Sashe 157
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan dawowar Bilal Fadilan da mijinta sunzo gidan har yayi alƙawarin warwarewa Bilal ɗin sauran bashin da yake tsakaninsa da Jalilah. Haka Hajja ta manta da haushinsa takeji ta ringa masa godiya harda hawaye, Bilal dai ko a fuska bai nuna jin daɗi ba balle ma yayi masa godiya. Bakinsu ɗaya, kuɗin da yake maganar zai bata kuma dama ƙarya ce bai ci ba dan kayan daya ɗiba miliyan bakwai da motsi ya siyar dasu ya san kuma dukda karyar dasu yayi sunyi wutar duniya ace miliyan goma ba talatin ɗin data ƙaƙaba masa ba. Amma ya ya iya? Dama an ce tsuntsun daya ja ruwa ai shi ruwa zai doka.
Shikenan maganar Jalilah ta mutu dan kwana biyu a tsakani ta kirashi da kanta kamar ba zai ɗauka bama amma ya amsa, ta faɗa masa Ahlan ya biya masa sauran kuɗin da take binsa dan haka ya faɗawa lauyansa yaje kotu ya ƙarasa warware abinda yayi saura.
"Dukda mugun halinka Allah ya taimakeka ya haɗaka da mutanen kirki a rayuwarka. Ban zata Hafiz zai sake waiwayarka ba sai gashi ya biya maka tara. Toh ka saurareni da kyau, kada ka ɗauka shikenan iya wannan taskun dana sakaka kaci banza. Daga yau ba lallai ka sake jin ko da labarina ba amma kafin na fita daga rayuwarka ina mai tabbatar maka sai na bar maka tabon da har ka koma ga Allah ba zai taɓa gogewa daga zuciyarka ba Bilal" daga haka ta katse wayar shima yayi tsaki ya danna mata block.
Tunda sun rigada sun warware babu wani abu data isa tayi masa idan ma batayi wasa ba a yanzu zai ita ɗaura ɗamarar yin wasan Kura da ita tunda ba ita kaɗai ta iya haɗa sharri ba ai.
Haka rayuwa ta cigaba da gurgurawa tsakanin Hajja da Zulaiha ana zaman doya da manja, ba Hajja kaɗai ba hatta da shi kansa zama suke kamar wasu roommates na Hostel ya rasa dalili yanzu idan zasu kwana su wuni idan ba shi yayi mata magana ba ba zata ce masa uffan ba ko maganar yayi mata ma sai taga dama zata mayar masa da mai daɗi. Idan zaman gidan ya isheta ta gaji da sababin Hajja tayi wanka ta fice tace ta tafi gida.
Satinsu shida a gidan tace masa tace masa ita ta gaji, ko dai ya sama musu wani gidan su koma bata damu ba ko gidan haya ne mai ɗaki ɗaya yafi mata zaman nan ko kuma ta tafi gidansu, bata ce ya saketa ba amma zata tafi zuwa duk sanda ya samu sarari da zai samar mata inda zata zauna sai ta dawo.
Shi kansa a takuren yake toh amma bashida halin da zaice zai nemi gidan haya a yanzu. Yan kuɗaɗen da sukayi saura da Abubakar ya bashi a ciki yacd yayo musu siyayyar kayan abinci da zasu ɗan ja lokaci sauran kuma ya rike ya juya masa tunda bayan aiki Abubakar ɗin yana taɓa kasuwanci kuma ba laifi abun ya karɓe shi banda sabgar Bilal ɗin daya laƙume masa fin rabin jarinsa dole ya ture maganar aurensa data taso a gefe yanzu yake ƙoƙarin sake farfaɗo da jarin.
Tunani yayi ko ya karɓi wani abu a hannun Abubakar ɗin ya kama gidan sai kuma ya fasa dan har ga Allah ƙoƙari yakeyi ya gyara kura-kurensa na baya. Yanzun ya zama ba sawa babu hanawa, ba ruwansa da kowa daga gida sai masallaci tunda ta tabbata an koreshi daga aiki dama kuma shi ba wata sana'a ya iya ba balle yace zai yi shiyasa ma yace Abubakar ya juya masa kuɗin, idan
sai idan kaɗaici ya dameshi ya tafi Chemist Nasir na nan unguwar idan yana nan kenan dan yanzu kuzan branch huɗu gareshi a unguwanni daban daban, diploma da Bilal yake masa iskanci akanta wai ba abinda zata tsinana masa ya tafi suyi degree gashi da ita ya fara kuma ita ce tushen duk abinda ya samu a yanzu.
Ganin yanda Hajja da Zulaiha suka zama kamar wasu sa'anni kullum cikin kacenace wanda yake ganin kamar da gayya Zulaihan take yin abinda ta san Hajjan zatayi magana dole ya nemi sharar Nasir akan zancen neman gida ya ce masa hakan babu laifi dama ya sani da wahala zaman ya yuwu baya ga haka akwai takura dan haka ya barta ta tafi gida idan ya so sai ayi ƙoƙarin a nema masa ko ƙarami ne da zasu zauna kafin kuma aga tanadin da Allah yayi a gaba.
Shikenan Zulaiha ta koma gida Hajja ta huta da surutu.
Ranar Juma'a yana kwance a falon Hajja bayan an sakko daga sallar Juma'a, da zazzaɓi ya tashi ranar dan daƙyar ya iya fita masallacin yana dawowa kuma shine ya kwanta. Yana kwancen wayarsa ta shiga ƙara, yayi mamakin ganin mai kiran, Hafiz ne. Ji yayi yana jin kunyar magana dashi dan haka ya kasa ɗagawa har saida ta katse wani kiran ya sake shigowa kafin yayi ta maza ya amsa.
Muryar Hafiz a sake suka gaisa yace masa yana waje. Fita yayi ya tarar dasu su uku suka shiga ciki sai da sukayi jiran Hajja dake sallah a cikin ɗaki ta idar kafin ta lallaɓa ta fito suka gaisa. Damuwar Fadila data saka a ranta ta saka lafiya take mata wasa hawan jininta ya tsananta har ta dawo shan magani kullum.
"Idonka kenan Hafizu" Hajja ta faɗa bayan data zauna ba kunya, yayi murmushi suka gaisheta ta tambayeshi iyali sai lokacin Bilal yaji ashe Suhaila ta sake haihu mace.
"Ɗaurin aure muka zo can ƙasa, shine nace bari na ratso mu gaisa dan na jima ban yuwo ta nan haka ba" Hafiz ɗin ya faɗa. Hajja tace
"Allah sarki ai kuwa ka kyauta. Munji abin arziƙi da akayi ubangiji ya sa a ɗauka a gaba, tun lokacin nake cewa zamuzo har gida muyi godiya toh ka ganmu daga ni har shi ɗin mun zama lafi-lafiya, yau lafiya gobe ciwo"
"Allah ya rufa asiri ya ƙara lafiya" cewar Hafiz kafin ya juya kan Bilal da yayi shiru yana sauraronsu ya ce
"Wani abokinmu ne yayi aure, ba shiri ma fa tambaya aka zo ɗazu da safe kawai iyayen yarinyar suka ce a ɗaura aure. Shine yace dan Allah su bari a sakko Juma'a kafin nan ya sanarwa mutanensa na kusa aka taso mu babu shiri sai da mukaje gaisuwa bayan an ɗauro auren abin mamaki naga ashe Halima ce amaryar".
Yanda Bilal yayi sai ka ɗauka bindiga ko wuƙa aka nuna masa amma ya kasa cewa komai sai idanuwa da yake zarewa, Hajja ce ta tambayi wace Halimar ya bata amsa da
"Halima dai Maman Al'amin tsohuwar matarsa. Wlh nasha mamaki na kuma yi masa musu murna shi da ita dan kowanne ya dace da abokin zama na ƙwarai. Halima mutuniyar kirkice shima kuma Salman babu laifi na san shi junior na ne a secondary school kafin muka zama abokai a Jami'a sama da shekara ashirin da ɗori muna tare har familyn mu an zama kamar yan uwa".
Haka Hafiz ya tafi ya bar Bilal cikin yanayin da bai taɓa zaton zai shiga akan Halima ba. Ƙasa ya zame y zauna ya saki hawayen da suka cika masa ido, Hajja kanta ɗaki ta koma duk jikinta yayi sanyi. Zuwan da Halima tayi yanda taga ta zama wata babbar mace ko makaho ya shafata ya san tana cikin nutsuwa da kwanciyar hankali saɓanin Bilal da tunda ya rabu da ita iftila suke dirar masa daga wannan sai wannan.
Tun ranar take lissafa ta inda Bilal ɗin zai fara gyaro ɓarnar daya tafka. Dukda Abubakar yace mata wanda suka zo tare wai Mijin da zata aura ne amma bata sare ba. Iya zuwan da tayi ya isa shaidar har yanzun akwai ɓurɓushin soyayyarsa a zuciyarta ba kuma za'a sha wahalar dawo da komai ba. Tana ganin idan har Allah ya yarda Haliman ta dawo Bilal ɗin zai samu madafa domin dai Mahaifin Halimar baze barshi haka ba sai kuma ga wannan magana wai ta ɗaura aure.
Bilal kuwa ɗaki ya koma ya kwanta yana jinyar jiki da zuciya. Bayan sallar isha'i yana zaune in da yayi sallah ya jiyo Hajja na ƙwala masa kira, yanda take kiran kamar ba lafiya ba ya fita da sauri a tsakar gidan ya tarar da ita da rarrafe ta fito daga ɗakin tana haki tace yayi maza ya nemo mata Adaidaita sahu da zai kaita gidan Fadila.
Taƙi ta masa bayanin komai dole ya fita ya taro mashin ɗin kafin yazo ya kamata suka kama hanya ko gidan bai rufe ba saboda yanda duk ta firgita shi. A hanya take ce masa "Kirana tayi tana kuka azo a taimaka mata zai kasheta saboda ya kawo karuwa gidan tace yaji tsoron Allah shine ya hau dukanta ya turota ta faɗo daga bene har yana cewa ni uwarta nice mazinaciya ba, tana can cikin jiini kuma wai ciki ne da ita" Hajjan ta faɗa tana rushewa da kuka.
Ranar da Halima ta buɗe wayarsa ya tuna har ya mareta ya kuma danganta mahaifiyarta da zina ce ta dawo masa, ya runtse ido ba tareda ya ce komai ba. Da suka isa suna tura ƙofar gidan ta buɗe suka shiga yana riƙe da Hajja dan bata ko taho da sandunanta ba saboda kiɗima. A falon ƙasa ta zauna suka ringa kiran sunan Fadila shiru tace ya hau sama ya dubo mata yarta. Haka nan ya ringa jin gabansa yana faɗuwa duk taku ɗaya da yayi akan benen, ƙofar falon saman ma a buɗe take an turo bata ƙarasa rufewa ba dan haka yana hango mutum biyu Mace da Namiji dake zaune Namijin yayi matashi da cinyar Macen.
Tura ƙofar yayi, dai-dai da gama buɗewa gaba ɗaya kuma idanuwansa sukayi kyakkyawan gani, irin ganin da Halima tayi masa a cikin gidanta shi yayiwa matarsa Zulaiha da Mijin ƙanwarsa.
Shikenan maganar Jalilah ta mutu dan kwana biyu a tsakani ta kirashi da kanta kamar ba zai ɗauka bama amma ya amsa, ta faɗa masa Ahlan ya biya masa sauran kuɗin da take binsa dan haka ya faɗawa lauyansa yaje kotu ya ƙarasa warware abinda yayi saura.
"Dukda mugun halinka Allah ya taimakeka ya haɗaka da mutanen kirki a rayuwarka. Ban zata Hafiz zai sake waiwayarka ba sai gashi ya biya maka tara. Toh ka saurareni da kyau, kada ka ɗauka shikenan iya wannan taskun dana sakaka kaci banza. Daga yau ba lallai ka sake jin ko da labarina ba amma kafin na fita daga rayuwarka ina mai tabbatar maka sai na bar maka tabon da har ka koma ga Allah ba zai taɓa gogewa daga zuciyarka ba Bilal" daga haka ta katse wayar shima yayi tsaki ya danna mata block.
Tunda sun rigada sun warware babu wani abu data isa tayi masa idan ma batayi wasa ba a yanzu zai ita ɗaura ɗamarar yin wasan Kura da ita tunda ba ita kaɗai ta iya haɗa sharri ba ai.
Haka rayuwa ta cigaba da gurgurawa tsakanin Hajja da Zulaiha ana zaman doya da manja, ba Hajja kaɗai ba hatta da shi kansa zama suke kamar wasu roommates na Hostel ya rasa dalili yanzu idan zasu kwana su wuni idan ba shi yayi mata magana ba ba zata ce masa uffan ba ko maganar yayi mata ma sai taga dama zata mayar masa da mai daɗi. Idan zaman gidan ya isheta ta gaji da sababin Hajja tayi wanka ta fice tace ta tafi gida.
Satinsu shida a gidan tace masa tace masa ita ta gaji, ko dai ya sama musu wani gidan su koma bata damu ba ko gidan haya ne mai ɗaki ɗaya yafi mata zaman nan ko kuma ta tafi gidansu, bata ce ya saketa ba amma zata tafi zuwa duk sanda ya samu sarari da zai samar mata inda zata zauna sai ta dawo.
Shi kansa a takuren yake toh amma bashida halin da zaice zai nemi gidan haya a yanzu. Yan kuɗaɗen da sukayi saura da Abubakar ya bashi a ciki yacd yayo musu siyayyar kayan abinci da zasu ɗan ja lokaci sauran kuma ya rike ya juya masa tunda bayan aiki Abubakar ɗin yana taɓa kasuwanci kuma ba laifi abun ya karɓe shi banda sabgar Bilal ɗin daya laƙume masa fin rabin jarinsa dole ya ture maganar aurensa data taso a gefe yanzu yake ƙoƙarin sake farfaɗo da jarin.
Tunani yayi ko ya karɓi wani abu a hannun Abubakar ɗin ya kama gidan sai kuma ya fasa dan har ga Allah ƙoƙari yakeyi ya gyara kura-kurensa na baya. Yanzun ya zama ba sawa babu hanawa, ba ruwansa da kowa daga gida sai masallaci tunda ta tabbata an koreshi daga aiki dama kuma shi ba wata sana'a ya iya ba balle yace zai yi shiyasa ma yace Abubakar ya juya masa kuɗin, idan
sai idan kaɗaici ya dameshi ya tafi Chemist Nasir na nan unguwar idan yana nan kenan dan yanzu kuzan branch huɗu gareshi a unguwanni daban daban, diploma da Bilal yake masa iskanci akanta wai ba abinda zata tsinana masa ya tafi suyi degree gashi da ita ya fara kuma ita ce tushen duk abinda ya samu a yanzu.
Ganin yanda Hajja da Zulaiha suka zama kamar wasu sa'anni kullum cikin kacenace wanda yake ganin kamar da gayya Zulaihan take yin abinda ta san Hajjan zatayi magana dole ya nemi sharar Nasir akan zancen neman gida ya ce masa hakan babu laifi dama ya sani da wahala zaman ya yuwu baya ga haka akwai takura dan haka ya barta ta tafi gida idan ya so sai ayi ƙoƙarin a nema masa ko ƙarami ne da zasu zauna kafin kuma aga tanadin da Allah yayi a gaba.
Shikenan Zulaiha ta koma gida Hajja ta huta da surutu.
Ranar Juma'a yana kwance a falon Hajja bayan an sakko daga sallar Juma'a, da zazzaɓi ya tashi ranar dan daƙyar ya iya fita masallacin yana dawowa kuma shine ya kwanta. Yana kwancen wayarsa ta shiga ƙara, yayi mamakin ganin mai kiran, Hafiz ne. Ji yayi yana jin kunyar magana dashi dan haka ya kasa ɗagawa har saida ta katse wani kiran ya sake shigowa kafin yayi ta maza ya amsa.
Muryar Hafiz a sake suka gaisa yace masa yana waje. Fita yayi ya tarar dasu su uku suka shiga ciki sai da sukayi jiran Hajja dake sallah a cikin ɗaki ta idar kafin ta lallaɓa ta fito suka gaisa. Damuwar Fadila data saka a ranta ta saka lafiya take mata wasa hawan jininta ya tsananta har ta dawo shan magani kullum.
"Idonka kenan Hafizu" Hajja ta faɗa bayan data zauna ba kunya, yayi murmushi suka gaisheta ta tambayeshi iyali sai lokacin Bilal yaji ashe Suhaila ta sake haihu mace.
"Ɗaurin aure muka zo can ƙasa, shine nace bari na ratso mu gaisa dan na jima ban yuwo ta nan haka ba" Hafiz ɗin ya faɗa. Hajja tace
"Allah sarki ai kuwa ka kyauta. Munji abin arziƙi da akayi ubangiji ya sa a ɗauka a gaba, tun lokacin nake cewa zamuzo har gida muyi godiya toh ka ganmu daga ni har shi ɗin mun zama lafi-lafiya, yau lafiya gobe ciwo"
"Allah ya rufa asiri ya ƙara lafiya" cewar Hafiz kafin ya juya kan Bilal da yayi shiru yana sauraronsu ya ce
"Wani abokinmu ne yayi aure, ba shiri ma fa tambaya aka zo ɗazu da safe kawai iyayen yarinyar suka ce a ɗaura aure. Shine yace dan Allah su bari a sakko Juma'a kafin nan ya sanarwa mutanensa na kusa aka taso mu babu shiri sai da mukaje gaisuwa bayan an ɗauro auren abin mamaki naga ashe Halima ce amaryar".
Yanda Bilal yayi sai ka ɗauka bindiga ko wuƙa aka nuna masa amma ya kasa cewa komai sai idanuwa da yake zarewa, Hajja ce ta tambayi wace Halimar ya bata amsa da
"Halima dai Maman Al'amin tsohuwar matarsa. Wlh nasha mamaki na kuma yi masa musu murna shi da ita dan kowanne ya dace da abokin zama na ƙwarai. Halima mutuniyar kirkice shima kuma Salman babu laifi na san shi junior na ne a secondary school kafin muka zama abokai a Jami'a sama da shekara ashirin da ɗori muna tare har familyn mu an zama kamar yan uwa".
Haka Hafiz ya tafi ya bar Bilal cikin yanayin da bai taɓa zaton zai shiga akan Halima ba. Ƙasa ya zame y zauna ya saki hawayen da suka cika masa ido, Hajja kanta ɗaki ta koma duk jikinta yayi sanyi. Zuwan da Halima tayi yanda taga ta zama wata babbar mace ko makaho ya shafata ya san tana cikin nutsuwa da kwanciyar hankali saɓanin Bilal da tunda ya rabu da ita iftila suke dirar masa daga wannan sai wannan.
Tun ranar take lissafa ta inda Bilal ɗin zai fara gyaro ɓarnar daya tafka. Dukda Abubakar yace mata wanda suka zo tare wai Mijin da zata aura ne amma bata sare ba. Iya zuwan da tayi ya isa shaidar har yanzun akwai ɓurɓushin soyayyarsa a zuciyarta ba kuma za'a sha wahalar dawo da komai ba. Tana ganin idan har Allah ya yarda Haliman ta dawo Bilal ɗin zai samu madafa domin dai Mahaifin Halimar baze barshi haka ba sai kuma ga wannan magana wai ta ɗaura aure.
Bilal kuwa ɗaki ya koma ya kwanta yana jinyar jiki da zuciya. Bayan sallar isha'i yana zaune in da yayi sallah ya jiyo Hajja na ƙwala masa kira, yanda take kiran kamar ba lafiya ba ya fita da sauri a tsakar gidan ya tarar da ita da rarrafe ta fito daga ɗakin tana haki tace yayi maza ya nemo mata Adaidaita sahu da zai kaita gidan Fadila.
Taƙi ta masa bayanin komai dole ya fita ya taro mashin ɗin kafin yazo ya kamata suka kama hanya ko gidan bai rufe ba saboda yanda duk ta firgita shi. A hanya take ce masa "Kirana tayi tana kuka azo a taimaka mata zai kasheta saboda ya kawo karuwa gidan tace yaji tsoron Allah shine ya hau dukanta ya turota ta faɗo daga bene har yana cewa ni uwarta nice mazinaciya ba, tana can cikin jiini kuma wai ciki ne da ita" Hajjan ta faɗa tana rushewa da kuka.
Ranar da Halima ta buɗe wayarsa ya tuna har ya mareta ya kuma danganta mahaifiyarta da zina ce ta dawo masa, ya runtse ido ba tareda ya ce komai ba. Da suka isa suna tura ƙofar gidan ta buɗe suka shiga yana riƙe da Hajja dan bata ko taho da sandunanta ba saboda kiɗima. A falon ƙasa ta zauna suka ringa kiran sunan Fadila shiru tace ya hau sama ya dubo mata yarta. Haka nan ya ringa jin gabansa yana faɗuwa duk taku ɗaya da yayi akan benen, ƙofar falon saman ma a buɗe take an turo bata ƙarasa rufewa ba dan haka yana hango mutum biyu Mace da Namiji dake zaune Namijin yayi matashi da cinyar Macen.
Tura ƙofar yayi, dai-dai da gama buɗewa gaba ɗaya kuma idanuwansa sukayi kyakkyawan gani, irin ganin da Halima tayi masa a cikin gidanta shi yayiwa matarsa Zulaiha da Mijin ƙanwarsa.