Sashe 110
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta zauna kan bedside drawer fuska a washe tana kallo na ta ce
"Ta Bilal bada kanki a sare ya jikin?" Ba tareda na kalleta ba na amsa da cewa
"Da sauƙi" na ɗora da gaisheta. Ta amsa ta ce
"Ashe kuma haka abu ya faru? Toh Allah ya kiyaye gaba ya sa ya zame miki kaffara". Na ɗaga kai na kalleta dan ban fahimci mai take nufi ba, maimakon ta ƙara mun bayani sai ta ce
"Na tambayi Mama yaushe za'a je kwaso kaya ta ce ke za'a tambaya, yaushe zamuje? Dan na ji an ce ranar asabar amarya zata tare ko kin bar musu kayan naki ne da su zata tare?"
Sai lokacin na ɗaga kai na kalleta kamar mai tsoron magana na ce
"Anty ya aiko da takardar ne?"
"Au jiyan haka kika fito ziƙau baki musu aika aika kin kuma karɓo tikitin yancin ki ba?" Ta maida mun da tambaya. Ƙasa na sauke kaina hawaye suka ɓalle mun Anty Labiba ta ce
"Toh Allah ya rufa asiri, daga yau zuwa gobe dai ki san me kike ciki gaskiya in za'a je kwaso kayan toh in ma ba za'a je ba dai mu sani da wuri" daga haka ta miƙe ta fita tareda Al'amin.
BILAL
Kasa zaune yayi tunda sukayi waya da Anty Amina da safe ta ce masa ta yarda zataje gidansu Halima amma tareda Yaya Aminu zasuje. Dukda ba haka ya so ba amma babu yanda ya iya, in dai Haliman zata dawo shine muradin sa a yanzu.
Sai da ya dai dai ci lokacin ya kamata ace sun isa gidan su Halimar har sun gama abinda ya kai su kafin ya kunna wayarsa dan tun farar safiya Zulaiha ta dira masa kira akan Kawunsu yana son ganinsa yau. Kasa gane wasu maganganu da take masa akan wai idan ya je duk abinda Kawun ya ce masa ya ce Eh ya sani, kawai ya katse wayar bayan ya ce mata bari zai kirata yanzu shikenan ya kasheta gaba ɗaya dan ya san kira zatayi tayi ba zata ƙyale shi ba.
Shi kam tun da aka ɗaura musu aure yake ganin sababbin halayenta da a baya bai san da su ba abun na ɗaure masa kai yana kuma bashi mamaki amma yanayin da yake ciki a yanzu ya sa baya bari abun ya dame shi a rai kawai yake mata uzuri koma menene ya san idan suka zauna zai dai daita.
Wayar na kunnuwa message ɗin Anty Amina ya shigo ya buɗe ya karanta 'wayarka a kashe, idan ka kunna ka sameni a gidan Hajja yanzun nan' abinda ta rubuta kenan.
Muƙullin mota ya ɗauka ya fita dukda bai so ta ce su haɗu a gidan Hajjan ba amma kuma ita ɗin dai dama ita zata gayawa Hajja zancen dawowar Haliman dan shi ba zai iya ba. Basu gama da Zulaiha ba ma balle ya sakw ɓallo wata rigimar.
Motar Yaya Aminu da ya gani ya saka ya ji tamkar ya juya amma ya makara dan suna tsaye a ƙofar gidan shi da Baba Sani suna magana, ya gama ƙunƙunin sa kafin ya fito ya shige cikin gidan ba tareda ya ko tsaya ya gaishe su ba. Yaya Aminu dake kallon sa ya yi ƙwafa ya ce
"Kana kallon yaron nan yanda ya wuce mu wato bamu ma ishe shi kallo ba kenan"
"Haƙuri za'a yi Aminu, yayan yau sai a barsu da halin su kawai amma ban taɓa zaton samun Bilal da irin haka ba, ni har na rasa abin cewa ma wlh gaba ɗaya" cewar Baba Sani. Yaya Aminu bai tanka ba ya juya suka shiga cikin gidan.
Daga yanda Bilal ya tarar da Anty Amina ya san cewa tafiya ba tayi yanda ake so ba. Gefe ya samu ya zauna kan kujera ya shiga gaida Hajja da tayi masa banza tamkar bata ji shigowarsa ba, ya juya kan Anty Aminan itama a ɗage ta amsa tana maka masa hararar da bai san dalili ba. Yaya Aminu da Baba Sani suka shigo kowa ya samu guri ya zauna.
Tunda Yaya Aminub ya buɗe baki ya ringa ji ina ma ƙasa ta buɗe ya shige ciki ko kuma ya ɓace ɓat daga gurin ko ya samu sauƙin tashin hankali, kunya da nadamar da suka masa rubdugu lokaci ɗaya. Zufa ta ringa keto masa, tsabar yanda ya duƙar da kai take wuyansa ya fara ciwo amma bai ko yi yunƙurin ɗagowa ya gyara zama ba balle yayi kuskuren haɗa ido da wani daga cikinsu.
A duk cikin maganganun babu abinda yafi ɗaga masa hankali irin cewar da Yaya Aminun yayi wai mahaifin Halima ne duk ya faɗa masa waɗannan maganganun, ya akayi Abba ya san alaƙar aa da Jalilah? Yanzu dama Halima bata rufa masa asiri ba kamar yanda yake zato duk ta faɗa musu komai?
Ya ringa share zufar dake keto masa, Yaya Aminu kuwa kamar zai aro baki tsabar masifa. Anty Amina sai ƙafa take jijjigawa dan tun a mota bayan sun baro gidansu Halima Yaya Aminun ya balbaleta da masifa akan me zata zubar masa da mutunchi ta sako shi cikin wannan maganar bayan ta san ta'asar da Bilal ɗin yake aikatawa? Ta sha mamaki har ta kasa cewa komai domin idan ba dan ta san babu wani dalili da zai saka Abban Halima yayi wa Bilal irin wannan ƙazafin ba da zata iya musawa. Ko da wasa wani ya ce mata Bilal ɗin mutumin banza ne haka zata ƙaryata domin dai duk mugun halin Hajja da son zuciyarta tayi ƙoƙari gurin basu tarbiyya ta san kuma da saninta Bilal ba zai aikata irin abun nan kuma tayi shiru ba.
Sai dai kuma Hajjan ta shayar da ita mamaki domin bata zaci irin amsar da ta ji daga bakinta bayan Aminun ya gama zazzaga masifarsa ba. Kuka Hajjan ta fashe da shi tana cewa
"Wannan yarinya Halima ban san me take nema damu ba, yanzu a duniya ta rasa sharrin d zata bibiyi Bilal da shi sai ta masa ƙazafin nema mata? Wlh Allah ya isa tsakaninmu da su kuma maganar nan ba zamu barta ba sai munyi shari'a da su ba ta isa ta ɓatawa ɗana suna a banza ba sai naga uban da ya tsaya mata".
A zuciya Yaya Aminu ya ce
"Wlh Hajja kiji tsoron Allah, ai duk abinda ya zama kece sila domin ya sani duk aje a dawo zaki san yanda zakiyi ki kare shi. Tun ba yanzu ba duk iskancin sa yakeyi da yanda ya ringa azabar da yarinyar nan kina kallo amma baki taɓa tsawatar masa ba sai ma ƙara zugashi da kike yi kin ɗauki karan tsana kin ɗora mata saboda dama ba dan Allah kuka ƙulla auren ba kin so iyayenta su zame me muku bayi sai yanda kukayi da su da dukiyar su da baki samu haka bane shine kika uzzuraqa yar su ba kalar uƙuba da jidalin da baku mata ba amma ta jure take zaune da shi.
Saboda shegen ƙwadayi da son abin duniya ya rufe miku ido baki taɓa tunanin a ina ya samu kuɗi lokaci ɗaya da yake buƙatu da suka zarce samunsa ba, ke dai kawai tunda yana kawo miki baki damu da ina yake samowa ba. Wlh da ace Mahaifin mu zai dawo doron duniya sai yayi ala wadai da irin tarbiyyar da kika ɗora yaran nan a bayan babu shi.
Abin takaici abin baƙin ciki ɗan ki ya zama karuwa, bama shi yake neman matan yana kashe musu kuɗi ba saboda mutuwar zuciya shi yake biyawa mace buƙata tana bashi kuɗi wlh tallahi kayi asara Bilal ka kuma zubar da ƙima da mutunchinka a idon duk wanda suke maka kallon mutumin kirki".
"Idan baka daina jifan ɗana da mugayen kalamai ba Aminu wlh idan na tashi kai ƙara harda kai zan haɗa, dama ai ba ƙaunar mu kukeyi ba. Tunda ubanku ya mutu aka raba gado a cikinku waye ya sake waiwayarmu sai yau da yake sharri ne shine zaka zo kana tada jijiyoyin wuya kana faɗar maganganu son ranka toh wlh ka kiyaye ni" Hajja ta taso masa. Sai lokacin Baba Sani ya ce
"Wannan shine babbar matsalarki Hajara ƙin gaskiya kuma ban san lokacin da kika zama haka ba"
"Eh ai dama zaka faɗi haka tunda ka gama lasa a nan yanzu ka koma gindinsu zaka cigaba da maula a haka dai zaka ƙare karen farauta kawai" ta zaburowa Baba Sanin.
Aminu ya miƙe yana cewa
"Tun da sauran mutunchi ka rubuta takarda ka aika musu da ita dan mahaifinta ya ce idan ka bari satin nan ya wuce baka sakar masa yar sa ba ƙarar ka zaiyi, wlh kayi asara, kuma haƙƙin wannan yarinyar kaɗai idan kayi wasa ba zai barka ka zauna lafiya ba domin karamchi ba kalar wanda ita da iyayenta basu maka ba amma ka butulche musu ka zaɓi hanyar banza ta saɓawa ubangiji" daga haka ya sa kai ya fice daga falon ba tareda ya saurari Hajja dake zaginsa ba.
Baba Sani ma tashi yayi ya bi bayansa ba tareda ya sake cewa komai ba. Suna fita Hajja ta miƙe ta rufe ƙofa harda saka sakata kafin ta koma ta zauna tana kallon Bilal da yake nan zaune kamar mara rai ta ce
"Menene gaskiyar abinda suka faɗa?"
Sai lokacin ya ɗaga kai amma ba duka ba ba tareda ya kalleta ba ya ce
"Kiyi haƙuri Hajja"
"Ba haƙuri zaka bani ba Bilal cewa nayi ka gaya mun gaskiya akan maganar da suka faɗa, da gaske ne matan banza kake bi a waje ko sharri sukayi maka?"
Sai da ya rintse ido kafin ya ce
"Guda ɗaya ce, Jalilah. Kuma wlh ba abinda suke zato bane kawai yan ƙananan abubuw....." Bai kai ƙarshen maganar ba ta katse shi ta hanyar sharara masa marin da sai da yayi baya saboda bai shirya masa ba. Kuka mai haɗe da gunji ta fashe da shi tana cewa
[5/11, 9:38 AM] +234 810 691 6476: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
"Ta Bilal bada kanki a sare ya jikin?" Ba tareda na kalleta ba na amsa da cewa
"Da sauƙi" na ɗora da gaisheta. Ta amsa ta ce
"Ashe kuma haka abu ya faru? Toh Allah ya kiyaye gaba ya sa ya zame miki kaffara". Na ɗaga kai na kalleta dan ban fahimci mai take nufi ba, maimakon ta ƙara mun bayani sai ta ce
"Na tambayi Mama yaushe za'a je kwaso kaya ta ce ke za'a tambaya, yaushe zamuje? Dan na ji an ce ranar asabar amarya zata tare ko kin bar musu kayan naki ne da su zata tare?"
Sai lokacin na ɗaga kai na kalleta kamar mai tsoron magana na ce
"Anty ya aiko da takardar ne?"
"Au jiyan haka kika fito ziƙau baki musu aika aika kin kuma karɓo tikitin yancin ki ba?" Ta maida mun da tambaya. Ƙasa na sauke kaina hawaye suka ɓalle mun Anty Labiba ta ce
"Toh Allah ya rufa asiri, daga yau zuwa gobe dai ki san me kike ciki gaskiya in za'a je kwaso kayan toh in ma ba za'a je ba dai mu sani da wuri" daga haka ta miƙe ta fita tareda Al'amin.
BILAL
Kasa zaune yayi tunda sukayi waya da Anty Amina da safe ta ce masa ta yarda zataje gidansu Halima amma tareda Yaya Aminu zasuje. Dukda ba haka ya so ba amma babu yanda ya iya, in dai Haliman zata dawo shine muradin sa a yanzu.
Sai da ya dai dai ci lokacin ya kamata ace sun isa gidan su Halimar har sun gama abinda ya kai su kafin ya kunna wayarsa dan tun farar safiya Zulaiha ta dira masa kira akan Kawunsu yana son ganinsa yau. Kasa gane wasu maganganu da take masa akan wai idan ya je duk abinda Kawun ya ce masa ya ce Eh ya sani, kawai ya katse wayar bayan ya ce mata bari zai kirata yanzu shikenan ya kasheta gaba ɗaya dan ya san kira zatayi tayi ba zata ƙyale shi ba.
Shi kam tun da aka ɗaura musu aure yake ganin sababbin halayenta da a baya bai san da su ba abun na ɗaure masa kai yana kuma bashi mamaki amma yanayin da yake ciki a yanzu ya sa baya bari abun ya dame shi a rai kawai yake mata uzuri koma menene ya san idan suka zauna zai dai daita.
Wayar na kunnuwa message ɗin Anty Amina ya shigo ya buɗe ya karanta 'wayarka a kashe, idan ka kunna ka sameni a gidan Hajja yanzun nan' abinda ta rubuta kenan.
Muƙullin mota ya ɗauka ya fita dukda bai so ta ce su haɗu a gidan Hajjan ba amma kuma ita ɗin dai dama ita zata gayawa Hajja zancen dawowar Haliman dan shi ba zai iya ba. Basu gama da Zulaiha ba ma balle ya sakw ɓallo wata rigimar.
Motar Yaya Aminu da ya gani ya saka ya ji tamkar ya juya amma ya makara dan suna tsaye a ƙofar gidan shi da Baba Sani suna magana, ya gama ƙunƙunin sa kafin ya fito ya shige cikin gidan ba tareda ya ko tsaya ya gaishe su ba. Yaya Aminu dake kallon sa ya yi ƙwafa ya ce
"Kana kallon yaron nan yanda ya wuce mu wato bamu ma ishe shi kallo ba kenan"
"Haƙuri za'a yi Aminu, yayan yau sai a barsu da halin su kawai amma ban taɓa zaton samun Bilal da irin haka ba, ni har na rasa abin cewa ma wlh gaba ɗaya" cewar Baba Sani. Yaya Aminu bai tanka ba ya juya suka shiga cikin gidan.
Daga yanda Bilal ya tarar da Anty Amina ya san cewa tafiya ba tayi yanda ake so ba. Gefe ya samu ya zauna kan kujera ya shiga gaida Hajja da tayi masa banza tamkar bata ji shigowarsa ba, ya juya kan Anty Aminan itama a ɗage ta amsa tana maka masa hararar da bai san dalili ba. Yaya Aminu da Baba Sani suka shigo kowa ya samu guri ya zauna.
Tunda Yaya Aminub ya buɗe baki ya ringa ji ina ma ƙasa ta buɗe ya shige ciki ko kuma ya ɓace ɓat daga gurin ko ya samu sauƙin tashin hankali, kunya da nadamar da suka masa rubdugu lokaci ɗaya. Zufa ta ringa keto masa, tsabar yanda ya duƙar da kai take wuyansa ya fara ciwo amma bai ko yi yunƙurin ɗagowa ya gyara zama ba balle yayi kuskuren haɗa ido da wani daga cikinsu.
A duk cikin maganganun babu abinda yafi ɗaga masa hankali irin cewar da Yaya Aminun yayi wai mahaifin Halima ne duk ya faɗa masa waɗannan maganganun, ya akayi Abba ya san alaƙar aa da Jalilah? Yanzu dama Halima bata rufa masa asiri ba kamar yanda yake zato duk ta faɗa musu komai?
Ya ringa share zufar dake keto masa, Yaya Aminu kuwa kamar zai aro baki tsabar masifa. Anty Amina sai ƙafa take jijjigawa dan tun a mota bayan sun baro gidansu Halima Yaya Aminun ya balbaleta da masifa akan me zata zubar masa da mutunchi ta sako shi cikin wannan maganar bayan ta san ta'asar da Bilal ɗin yake aikatawa? Ta sha mamaki har ta kasa cewa komai domin idan ba dan ta san babu wani dalili da zai saka Abban Halima yayi wa Bilal irin wannan ƙazafin ba da zata iya musawa. Ko da wasa wani ya ce mata Bilal ɗin mutumin banza ne haka zata ƙaryata domin dai duk mugun halin Hajja da son zuciyarta tayi ƙoƙari gurin basu tarbiyya ta san kuma da saninta Bilal ba zai aikata irin abun nan kuma tayi shiru ba.
Sai dai kuma Hajjan ta shayar da ita mamaki domin bata zaci irin amsar da ta ji daga bakinta bayan Aminun ya gama zazzaga masifarsa ba. Kuka Hajjan ta fashe da shi tana cewa
"Wannan yarinya Halima ban san me take nema damu ba, yanzu a duniya ta rasa sharrin d zata bibiyi Bilal da shi sai ta masa ƙazafin nema mata? Wlh Allah ya isa tsakaninmu da su kuma maganar nan ba zamu barta ba sai munyi shari'a da su ba ta isa ta ɓatawa ɗana suna a banza ba sai naga uban da ya tsaya mata".
A zuciya Yaya Aminu ya ce
"Wlh Hajja kiji tsoron Allah, ai duk abinda ya zama kece sila domin ya sani duk aje a dawo zaki san yanda zakiyi ki kare shi. Tun ba yanzu ba duk iskancin sa yakeyi da yanda ya ringa azabar da yarinyar nan kina kallo amma baki taɓa tsawatar masa ba sai ma ƙara zugashi da kike yi kin ɗauki karan tsana kin ɗora mata saboda dama ba dan Allah kuka ƙulla auren ba kin so iyayenta su zame me muku bayi sai yanda kukayi da su da dukiyar su da baki samu haka bane shine kika uzzuraqa yar su ba kalar uƙuba da jidalin da baku mata ba amma ta jure take zaune da shi.
Saboda shegen ƙwadayi da son abin duniya ya rufe miku ido baki taɓa tunanin a ina ya samu kuɗi lokaci ɗaya da yake buƙatu da suka zarce samunsa ba, ke dai kawai tunda yana kawo miki baki damu da ina yake samowa ba. Wlh da ace Mahaifin mu zai dawo doron duniya sai yayi ala wadai da irin tarbiyyar da kika ɗora yaran nan a bayan babu shi.
Abin takaici abin baƙin ciki ɗan ki ya zama karuwa, bama shi yake neman matan yana kashe musu kuɗi ba saboda mutuwar zuciya shi yake biyawa mace buƙata tana bashi kuɗi wlh tallahi kayi asara Bilal ka kuma zubar da ƙima da mutunchinka a idon duk wanda suke maka kallon mutumin kirki".
"Idan baka daina jifan ɗana da mugayen kalamai ba Aminu wlh idan na tashi kai ƙara harda kai zan haɗa, dama ai ba ƙaunar mu kukeyi ba. Tunda ubanku ya mutu aka raba gado a cikinku waye ya sake waiwayarmu sai yau da yake sharri ne shine zaka zo kana tada jijiyoyin wuya kana faɗar maganganu son ranka toh wlh ka kiyaye ni" Hajja ta taso masa. Sai lokacin Baba Sani ya ce
"Wannan shine babbar matsalarki Hajara ƙin gaskiya kuma ban san lokacin da kika zama haka ba"
"Eh ai dama zaka faɗi haka tunda ka gama lasa a nan yanzu ka koma gindinsu zaka cigaba da maula a haka dai zaka ƙare karen farauta kawai" ta zaburowa Baba Sanin.
Aminu ya miƙe yana cewa
"Tun da sauran mutunchi ka rubuta takarda ka aika musu da ita dan mahaifinta ya ce idan ka bari satin nan ya wuce baka sakar masa yar sa ba ƙarar ka zaiyi, wlh kayi asara, kuma haƙƙin wannan yarinyar kaɗai idan kayi wasa ba zai barka ka zauna lafiya ba domin karamchi ba kalar wanda ita da iyayenta basu maka ba amma ka butulche musu ka zaɓi hanyar banza ta saɓawa ubangiji" daga haka ya sa kai ya fice daga falon ba tareda ya saurari Hajja dake zaginsa ba.
Baba Sani ma tashi yayi ya bi bayansa ba tareda ya sake cewa komai ba. Suna fita Hajja ta miƙe ta rufe ƙofa harda saka sakata kafin ta koma ta zauna tana kallon Bilal da yake nan zaune kamar mara rai ta ce
"Menene gaskiyar abinda suka faɗa?"
Sai lokacin ya ɗaga kai amma ba duka ba ba tareda ya kalleta ba ya ce
"Kiyi haƙuri Hajja"
"Ba haƙuri zaka bani ba Bilal cewa nayi ka gaya mun gaskiya akan maganar da suka faɗa, da gaske ne matan banza kake bi a waje ko sharri sukayi maka?"
Sai da ya rintse ido kafin ya ce
"Guda ɗaya ce, Jalilah. Kuma wlh ba abinda suke zato bane kawai yan ƙananan abubuw....." Bai kai ƙarshen maganar ba ta katse shi ta hanyar sharara masa marin da sai da yayi baya saboda bai shirya masa ba. Kuka mai haɗe da gunji ta fashe da shi tana cewa
[5/11, 9:38 AM] +234 810 691 6476: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*