Sashe 106
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk cikinmu babu mai iya miki musu, Allah ya hore miki yayanki mutum nawa ne suke addu'a da fatan Allah ya ɗora su akan yayansu ta yanda zasu ringa jin maganarsu amma ke Allah ya miki wannan arziƙin a maimakon kiyi amfani da hakan ki tarbiyyantar damu ta yanda ko bayan ranki za'ayi alfahari da abinda kika haifa amma kin bari son zuciya da shaiɗan sunyi tasiri a zuciyarki suna kuma jagorantar al'amuranki".
Tsit sukayi kamar ruwa ya cinye su suna sauraronsa, ya miƙe tsaye yana cigaba da cewa
"Wlh idan har baku canza wannan hanyar da kuke tafiya akai ba nan ba da daɗewa ba zaku fara dana sani mara amfani, abinda Yaya Bilal yayi idan da da niyya mai kyau yayi shi ai ba aibu bane har a gurin Allah kuma zai samu lada, amma yanzu kuwa aikin banza kayi domin ka tsallake farilla ka bar dolenka a gida matar aurenka ka barta ɗauke da nauyin kanta dana yayanka ka tafi kana bautawa wasu. Kuma nan ba da daɗewa ba zaka gane kallon kitse ka daɗe kana yiwa rogo" ya ƙarasa yana wata yar dariya mai cike da ma'anoni daga nan ya fice daga falon.
Anty Ladi ce ta ce
"Ashe ba iya Bilal ne ɗan abu ta kazan uban ba, koda yake dama shiru shiru mutum ai kaji tsoron sa idan suka tashi sai sunfi uban kowa iya iskanci toh wlh Hajja dole ma ki tashi a tsaye kina dai jin sa tun bai yi aurenba ya iya tsayawa gabanki yana faɗa miki magana wannan ai kuma bamu san kalar matar da zai kwaso ba ƙila haɗuwa zasu ringayi shi da ita suna zaginki"
"Allah ya kiyashe shi da zagin mahaifiyar sa balle har ya auro wacce zasu zageta tare" Anty Amina ta faɗa sannan ta juya kan Hajja ta ce
"Kiyi haƙuri Hajja amma gaskiya Abubakar ya faɗa miki, idan muka gyaru kece haka idan muka lalace duka ke za'a zaga. Yanzu wane kallo kike so duniya tayi miki ba'a gama da Halima ba yanzu ki ce sai ya saki matar da ko tarewa ba tayi a ɗakinsa ba akan me?
Babu wanda ya ce abinda yayi yayi daidai ko ya kyauta amma kuma ya rigada ya faru tunda har ba wani aibu bane a ciki ai babu hujjar kuma ace za'a raba aure ko makamancin haka.
Yanda kika ce kin haƙura kin karɓi ƙaddara kiyi haƙuri ki kuma bishi da addu'a shikenan amma ace da kanki kike nema ki buɗe masa hanyar auri saki wace riba zaki ci akan hakan?
Ni wlh na ɗauka kiran da kika mana maganar Halima zakiyi, yanzu tsakani da Allah ace yarinyar nan kusan watanta biyu a gida amma babu wanda ya bi sahu ko yaje bada haƙuri ai ko shirun da iyayenta sukayi kaɗai ya isa ya saka ku sha jinin jikinku ayi abinda ya kamata domin dai sai dai mutum yaƙi Allah kawai ya zagi Halima baya ga haka duk mun san irin haƙurin zaman da takeyi dashi a yanzu ko a gaba wlh ba zai taɓa samun macen da zai taka kamarta su kwashe lafiya ba kuma har idan yayi kasadar rabuwa da ita ban masa baki ba amma wlh ba zai maida kamarta ba ke kanki na zaki maida suruka kamar Halima ba".
"Ni idan kina magana wlh mamaki kike bani Amina har yaushe kika sauka daga tafiyar da yanzu kike kira ta rashin dai dai da har zaki ringa yiwa mutane wa'azi?" Habiba ta faɗa, Amina ta kalle ta tace
"Kema kika ce na sauka daga turbar ɓata na bi ta gaskiya toh Alhamdulillah tunda na gane kuma kuma fatan da nake muku kenan ku gane kafin lokaci ya ƙure muku"
"Wato mu da Hajjan ne akan turbar ɓata?" Anty Ladi ta faɗa ba tareda shakka ba kuma tace
"Ƙwarai kuwa, kun ɗora ranku akan son zuciya da kwaɗayi ga gaskiya ƙiri ƙiri a gabanku ku rintse iso ku ƙi kallonta. A shekarun Hajja yanzu dama akwai abubuwan da sai an fara mata uzuri, mu ya kamata idan ta kuskure mu nusar da ita ba kuma mu cigaba da biye mata akan abinda mun tabbatar ba gaskiya bane duniyar nan fa ba matabbata bace duk yanda ka so da sonta kuma akwai ranar da zaka barta dan haka gara mu yiwa kanmu faɗa mu kuma yiwa goben mu ta ainihi tanadi. Ni dai idan har ba maganar yanda za'ayi uwargidan sa ta dawo za'a yi ba kiyi haƙuri Hajja kada a sake kirana dan ba zan zo ba" daga haka ta ɗauki jakarta ta fita tana jin Ladi da Habiba na faɗa mata maganganu amma bata tamka ba.
A hankali ba tareda ya haɗa ido da kowa ba ya bi bayan Anty Aminan yana ko Hadiza tana cewa
"Ina zaka je kuma munafukin Allah ko an sallameka ne?"
[5/9, 8:49 AM] +234 810 691 6476: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 45*
ALHAMDULILLAH Mun gama biki lafiya nagode da fatan Alkhairi.
"Dan girman Allah Anty Amina kiyi mun wannan alfarmar, wlh nayi duk dabarata amma taƙi saurarona, idan naje gidan bata fitowa haka idan na kira wayarta bata amsawa. Ɗazu da safe suka zo ba dan na kulle gidan ta ciki ba ma da tuni sun kwashe kaya.
Ke shaida ce ina son Halima duk abinda kuma ya faru sharrin shaiɗan ne da kuma Hajja amma wlh ba a son raina bane" ya faɗa bayan da ya tsayar da Anty Amina a ƙofar gida.
Kallonsa ta ringayi har ya kai aya kafin ta harare shi ta ce
"Kaine shaiɗan ɗin ai ba wani ba zancen Hajja kuma ko da da gaske da saka hannunta ai kai ba mahaukaci bane; da zaka ringa biye mata idan dama ba gangara kake nema ba ai ka san ta yanda zaka lallaɓata ka zauna da matarka lafiya. Karma ka raina mun wayau na san kana sane yanzun ma Allah kaɗai ya san abinda yake ƙasan ranka da kake so ka sake janyota ka cigaba da gasa mata aya a hannu, to ni dai babu ruwana; yanda sanda ka koreta bakayi shawara da kowa ba yanzu ma sai ka san ta yanda zaka bi idan itama bata gaji da uƙubar da kake mata ba sai ta dawo" ta faɗa tana ƙoƙarin buɗe motarta.
Riƙe murfin yayi tamkar zai fashe mata da kuka harda rage tsayi ya ce
"Na rantse da Allah bani na ce ta tafi ba haka kawai ta haɗa kayanta kuma babu yanda banyi da tayi haƙuri mu zauna mu sasanta koma menene ba amma ta ce ita tafiya zatayi".
"Lallai Bilal, wato har yanzu bakayi laushi ba ka iya kallon tsabar ido na ka shirga mun ƙarya har kana rantsuwa da Allah ko?
Ka san ko jikina kunnuwa ne ba zan taɓa yarda haka nan Halima ta sa ƙafa ta bar gidanka ba domin a baya ka mata abubuwan daya kamata ta tafin amma ta shanye sai yanzu zaka ce haka nan ta tafi?
To bari kaji, babu ruwana; yanda baka godewa ni'imar da Allah yayi maka ta aurenta ba yanzu sai ka godewa azabar sakacin da kayi har ka rasata" ta faɗa tana fizge murfin motarta. Ƙasa ya zube ya kama ƙafarta yana cewa
"Dan girman Allah Anty karki ce haka; ke kaɗai nake saka ran zaki fahimce ni kuma ki mun uzuri na kuma san itama ba zata ƙi sauraronki ba. Dagaske laifi nayi mata amma wannan tsakaninmu ne kuma na san yanzu ta haƙura. Dan Allah ki tayani rarrashinta wlh na miki alƙawarin har idan ta dawo ba za'a sake jin kanmu ba".
Ganin masu giftawa sun fara tsayawa suna kallon su ya saka ta daka maza tsawa ta ce
"Dallah tashi karka tara mun mutane" ya miƙe tareda riƙe hannunta, ta balla masa harara sai ya saketa ya zare key ɗin motar dGa hannunta yana cewa
"Muje na kaiki dan Allah"
"Ka kaini ina? Kaga Bilal ka bani key ɗin motara na tafi; tunda kake shuka mata tsiya banje na tayata ƙwatar yancinta ba sai yanzu da ta tasarwa kanta kake so naje saboda goyon bayan rashin gaskiya na ce ta dawo taci gaba da zama da kai? To ba haka nake ba" ta faɗa cikin muryar dake nuna ba wasa take ba.
Hannu biyu ya dafe kansa kafin ya juya ya kalli ɗai ɗaikun yan unguwa dake satar kallon su ya ce
"Idan na faɗa miki laifin da na mata zaki tayani bata haƙuri?"
Ta kafe shi da ido kamar mai nazari kafin ta ce
"Idan ka cancanci yafiya zan ga abinda zan iya". Saida ta zagaya ta zauna a kujerar mai zaman banza ya rufe mata ƙofar kafin ya koma mazaunin direba ya tada motar suka bar layin, can gefen titi ya samu guri yayi parking, sun fi minti biyar yana saƙa abinda zai gaya mata da zata yarda ita kuma tana danna wayarta kafin yayi ƙarfin halin cewa
"Wayata ta ɗauka ta bincika shi ne ta ga chats ɗina da Zulaiha da kuma Jalilah. Ba tareda ta buƙaci wani ƙarin bayani ba kawai ta hau zagina tana gayamun baƙaƙen maganganu; na faɗa mata ba abinda take tunani bane duk su biyun auren su zanyi amma taƙi fahimta ta ringa zagina har da kama mun wuyan riga wai na saketa ni kuma na zuciya na mareta shikenan ta haɗa kayanta ta tafi gida".
Yanda yayi maganar sai ka rantse da Allah gaskiya ya faɗa, Anty Amina da tayi shiru tana kallon sa ta ce
"Ka faɗa mun abinda hankali zai ɗauka in kuma ba haka ba ka daina ɓata mun lokaci ka rabu da ni na tafi".
Wata rantsuwar ya sake kwasowa ya dire yana tabbatar mata da iya gaskiyar abinda ya faru kenan.
Tsit sukayi kamar ruwa ya cinye su suna sauraronsa, ya miƙe tsaye yana cigaba da cewa
"Wlh idan har baku canza wannan hanyar da kuke tafiya akai ba nan ba da daɗewa ba zaku fara dana sani mara amfani, abinda Yaya Bilal yayi idan da da niyya mai kyau yayi shi ai ba aibu bane har a gurin Allah kuma zai samu lada, amma yanzu kuwa aikin banza kayi domin ka tsallake farilla ka bar dolenka a gida matar aurenka ka barta ɗauke da nauyin kanta dana yayanka ka tafi kana bautawa wasu. Kuma nan ba da daɗewa ba zaka gane kallon kitse ka daɗe kana yiwa rogo" ya ƙarasa yana wata yar dariya mai cike da ma'anoni daga nan ya fice daga falon.
Anty Ladi ce ta ce
"Ashe ba iya Bilal ne ɗan abu ta kazan uban ba, koda yake dama shiru shiru mutum ai kaji tsoron sa idan suka tashi sai sunfi uban kowa iya iskanci toh wlh Hajja dole ma ki tashi a tsaye kina dai jin sa tun bai yi aurenba ya iya tsayawa gabanki yana faɗa miki magana wannan ai kuma bamu san kalar matar da zai kwaso ba ƙila haɗuwa zasu ringayi shi da ita suna zaginki"
"Allah ya kiyashe shi da zagin mahaifiyar sa balle har ya auro wacce zasu zageta tare" Anty Amina ta faɗa sannan ta juya kan Hajja ta ce
"Kiyi haƙuri Hajja amma gaskiya Abubakar ya faɗa miki, idan muka gyaru kece haka idan muka lalace duka ke za'a zaga. Yanzu wane kallo kike so duniya tayi miki ba'a gama da Halima ba yanzu ki ce sai ya saki matar da ko tarewa ba tayi a ɗakinsa ba akan me?
Babu wanda ya ce abinda yayi yayi daidai ko ya kyauta amma kuma ya rigada ya faru tunda har ba wani aibu bane a ciki ai babu hujjar kuma ace za'a raba aure ko makamancin haka.
Yanda kika ce kin haƙura kin karɓi ƙaddara kiyi haƙuri ki kuma bishi da addu'a shikenan amma ace da kanki kike nema ki buɗe masa hanyar auri saki wace riba zaki ci akan hakan?
Ni wlh na ɗauka kiran da kika mana maganar Halima zakiyi, yanzu tsakani da Allah ace yarinyar nan kusan watanta biyu a gida amma babu wanda ya bi sahu ko yaje bada haƙuri ai ko shirun da iyayenta sukayi kaɗai ya isa ya saka ku sha jinin jikinku ayi abinda ya kamata domin dai sai dai mutum yaƙi Allah kawai ya zagi Halima baya ga haka duk mun san irin haƙurin zaman da takeyi dashi a yanzu ko a gaba wlh ba zai taɓa samun macen da zai taka kamarta su kwashe lafiya ba kuma har idan yayi kasadar rabuwa da ita ban masa baki ba amma wlh ba zai maida kamarta ba ke kanki na zaki maida suruka kamar Halima ba".
"Ni idan kina magana wlh mamaki kike bani Amina har yaushe kika sauka daga tafiyar da yanzu kike kira ta rashin dai dai da har zaki ringa yiwa mutane wa'azi?" Habiba ta faɗa, Amina ta kalle ta tace
"Kema kika ce na sauka daga turbar ɓata na bi ta gaskiya toh Alhamdulillah tunda na gane kuma kuma fatan da nake muku kenan ku gane kafin lokaci ya ƙure muku"
"Wato mu da Hajjan ne akan turbar ɓata?" Anty Ladi ta faɗa ba tareda shakka ba kuma tace
"Ƙwarai kuwa, kun ɗora ranku akan son zuciya da kwaɗayi ga gaskiya ƙiri ƙiri a gabanku ku rintse iso ku ƙi kallonta. A shekarun Hajja yanzu dama akwai abubuwan da sai an fara mata uzuri, mu ya kamata idan ta kuskure mu nusar da ita ba kuma mu cigaba da biye mata akan abinda mun tabbatar ba gaskiya bane duniyar nan fa ba matabbata bace duk yanda ka so da sonta kuma akwai ranar da zaka barta dan haka gara mu yiwa kanmu faɗa mu kuma yiwa goben mu ta ainihi tanadi. Ni dai idan har ba maganar yanda za'ayi uwargidan sa ta dawo za'a yi ba kiyi haƙuri Hajja kada a sake kirana dan ba zan zo ba" daga haka ta ɗauki jakarta ta fita tana jin Ladi da Habiba na faɗa mata maganganu amma bata tamka ba.
A hankali ba tareda ya haɗa ido da kowa ba ya bi bayan Anty Aminan yana ko Hadiza tana cewa
"Ina zaka je kuma munafukin Allah ko an sallameka ne?"
[5/9, 8:49 AM] +234 810 691 6476: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 45*
ALHAMDULILLAH Mun gama biki lafiya nagode da fatan Alkhairi.
"Dan girman Allah Anty Amina kiyi mun wannan alfarmar, wlh nayi duk dabarata amma taƙi saurarona, idan naje gidan bata fitowa haka idan na kira wayarta bata amsawa. Ɗazu da safe suka zo ba dan na kulle gidan ta ciki ba ma da tuni sun kwashe kaya.
Ke shaida ce ina son Halima duk abinda kuma ya faru sharrin shaiɗan ne da kuma Hajja amma wlh ba a son raina bane" ya faɗa bayan da ya tsayar da Anty Amina a ƙofar gida.
Kallonsa ta ringayi har ya kai aya kafin ta harare shi ta ce
"Kaine shaiɗan ɗin ai ba wani ba zancen Hajja kuma ko da da gaske da saka hannunta ai kai ba mahaukaci bane; da zaka ringa biye mata idan dama ba gangara kake nema ba ai ka san ta yanda zaka lallaɓata ka zauna da matarka lafiya. Karma ka raina mun wayau na san kana sane yanzun ma Allah kaɗai ya san abinda yake ƙasan ranka da kake so ka sake janyota ka cigaba da gasa mata aya a hannu, to ni dai babu ruwana; yanda sanda ka koreta bakayi shawara da kowa ba yanzu ma sai ka san ta yanda zaka bi idan itama bata gaji da uƙubar da kake mata ba sai ta dawo" ta faɗa tana ƙoƙarin buɗe motarta.
Riƙe murfin yayi tamkar zai fashe mata da kuka harda rage tsayi ya ce
"Na rantse da Allah bani na ce ta tafi ba haka kawai ta haɗa kayanta kuma babu yanda banyi da tayi haƙuri mu zauna mu sasanta koma menene ba amma ta ce ita tafiya zatayi".
"Lallai Bilal, wato har yanzu bakayi laushi ba ka iya kallon tsabar ido na ka shirga mun ƙarya har kana rantsuwa da Allah ko?
Ka san ko jikina kunnuwa ne ba zan taɓa yarda haka nan Halima ta sa ƙafa ta bar gidanka ba domin a baya ka mata abubuwan daya kamata ta tafin amma ta shanye sai yanzu zaka ce haka nan ta tafi?
To bari kaji, babu ruwana; yanda baka godewa ni'imar da Allah yayi maka ta aurenta ba yanzu sai ka godewa azabar sakacin da kayi har ka rasata" ta faɗa tana fizge murfin motarta. Ƙasa ya zube ya kama ƙafarta yana cewa
"Dan girman Allah Anty karki ce haka; ke kaɗai nake saka ran zaki fahimce ni kuma ki mun uzuri na kuma san itama ba zata ƙi sauraronki ba. Dagaske laifi nayi mata amma wannan tsakaninmu ne kuma na san yanzu ta haƙura. Dan Allah ki tayani rarrashinta wlh na miki alƙawarin har idan ta dawo ba za'a sake jin kanmu ba".
Ganin masu giftawa sun fara tsayawa suna kallon su ya saka ta daka maza tsawa ta ce
"Dallah tashi karka tara mun mutane" ya miƙe tareda riƙe hannunta, ta balla masa harara sai ya saketa ya zare key ɗin motar dGa hannunta yana cewa
"Muje na kaiki dan Allah"
"Ka kaini ina? Kaga Bilal ka bani key ɗin motara na tafi; tunda kake shuka mata tsiya banje na tayata ƙwatar yancinta ba sai yanzu da ta tasarwa kanta kake so naje saboda goyon bayan rashin gaskiya na ce ta dawo taci gaba da zama da kai? To ba haka nake ba" ta faɗa cikin muryar dake nuna ba wasa take ba.
Hannu biyu ya dafe kansa kafin ya juya ya kalli ɗai ɗaikun yan unguwa dake satar kallon su ya ce
"Idan na faɗa miki laifin da na mata zaki tayani bata haƙuri?"
Ta kafe shi da ido kamar mai nazari kafin ta ce
"Idan ka cancanci yafiya zan ga abinda zan iya". Saida ta zagaya ta zauna a kujerar mai zaman banza ya rufe mata ƙofar kafin ya koma mazaunin direba ya tada motar suka bar layin, can gefen titi ya samu guri yayi parking, sun fi minti biyar yana saƙa abinda zai gaya mata da zata yarda ita kuma tana danna wayarta kafin yayi ƙarfin halin cewa
"Wayata ta ɗauka ta bincika shi ne ta ga chats ɗina da Zulaiha da kuma Jalilah. Ba tareda ta buƙaci wani ƙarin bayani ba kawai ta hau zagina tana gayamun baƙaƙen maganganu; na faɗa mata ba abinda take tunani bane duk su biyun auren su zanyi amma taƙi fahimta ta ringa zagina har da kama mun wuyan riga wai na saketa ni kuma na zuciya na mareta shikenan ta haɗa kayanta ta tafi gida".
Yanda yayi maganar sai ka rantse da Allah gaskiya ya faɗa, Anty Amina da tayi shiru tana kallon sa ta ce
"Ka faɗa mun abinda hankali zai ɗauka in kuma ba haka ba ka daina ɓata mun lokaci ka rabu da ni na tafi".
Wata rantsuwar ya sake kwasowa ya dire yana tabbatar mata da iya gaskiyar abinda ya faru kenan.