Sashe 71
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na sauke numfashin da ban san dalilin yin sa ba haɗi da yin gajeran murmushin da iyakacin sa baki. Fita yayi ya barni. Ban san tsahon lokacin da na ɗauka a zaune ba ban kuma san tunanin me nake yi ba har aka kira sallar magriba kafin na iya tashi daga gurin da nake. Me ya sa ban tambaye shi matar aure ba ce ko budurwa ko ba komai na samu cikakkiyar nutsuwa daga tunane tunanen da zuciya ta take ta raya mun? Haka nan na yi sallah ina jiran ya dawo na ji cikakken bayani akan wacece JALILA? Daga muryar ta zan iya fasaltata a shekaru talatin zuwa sama daga kuma maganar ta na tabbatar yar gayu ce, har na fasaltata a idanuwa na irin matan Abuja jiki duk madarar nan. Wannan tunanin ya saka mun ƙunci da rashin nutsuwa a zuciya ta amma kuma duk yanda ma zaƙu ya dawo na yi masa tambayar sai na kasa lokacin da ya dawo.
Sai da aka yi isha'i ya sake shigowa falon lokacin ina cin sauran abincin da ya rage, ya zauna a kusa da ni fuska a sake ya ɗauki Al'amin ya fara masa wasa ni dai kallo ɗaya na masa na mayar da kai na cigaba da cin abincin da nake yi ina kokawa da zuciya ta dake azalzalata akan na tambaye shi wacece JALILA amma na kasa.
"Akwai sauran abincin ne?" Ya tambaye ni, ba tare da na yi magana ba na girgiza masa kai kawai, ya sake cewa
"Ba har dare kika yi girkin gaba ɗaya ba ko me?"
"Iya abin da na siyo kenan na dafa" na bashi amsa ba tare da na kalle shi ba, sai na ji ya ce
"Au, dama ba Gara aka kawi miki ba?". Na yi tsam kafin na waiwaya na kalle shi dan ban fahimci in da maganar sa ta dosa ba, wace Gara kuma yake magana akai?
"Wace irin Gara kuma?" Na tambaye shi ganin ya tsare ni da ido, ya haɗe girar sama ya ce
"Gara kala nawa kika sani?" Nima haɗe tawa girar na yi na ce
"Nasan dai ana Garar aure ta al'ada, idan ita kake magana kuma an yi mun" na bashi amsa ina cigaba da cin abincin gabana. Sai ji na yi ya d
Sake cewa
"Kawai ki ce saboda mugun hali ku a gidan ku bakwa yin Garar haihuwa ko kuma kece ba za'a yi wa ba tun da ba'a sona?"
Mamaki, takaici da haushi duk suka kamani lokaci ɗaya. Bilal dai ba zai canza hali ba, sam bakin sa ba zai taɓa koyon tauna kalami kafin ya furta su ba. Gyara zama na yi na kalle shi da kyau na ce
"Muguntar ce ta saka aka baka aure na, duk a cikin muguntar aka cika maka gida da kayan ɗaki aka kuma haɗo ni da kayan abincin da har yau shekara biyu auren mu babu wata uku kake ci a cikin su ba. Sharaɗin ciyarwa akan Namiji ya ke ba Mace ba, haƙƙin ka ne da ka kawo mun abin da zan ci a cikin gidan nan ba wai ka zauna kana jiran a kawo daga gidan mu ba, baka ga duk ƙoƙarin da aka yi maka a baya ba ashe kai nan jira ma kake yi bayan Garar aure a sake lodo ta haihuwa a sake kawowa kenan? Sannu Bilal" Na faɗa ina tsare shi da ido.
"Gori zaki yi mun kenan?" Ya faɗa lokaci ɗaya fuskar sa na rinewa da ɓacin rai. Na ture kwanon gaba na na miƙe na ce
"Gaskiya ce kawai na faɗa ba gori na maka ba, na zata ai yau sabon muna da kayan abinci ya sa ka manta ka fita ba tare da ka bar mun abinda zan ci ba ashe kai duk a tunanin za'a kawo mun Gara daga gidan mu".
Ya mun kallon bani da lokacin ki a yanzu kafin yayi tashin Magajin Dagacin Ƙauye da Al'amin a hannun sa, na yi ta jira ya dawo ya rufe ni da masifar da ya saba amma shiru har na gama tunane tunane na bacci ya kwashe ni bai shigo ba balle ya dawo da Al'amin ɗin sai cikin dare na farka na ganshi a kusa da ni.
Bayan na yi fitsari na canza masa diaper muka sake komawa bacci. Gurin ƙarfe bakwai da rabi ina tsaka da mopping dan tun asuba da na tashi sallah shima Al'amin ya farka ya kuma ƙi komawa dan haka na goya shi kawai na shiga aika ce aika ce na naji ana buga get, Hijab na zura na fita, jin muryar Sunusi maigadin maƙwaftan mu ya saka na buɗe kofar.
Ya gaishe ni na amsa ina mamakin tsadadden warmer na da na gani a hannun sa, a iya tunani na ban tuna sanda na fitar da shi ba da har zai je hannun Sunusi. Miƙo mun ya yi da baƙar leda na karɓa ina masa kallon rashin fahimta ya ce
"Yallaɓai ne ya bani tun jiya da dare ya ce a siyo Ƙosai da Kunu".
A kan dining na ajiye kayan na buɗe Ƙosan da basu fi ƙwaya goma sha biyar ba na rufe, Kunun ma ƙulli biyu ne tsululu da shi da gani ma na masara ne ina jin ko ɗumin kirki babu sai wani ƙullin sugar abin dai kamar na rusa kuka saboda takaici. A gurin na barsu na cigaba da abinda nake yi ina jiyo motsin buɗe ƙofar sa lokacin ina mopping kan barander dan tun da ya dawo daga masallaci na jiyo shi yana share compound ɗin ya kuma wanke na ɗauka ma harda barander ya wanke sai da na fita karɓo ƙosan na ga gurin da datti shine na sake shareta na goge.
Fuska ba yabo ba fallasa ya tsaya yana kallo na, na gaishe shi daga in da nake tsaye ina ɗauraye mopper ya amsa kafin ya shige cikin falon. Sai da na shanya mopper na kwashe kayan wankin da na manta ban ɗauke ba jiya kafin na shiga falon nima.
"Ina abin karyawa?" Ya faɗa dai dai ina ƙoƙarin shigewa ɗaki na, na nuna masa kan dining ba tare da na ce komai ba na shige ɗakin, ban fito ba sai da na yi wanka na yiwa Al'amin na tarar ya bar mun Ƙosan guda bakwai sai ƙullin Kunu ɗaya, Hijabi kawai na saka na goya Al'amin bayan na juye Ƙosan a farar leda na fita da su na bawa wani Almajiri sannan na wuce kanti na siyo abinda nake buƙata. Sai bayan na gama karyawa sannan na lura da dubu ɗayar dake ajiye kan dining da yar takarda a samanta na ɗauka na buɗe
"Ga kuɗin cefane nan" abinda ya rubuta a jiki kenan. Na ringa juya dubu ɗayar ina kallon ta a raina ina lissafa me zan siya da ita?
Cefanen yaushe ma yake nufi na rana kenan ko kuwa har da dare? Da yake na siyo Indomie da rana ita na dafa da ƙwai na ci duk da ba wani ji na yi na ƙoshi ba ni tunda na dawo gidan ma nake ji na kamar wacce ulcer ta kama komai na ci bana ƙoshi ga Al'amin da tsotso har na fara tunanin ko dai na haɗa masa da madara ko zan samu sauƙi.
A hanya bayan na dawo daga cefanen girkin dare wanda sai da na yi cikon dubu uku kafin na samu siyo abinda nake buƙata ina ƙoƙarin buɗe gida na jiyo Maman Yusuf na kiran sunana, sai da na zura ledar hannu na ciki na janyo ƙofar kafin na juya ina murmushi a raina ina addu'ar Allah ya sa bata ga kayan hannu na ba.
"Na aiko Khairat ta ce bakya nan sai Sunusi ya ce kin tafi cefane, maimakon ki bawa Sunusin ko kuma ki aiko nan ko Hauwa ce na turo miki ta yo miki cefanen shine zaki ringa fita da kanki Amarya? Haka jiya ma fa na ganki can bakin titi da tsakar rana har ina cewa mai kama da ke ce ashe dai ke ɗin ce dagaske ni na zata ma Oga ya koma Abujan ne shiyasa kike yawon cefane da kanki ashe yana gari" ta faɗa tana kallo na.
Na yi guntun murmushi na ce
"Aiken sauri ne kin san halin Sunusi kuma idan ka aike shi wani lokacin sai ka manta ma kafin ya dawo Hauwa kuma ai na ji randa kika shigo kin ce ta je gida an musu rasuwa ban san ta dawo ba ai".
Na ɗauka zata wuce amma ta tsaya da alama shiga take so tayi ba'a son raina ba na buɗe ƙofar muka shiga tare. Sai da na kai kayan kitchen kafin na dawo falo muka sake gaisawa ta ce
"Kiyi haƙuri kin sanni da shegen surutu da shiga abun da babu ruwana. Da safe Sunusi ya ce mun maigidan nan ya aike shi siyan ƙosai da Kunu, naga an kwana da wuta Amarya ga blander ki babu abinda bata niƙawa ɗan ƙosan da baifi kiyi na gwangwani biyu kuci har kuyi sadaka ba shine zaki bari a siyo muku a inda baku san tsaftar sa ba? Kunun ma ai gara ki siyo geron kiyi gasara tunda yana so, In da kin aiko ma ni ina da gasarar sai na baki ki dama".
"Ni ce nayi sha'awar kunu da ƙosan ma naga kuma kafin na yi zan ɓata lokaci" na faɗa ina murmushin yaƙe, tayi jumm kamar dai ba iya maganar da ta kawo ta ba kenan kafin kuma ta miƙe tana cewa
"Shikenan dai bari na je dama baya zan zagaya gidan Maman Anisa kin san yaronta da ya tafi makarantar Sojoji Aliyu shine ya faɗo daga sama suna training an dawo da shi gida jinya zan shiga duba shi".
"Ayya Allah ya bashi lafiya ya kiyaye gaba ayi masa sannu" na faɗa ina taka mata, a bakin ƙofa ta tsaya ta ce
"Da babu abinda zakiyi ma se mu je tare tunda ba zama zanyi ba nima"
"Eh wlh girki zan yi da munje taren na faɗa ina kallon Bilal dake tahowa daga ɗakin sa mamakin sanda ya dawo gidan ya kamani, ganin sa ya saka ta wuce ita ma ni kuma na koma ciki.
Sai da aka yi isha'i ya sake shigowa falon lokacin ina cin sauran abincin da ya rage, ya zauna a kusa da ni fuska a sake ya ɗauki Al'amin ya fara masa wasa ni dai kallo ɗaya na masa na mayar da kai na cigaba da cin abincin da nake yi ina kokawa da zuciya ta dake azalzalata akan na tambaye shi wacece JALILA amma na kasa.
"Akwai sauran abincin ne?" Ya tambaye ni, ba tare da na yi magana ba na girgiza masa kai kawai, ya sake cewa
"Ba har dare kika yi girkin gaba ɗaya ba ko me?"
"Iya abin da na siyo kenan na dafa" na bashi amsa ba tare da na kalle shi ba, sai na ji ya ce
"Au, dama ba Gara aka kawi miki ba?". Na yi tsam kafin na waiwaya na kalle shi dan ban fahimci in da maganar sa ta dosa ba, wace Gara kuma yake magana akai?
"Wace irin Gara kuma?" Na tambaye shi ganin ya tsare ni da ido, ya haɗe girar sama ya ce
"Gara kala nawa kika sani?" Nima haɗe tawa girar na yi na ce
"Nasan dai ana Garar aure ta al'ada, idan ita kake magana kuma an yi mun" na bashi amsa ina cigaba da cin abincin gabana. Sai ji na yi ya d
Sake cewa
"Kawai ki ce saboda mugun hali ku a gidan ku bakwa yin Garar haihuwa ko kuma kece ba za'a yi wa ba tun da ba'a sona?"
Mamaki, takaici da haushi duk suka kamani lokaci ɗaya. Bilal dai ba zai canza hali ba, sam bakin sa ba zai taɓa koyon tauna kalami kafin ya furta su ba. Gyara zama na yi na kalle shi da kyau na ce
"Muguntar ce ta saka aka baka aure na, duk a cikin muguntar aka cika maka gida da kayan ɗaki aka kuma haɗo ni da kayan abincin da har yau shekara biyu auren mu babu wata uku kake ci a cikin su ba. Sharaɗin ciyarwa akan Namiji ya ke ba Mace ba, haƙƙin ka ne da ka kawo mun abin da zan ci a cikin gidan nan ba wai ka zauna kana jiran a kawo daga gidan mu ba, baka ga duk ƙoƙarin da aka yi maka a baya ba ashe kai nan jira ma kake yi bayan Garar aure a sake lodo ta haihuwa a sake kawowa kenan? Sannu Bilal" Na faɗa ina tsare shi da ido.
"Gori zaki yi mun kenan?" Ya faɗa lokaci ɗaya fuskar sa na rinewa da ɓacin rai. Na ture kwanon gaba na na miƙe na ce
"Gaskiya ce kawai na faɗa ba gori na maka ba, na zata ai yau sabon muna da kayan abinci ya sa ka manta ka fita ba tare da ka bar mun abinda zan ci ba ashe kai duk a tunanin za'a kawo mun Gara daga gidan mu".
Ya mun kallon bani da lokacin ki a yanzu kafin yayi tashin Magajin Dagacin Ƙauye da Al'amin a hannun sa, na yi ta jira ya dawo ya rufe ni da masifar da ya saba amma shiru har na gama tunane tunane na bacci ya kwashe ni bai shigo ba balle ya dawo da Al'amin ɗin sai cikin dare na farka na ganshi a kusa da ni.
Bayan na yi fitsari na canza masa diaper muka sake komawa bacci. Gurin ƙarfe bakwai da rabi ina tsaka da mopping dan tun asuba da na tashi sallah shima Al'amin ya farka ya kuma ƙi komawa dan haka na goya shi kawai na shiga aika ce aika ce na naji ana buga get, Hijab na zura na fita, jin muryar Sunusi maigadin maƙwaftan mu ya saka na buɗe kofar.
Ya gaishe ni na amsa ina mamakin tsadadden warmer na da na gani a hannun sa, a iya tunani na ban tuna sanda na fitar da shi ba da har zai je hannun Sunusi. Miƙo mun ya yi da baƙar leda na karɓa ina masa kallon rashin fahimta ya ce
"Yallaɓai ne ya bani tun jiya da dare ya ce a siyo Ƙosai da Kunu".
A kan dining na ajiye kayan na buɗe Ƙosan da basu fi ƙwaya goma sha biyar ba na rufe, Kunun ma ƙulli biyu ne tsululu da shi da gani ma na masara ne ina jin ko ɗumin kirki babu sai wani ƙullin sugar abin dai kamar na rusa kuka saboda takaici. A gurin na barsu na cigaba da abinda nake yi ina jiyo motsin buɗe ƙofar sa lokacin ina mopping kan barander dan tun da ya dawo daga masallaci na jiyo shi yana share compound ɗin ya kuma wanke na ɗauka ma harda barander ya wanke sai da na fita karɓo ƙosan na ga gurin da datti shine na sake shareta na goge.
Fuska ba yabo ba fallasa ya tsaya yana kallo na, na gaishe shi daga in da nake tsaye ina ɗauraye mopper ya amsa kafin ya shige cikin falon. Sai da na shanya mopper na kwashe kayan wankin da na manta ban ɗauke ba jiya kafin na shiga falon nima.
"Ina abin karyawa?" Ya faɗa dai dai ina ƙoƙarin shigewa ɗaki na, na nuna masa kan dining ba tare da na ce komai ba na shige ɗakin, ban fito ba sai da na yi wanka na yiwa Al'amin na tarar ya bar mun Ƙosan guda bakwai sai ƙullin Kunu ɗaya, Hijabi kawai na saka na goya Al'amin bayan na juye Ƙosan a farar leda na fita da su na bawa wani Almajiri sannan na wuce kanti na siyo abinda nake buƙata. Sai bayan na gama karyawa sannan na lura da dubu ɗayar dake ajiye kan dining da yar takarda a samanta na ɗauka na buɗe
"Ga kuɗin cefane nan" abinda ya rubuta a jiki kenan. Na ringa juya dubu ɗayar ina kallon ta a raina ina lissafa me zan siya da ita?
Cefanen yaushe ma yake nufi na rana kenan ko kuwa har da dare? Da yake na siyo Indomie da rana ita na dafa da ƙwai na ci duk da ba wani ji na yi na ƙoshi ba ni tunda na dawo gidan ma nake ji na kamar wacce ulcer ta kama komai na ci bana ƙoshi ga Al'amin da tsotso har na fara tunanin ko dai na haɗa masa da madara ko zan samu sauƙi.
A hanya bayan na dawo daga cefanen girkin dare wanda sai da na yi cikon dubu uku kafin na samu siyo abinda nake buƙata ina ƙoƙarin buɗe gida na jiyo Maman Yusuf na kiran sunana, sai da na zura ledar hannu na ciki na janyo ƙofar kafin na juya ina murmushi a raina ina addu'ar Allah ya sa bata ga kayan hannu na ba.
"Na aiko Khairat ta ce bakya nan sai Sunusi ya ce kin tafi cefane, maimakon ki bawa Sunusin ko kuma ki aiko nan ko Hauwa ce na turo miki ta yo miki cefanen shine zaki ringa fita da kanki Amarya? Haka jiya ma fa na ganki can bakin titi da tsakar rana har ina cewa mai kama da ke ce ashe dai ke ɗin ce dagaske ni na zata ma Oga ya koma Abujan ne shiyasa kike yawon cefane da kanki ashe yana gari" ta faɗa tana kallo na.
Na yi guntun murmushi na ce
"Aiken sauri ne kin san halin Sunusi kuma idan ka aike shi wani lokacin sai ka manta ma kafin ya dawo Hauwa kuma ai na ji randa kika shigo kin ce ta je gida an musu rasuwa ban san ta dawo ba ai".
Na ɗauka zata wuce amma ta tsaya da alama shiga take so tayi ba'a son raina ba na buɗe ƙofar muka shiga tare. Sai da na kai kayan kitchen kafin na dawo falo muka sake gaisawa ta ce
"Kiyi haƙuri kin sanni da shegen surutu da shiga abun da babu ruwana. Da safe Sunusi ya ce mun maigidan nan ya aike shi siyan ƙosai da Kunu, naga an kwana da wuta Amarya ga blander ki babu abinda bata niƙawa ɗan ƙosan da baifi kiyi na gwangwani biyu kuci har kuyi sadaka ba shine zaki bari a siyo muku a inda baku san tsaftar sa ba? Kunun ma ai gara ki siyo geron kiyi gasara tunda yana so, In da kin aiko ma ni ina da gasarar sai na baki ki dama".
"Ni ce nayi sha'awar kunu da ƙosan ma naga kuma kafin na yi zan ɓata lokaci" na faɗa ina murmushin yaƙe, tayi jumm kamar dai ba iya maganar da ta kawo ta ba kenan kafin kuma ta miƙe tana cewa
"Shikenan dai bari na je dama baya zan zagaya gidan Maman Anisa kin san yaronta da ya tafi makarantar Sojoji Aliyu shine ya faɗo daga sama suna training an dawo da shi gida jinya zan shiga duba shi".
"Ayya Allah ya bashi lafiya ya kiyaye gaba ayi masa sannu" na faɗa ina taka mata, a bakin ƙofa ta tsaya ta ce
"Da babu abinda zakiyi ma se mu je tare tunda ba zama zanyi ba nima"
"Eh wlh girki zan yi da munje taren na faɗa ina kallon Bilal dake tahowa daga ɗakin sa mamakin sanda ya dawo gidan ya kamani, ganin sa ya saka ta wuce ita ma ni kuma na koma ciki.