin ta dire na kwashe ta da marin da se bayan na aikata kuma nadamar yin sa ta kamani; dakewa nayi na shiga yi mata faɗa ina cewa

"Tarbiyyar da kika koyo a boarding ɗin kenan ta raina mutane saboda baki da mutunchi a gabana kike cewa miji na matsiyaci?"
"Ubana fa ya zaga; kenan kin bi bayan mijin ki ko?" Ta faɗa tsabar yanda take jan kuka da magana a haɗe kamar numfashin ta ze ɗauke.
"Zo ki fita daga gidan nan kafin na karya ki dan abu ta kazan ubanki" Bilal daya shigo yana naɗe belt a hannun sa ya faɗa; Amirah ta zabura cike da rashin kunya tace
"Badai ubana ba wlh" se yayiwo kanta na shiga tsakiyar su ina cewa

"Meye haka Bilal da Amirah zakayi faɗa saboda zubar da girma wannan wane irin abu ne?"

"Matsa mun Halima ko in haɗa dake da ita na koya muku tarbiyyar da ba'a muku a gida ba, ni wannan tatsitaiyar yarinyar zata cewa matsiyaci kina tsaye kina kallon ta har kizo mun da wata maganar banza? Da Allah malama matsa tun baki ja nayi abin da za'a ɗaure ni ba" ya faɗa yana ture ni gefe; dake ban zata ba se na tafi luu Allah ya taimake ni na dafe kujera Amirah ma ta riƙe ni. Belt ɗin ya ɗaga da niyyar dukan ta duk da azabar da nake ji saboda faɗuwar bazatan dana kusan yi ta tsinkar mun da zuciya haka na riƙe belt ɗin ina kuka nace

"Wlh se dai ka dake ni; har idan ka dakar mun ƙanwa se kayi nadamar hakan Bilal ina mai tabbatar maka da haka"

"Ni kike cewa zaki zaka nayi nadama Halima saboda zan hukunta mara tarbiyyar ƙanwar ki?" Ya faɗa yana nuna kansa idanun sa suna sake rikiɗewa da ɓacin rai. A ƙasa ya jefar da belt ɗin ya nufi ƙofa yana cewa
"Wallahi tallahi har idan na dawo na same ta a cikin gidana se na mata abinda idan an ga dama a kaini kurkukun ƙasan ruwa" yanda yayi furucin ba ƙaramin tsorata nayi ba; jiki na ya ɗauki rawa kamar mazari a ƙwaƙwalwa ta so nake na tantance da gaske Bilal ne ko wani daban? Ko kuma ya fara watsa ƙwayoyin gusar da hankali ne bani da labari?

Ji nayi ciwon dake taso mun ma ya kama gaban sa, na yunƙura Amirah na riƙe dani tace
"Ni dama na daɗe ina zargin yana shaye shaye; daga yanda yake yi da idon sa baya ma iya buɗe su da kyau za'a gane. Kowa se da yace karki aure shi kika ƙi, gashi nan ashe mahaukaci kika aura bamu sani ba" ta ƙarasa tana fashewa da sabon kuka.
[1/25, 11:31 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya nairag 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*

*Page 19*
Ba zan iya cewa ga ta yanda muka fita daga gidan ba ni dai kawai na san munje gidan mu; muna sauka daga Adaidaita sahu Amirah ta sake ni na dafe gini saboda jirin dake kokawar kayar dani ita kuma ta tura ƙofar get ta shiga tana rushewa da kuka tamkar wadda tazo isar da saƙon mutuwa. Daƙyar na cira ƙafata na rufa mata baya ina yi ina dakatawa saboda ciwon marar dake taso mun, na dafe ƙofar shiga falon na tsaya ina kallon mazauna ciki da suka rufu kan Amiran cikin tashin hankali suna tambayar ta ba'asin kukanta; tabbas idan na canka dai dai kowannen su abu guda yake ayyanawa shine wani mugun abun ne ya same ni.

Ƙarasawa nayi ciki ina cije leɓe, Abba ne ya fara gani na; "Alhamdulillah" ya furta a fili yana nufo ni hakan ya ankarar da Mama da Anty Labiba suka waiwayo. A ƙasa na zauna duk suma suka zauna suna kallon Amirah da har sannan take kuka ni ɗin ma ita nake kallo ina mamakin wannan dirama tata. Abba ne yayi mata tsawa; cikin hasalar da sam ba ɗabi'ar sa bace ya nuna ta yana cewa
"Ga dai yar uwarki lafiyarta ƙalau, tun banyi loosing temper ba Sauda ki faɗa mun me akayi miki kike wannan kukan" ya ambaceta da ainihin sunanta wanda kuma sunan Mahaifiyar su Mama ne.
"Ai wlh dab nake da kai mata duka; duk a zato na wani abu ne ya samu Haliman se gata da ƙafafun ta ta shigo amma dan iskanci shine ta shigo tana irin wannan kukan me tsinka zuciya" Mama ta faɗa, ba tareda Amirah ta dakata da kukanta ba gaba ɗaya tace

"Ai Allah ne kawai ya kiyaye da ba lallai ta dawo da ƙafarta ba se dai a shigo muku da gawarta; Bilal ne ya rufe mu da duka, Allah ne kawai ya ƙwace mu a hannun sa da ƙila duk mu biyun ma ze kashe muku" ta ƙarasa tana sake rushewa da wani kukan daya fi na farko. Duk su ukun ni suka zubawa ido in da ni kuma na kafe nawa kallon kan Amirah mamakinta na neman dakatar mun da numfashi.

"Ai dan kar in magana ne ace na faɗi abinda ba shikenan ba amma dama ina ganin su nasan Bilal ne; ai kuwa billahillazi ya dakarwa kansa masifa da bala'i yau" Anty Labiba ta faɗa tana miƙewa tsaye. Hannu Abba ya ɗaga mata yana kallo yace
"Dakata Labiba, Halima gaya mun meya faru, gaskiya ne abinda ƙanwar ki ta faɗa?"

Ajiyar zuciya me nauyi na sauke haɗi da maida kallo na ƙasa; cikin muryata da firgicin abinda ya faru a can gidan ya dasa mun na ce
"Ba gaskiya ta faɗa ba Abba, babu abinda Bilal ya mana kawai dai..."
"Wallahi ƙarya takeyi Abba dukan mu yayi kuma ya ringa zaginmu yana ce mana yayan matsiyata marasa tarbiyya sannan yace mu bar masa gida kafin ya dawo idan ba haka ba se yayi mana abinda za'a ɗaure shi" Amirah ta katse ni.
Chapter 45 · 0% Book details