Sashe 143
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsaki yayi ya kashe wayar kafin ya kunna motar yana tafe yana tunani wane mace da Namiji ne zasuje gurinsa? Hafiz ya kawo da matarsa dan shi kaɗai ne dai yake tunani dukda baya zaton ganin Hafiz a gidansa saboda tun ranar daya sanar masa daya saki Halima ɗan shirin da suka dawo yi ya sake ja baya balle matarsa daya fahimci ta ma fishi ɗaukar ɗumi akan lamarin.
Bai gane motar daya gani a ajiye ba dan haka shima yayi parking a waje ya kuma tsaya yaƙi shiga gidan wani abu mai kama da tsoro ko fargaba ya ɗarsu a ransa, to wai wane baƙo ne haka da shi ba zai kirashi a waya ba sai dai Zulaiha? Kuma da yace ta basu waya yaji su waye suka ƙi karɓa wai surprise zasu yi masa. Ƙarfin hali yayi ya buɗe gidan ya shiga yana ayyana koma dai menene ya san ba abin cutarwa bane tunda bai ji wata fargaba ko tsoro tattare da Zulaihan ba.
Takalmin mace da namiji, bai gane na namijin ba amma na macen tsinin takalman kawai ya gani ya fahimci na wanene, gabansa ya yanke ya faɗi lokaci ɗaya kuma kansa ya sara, cikin takatsantsan kamar wani ɓarawo ya juya da niyyar komawa muryar Zulaiha da yaji a bayansa ta saka yaci burki ya shiga mayar da numfashi kamar wanda yayi gudu.
"Allah ya so ka da kunyi saɓani" ta faɗa, sai da yayi matuƙar ƙoƙarin gurin saita yanayinsa kafin ya juya ya kalleta yana ɗan murmushi ya ce
"Ina baƙin?"
"Suna ciki shirin tafiya ma sukeyi, gaka nan gaka nan tun ɗazu sai kace wanda ya taho daga Kaduna ai da sun tafi ka huta kuma ga wani saƙon can an kawo maka sammaci daga kotu" ta sake faɗa hankali kwance ta wuce shi ta shige ɗakin Solar. Nepa aka ɗauke shine ta fito zata canza ta ganshi dan basu ji motsin buɗe get ɗin ba ma.
Dafe kansa daya sake sarawa yayi yana nanata sammaci a zuciyarsa, Sai da ya ga zata fito kafin ya lallaɓa ya nufi falon yana ƙaƙalo murmushi a ransa yana haɗa kalaman da zaiyi amfani dasu gurin yi musu magana, Hafiz da Jalilah suka ɗaga kai a tare suka kalle shi haɗi da amsa masa sallama. Ya saki murmushin yaƙe ya nufi Hafiz ya bashi hannu suka gaisa yana cewa
"Lallai kuwa an bani babban surprise, kuma da na san kaine da zance mata karta buɗe maka ƙofa"
Fuska ba yabo ba fallasa Hafiz ya ce
"Idan ni ba'a barni na shigo ba ai ba za'a hana uwarɗakinka shigowa ba ko ba haka ba Hajjaju?" Yayi maganar yana kallon inda Jalilah ke zaune ta harɗe ƙafafu tana latsa waya sai ka rantse bata san da wanzuwarsu a gurin ba.
Murmushin daya saka zuciyar Bilal fara gudun wuce ƙa'ida tayi kafin ta ce
"Ni da aka ɓoyewa amaryar ai ni naci albarkacinka". Ya haɗiye miyau kafin ya samu guri ya zauna yana kallonta ya ce
"Ranki ya daɗe yaushe a gari?"
"Zuwana kenan" ta bashi amsa tana gyara zama idonta akansa. Gyara zama yayi yana murmushin da gara kawai a bashi fili ya fashe da kuka, magan yake so yayi amma wai duk tarin kalaman kare kai daya ke da haddarsu a ka duk wacce ya kamo sai ta zille ya rasa kalaman da zai haɗa yayi magana sai kawai yayi shiru ya sadda kai ƙasa kamar wanda Alƙali ya tsura. Can ya miƙe ganin ba'a ajiye musu ko ledar pure water ba ya shiga kiran Zulaiha, tana ƙofar ɗakin Solar tana replying message ɗin da Ahlan ya turo mata.
Sunyi akan zasu haɗu yau tunda zataje gidan Hajja tana tsaka da shiri baƙin Bilal ɗin sukazo haushin rusa mata plan ya sa ko ruwa bata basu ba suna zaune sama da awa guda kenan suna jiransa. A bakin ƙofa suka haɗu zata shiga shi kuma zai fito yayi ƙasa da murya yana ce mata
"Babu wani abun taɓawa ne a gidan da ba ki basu ba naga ko ruwa ma baki ajiye musu ba?"
"Babu, ruwa kuma pure water muke dashi kuma naga su ɗin ba kalarsa bane shiyasa ban basu ba" ta bashi amsa, ya maka mata harara ya ce
"Ina dambun naman dana gani jiya? Kuma yau kwana nawa dana siyo ruwa katan biyu? Nufinki kin shanye ko me? Kuma ai akwai lemo a fridge kawai kice so kike ki wulaƙanta ni shiyasa kika wulaƙanta baƙi na" yayi tsaki ya koma ciki tabi bayansa. Kitchen suka shiga ya ɗauki try ya kwashi ruwan da tace babu dukda babu sanyi ya ɗora akai, da mamaki ya kalleta bayan daya buɗe fridge ɗin; lemuka kala kala a ciki harda Champagne. Gefe ta ɗauke kai, yayi ƙwafa ya kwashi lemukan ya haɗa da cake ɗin daya gani ya fita ya ajiye musu.
Hafiz da Jalilah suka bishi da kallo, dariya ce ta kama Hafiz ya danneta amma dukda haka saida wata ta fito sai ya fake da tari Bilal ya shiga yi masa sannu kafin ya koma ya kofuna ya ajiye musu ya bi Zulaiha data shige ɗaki da harara duk akan idon Hafiz, sai ya girgiza kai kawai ya ɗauki kofi ya tsiyaya lemo ya miƙawa Jalilah bata karɓa ba ta masa alamar aa da hannu tana cigaba da danna waya, ya karɓi kaɗan kafin ya kalli Bilal ya ce
"Su Al'amin fa?"
"Suna can gurin Mamansu" ya bashi amsa yana satar kallon Jalilah. Hafiz ya sake cewa
"Allah sarki, kwanaki na ganta kuwa a Alpen ina ta ɗaga mata hannu amma bata lura da ni ba, ta canza sosai ta ƙara kyau da farko ma nayi tantamar ita ɗin ce kuwa sai da naga ƙaninta sannan na yarda ita ɗin ce dagaske, gaskiya zawarci ya karɓeta idan ba'a faɗa bama zaka ɗauka budurwa ce wlh".
"Hmmm" kawai Bilal ya iya faɗa take kuma haushin Hafiz ɗin ya kamashi amma dai bai nuna ba yaci gaba da satar kallon Jalilah dake ta danna waya alamar wani abun take rubutawa. Kiran sallar la'asar da aka farayi yasa ta miƙe kamar wacce aka tsikara tana kallon Hafiz tace
"Muje ko?"
"Wai mai ya faru ne gaba ɗaya kin canza ba kamar yanda muka fito ba?" Hafiz ya tambayeta. Ta kalli Bilal kafin ta mayar da kallonta kan Hafiz tayi murmushi tace
"Na gaya maka maganar kayan da aka satar mana a store shine duk ya canza mun mood" ta faɗa tana langwaɓar da gefe kai. Mota ya rakasu basu ja sallamar da nisa ba suka wuce shi kuma ya jingina da ƙofa yana mayar da numfashi. Ta faru ta ƙare anyi wa mai dami ɗaya sata, shi dama ya daɗe yana hasashen shigo shigo ba zurfi kawai Hafiz yake yi masa da yakeyi kamar bashida masaniyar komai akan alaƙarsu, idan ma kuna dagaske ne bai sani ba toh yau kam ya san Jalilah ta gama farke masa laya shiyasa suka haɗo kai suka zo su ƙureshi amma ba zaiyi saurin kaiwa ƙasa ba dole ya nemi mafita domin shirun da Jalilah tayi ya sani tabbas ba alkhairi bane.
Ciki ya koma yana zura kai sukayi karo da Zulaiha dake shirin fitowa, tayi baya ta dafe kai kafin tayi tsaki ta raɓeshi har tana tureshi ta fice ya bi bayanta da kallo. Ɗakinsa ya shiga ya ringa safa da marwa tunani kamar kansa zaiyi bindiga ya tarwatse, yanzu ina zai kama? Jalilah tasan yayi aure da alama kuma tana da masaniya akan shi ya ɗauki kayan idan ma kuma bata sani ba toh tabbatas tana dabda sani bai kuma san irin matakin da zata ɗauka akan hakan ba, ga Alhaji Lawan ya makashi a kotu shi yanzu ina zai tsoma ransa yaji daɗi a faɗin ƙasar nan?
Tsabar ruɗin da yake ciki bai tuna baiyi sallar la'asar ba sai da yaji ana kiran sallar magriba tukunna yayi alwala ya haɗa su yayi. Yana nan zaune gida shi kaɗai har ƙarfe goma Hajja harta gaji da kiransa tun magriba wai suzo suyiwa Fadila faɗa kafin a tafi rakata ko faɗan mai zaiyi mata oho?
Ganin har ƙarfe goman Zulaiha bata dawo ba ya sa ya kirata tace masa suna gidan Amarya ba'a tafi kaita da wuri bane amma yanzu zasu taho. Haka nan zuciyarsa ta raya masa wani abu take kuma yayi na'am da hakan nan da nan ya shiga haɗa abinda zai buƙata a yar jaka, yana haɗa kayan yaji tsayuwar mota a ƙofar gidan, yanda kasan mara gaskiya ya fita da sauri ya leƙa.
A ƙofar gidan motar ta tsaya, ganin an buɗe ƙofa kuma ya saka mai motar yayi gaba, tsaki ya koma ciki amma bai rufe ƙofa ba yana kallon motar dake kunne har sannan. Kusan minti uku yana tsaye kafin ya koma ciki ya ɗauko jakar ya saka a mota ya buɗe Get ya fice.
A daren ya kama hanyar Minjibir, sai da ya nemi abinci yaci dan yunwa yake ji sosai kafin ya karɓi key ɗin ɗaki ya shiga. Wayarsa ya fara kashewa ya saka a cikin drawer bayan ya turawa da Zulaiha saƙo akan tafiyar gaggawa ta sameshi ta tafi gida idan ya dawo zaizo ya ɗauketa sannan yayi wanka ya kwanta bacci.
JALILAH
Tun daga sanda ta tabbatar da yayi blocking ɗin ta ta gasgata abinda zuciyarta ta daɗe tana raya mata akan Bilal yana so yayi amfani da ita ne kawai ya cimma burinsa sannan ya watsar da ita kamar yanda ya yiwa matarsa Halima. Harga Allah da aure take son Bilal dukda banbancin matsayi da yake tsakaninsu amma da yake shi So babu ruwansa da wannan tunda ta ganshi taji yayi mata, tayi masa uzuri a lokacin daya nuna mata cewar ba zai iya aurenta ba wannan dalilin ya saka ta buɗe masa bakin aljihunta a ganinta rashin wadatace ta saka yace ba zai aureta ɗin a lokacin ba amma a maimakon aure sai ya bijiro mata da abinda take ƙoƙarin bari harta yanke hukuncin auren nasa.
Bai gane motar daya gani a ajiye ba dan haka shima yayi parking a waje ya kuma tsaya yaƙi shiga gidan wani abu mai kama da tsoro ko fargaba ya ɗarsu a ransa, to wai wane baƙo ne haka da shi ba zai kirashi a waya ba sai dai Zulaiha? Kuma da yace ta basu waya yaji su waye suka ƙi karɓa wai surprise zasu yi masa. Ƙarfin hali yayi ya buɗe gidan ya shiga yana ayyana koma dai menene ya san ba abin cutarwa bane tunda bai ji wata fargaba ko tsoro tattare da Zulaihan ba.
Takalmin mace da namiji, bai gane na namijin ba amma na macen tsinin takalman kawai ya gani ya fahimci na wanene, gabansa ya yanke ya faɗi lokaci ɗaya kuma kansa ya sara, cikin takatsantsan kamar wani ɓarawo ya juya da niyyar komawa muryar Zulaiha da yaji a bayansa ta saka yaci burki ya shiga mayar da numfashi kamar wanda yayi gudu.
"Allah ya so ka da kunyi saɓani" ta faɗa, sai da yayi matuƙar ƙoƙarin gurin saita yanayinsa kafin ya juya ya kalleta yana ɗan murmushi ya ce
"Ina baƙin?"
"Suna ciki shirin tafiya ma sukeyi, gaka nan gaka nan tun ɗazu sai kace wanda ya taho daga Kaduna ai da sun tafi ka huta kuma ga wani saƙon can an kawo maka sammaci daga kotu" ta sake faɗa hankali kwance ta wuce shi ta shige ɗakin Solar. Nepa aka ɗauke shine ta fito zata canza ta ganshi dan basu ji motsin buɗe get ɗin ba ma.
Dafe kansa daya sake sarawa yayi yana nanata sammaci a zuciyarsa, Sai da ya ga zata fito kafin ya lallaɓa ya nufi falon yana ƙaƙalo murmushi a ransa yana haɗa kalaman da zaiyi amfani dasu gurin yi musu magana, Hafiz da Jalilah suka ɗaga kai a tare suka kalle shi haɗi da amsa masa sallama. Ya saki murmushin yaƙe ya nufi Hafiz ya bashi hannu suka gaisa yana cewa
"Lallai kuwa an bani babban surprise, kuma da na san kaine da zance mata karta buɗe maka ƙofa"
Fuska ba yabo ba fallasa Hafiz ya ce
"Idan ni ba'a barni na shigo ba ai ba za'a hana uwarɗakinka shigowa ba ko ba haka ba Hajjaju?" Yayi maganar yana kallon inda Jalilah ke zaune ta harɗe ƙafafu tana latsa waya sai ka rantse bata san da wanzuwarsu a gurin ba.
Murmushin daya saka zuciyar Bilal fara gudun wuce ƙa'ida tayi kafin ta ce
"Ni da aka ɓoyewa amaryar ai ni naci albarkacinka". Ya haɗiye miyau kafin ya samu guri ya zauna yana kallonta ya ce
"Ranki ya daɗe yaushe a gari?"
"Zuwana kenan" ta bashi amsa tana gyara zama idonta akansa. Gyara zama yayi yana murmushin da gara kawai a bashi fili ya fashe da kuka, magan yake so yayi amma wai duk tarin kalaman kare kai daya ke da haddarsu a ka duk wacce ya kamo sai ta zille ya rasa kalaman da zai haɗa yayi magana sai kawai yayi shiru ya sadda kai ƙasa kamar wanda Alƙali ya tsura. Can ya miƙe ganin ba'a ajiye musu ko ledar pure water ba ya shiga kiran Zulaiha, tana ƙofar ɗakin Solar tana replying message ɗin da Ahlan ya turo mata.
Sunyi akan zasu haɗu yau tunda zataje gidan Hajja tana tsaka da shiri baƙin Bilal ɗin sukazo haushin rusa mata plan ya sa ko ruwa bata basu ba suna zaune sama da awa guda kenan suna jiransa. A bakin ƙofa suka haɗu zata shiga shi kuma zai fito yayi ƙasa da murya yana ce mata
"Babu wani abun taɓawa ne a gidan da ba ki basu ba naga ko ruwa ma baki ajiye musu ba?"
"Babu, ruwa kuma pure water muke dashi kuma naga su ɗin ba kalarsa bane shiyasa ban basu ba" ta bashi amsa, ya maka mata harara ya ce
"Ina dambun naman dana gani jiya? Kuma yau kwana nawa dana siyo ruwa katan biyu? Nufinki kin shanye ko me? Kuma ai akwai lemo a fridge kawai kice so kike ki wulaƙanta ni shiyasa kika wulaƙanta baƙi na" yayi tsaki ya koma ciki tabi bayansa. Kitchen suka shiga ya ɗauki try ya kwashi ruwan da tace babu dukda babu sanyi ya ɗora akai, da mamaki ya kalleta bayan daya buɗe fridge ɗin; lemuka kala kala a ciki harda Champagne. Gefe ta ɗauke kai, yayi ƙwafa ya kwashi lemukan ya haɗa da cake ɗin daya gani ya fita ya ajiye musu.
Hafiz da Jalilah suka bishi da kallo, dariya ce ta kama Hafiz ya danneta amma dukda haka saida wata ta fito sai ya fake da tari Bilal ya shiga yi masa sannu kafin ya koma ya kofuna ya ajiye musu ya bi Zulaiha data shige ɗaki da harara duk akan idon Hafiz, sai ya girgiza kai kawai ya ɗauki kofi ya tsiyaya lemo ya miƙawa Jalilah bata karɓa ba ta masa alamar aa da hannu tana cigaba da danna waya, ya karɓi kaɗan kafin ya kalli Bilal ya ce
"Su Al'amin fa?"
"Suna can gurin Mamansu" ya bashi amsa yana satar kallon Jalilah. Hafiz ya sake cewa
"Allah sarki, kwanaki na ganta kuwa a Alpen ina ta ɗaga mata hannu amma bata lura da ni ba, ta canza sosai ta ƙara kyau da farko ma nayi tantamar ita ɗin ce kuwa sai da naga ƙaninta sannan na yarda ita ɗin ce dagaske, gaskiya zawarci ya karɓeta idan ba'a faɗa bama zaka ɗauka budurwa ce wlh".
"Hmmm" kawai Bilal ya iya faɗa take kuma haushin Hafiz ɗin ya kamashi amma dai bai nuna ba yaci gaba da satar kallon Jalilah dake ta danna waya alamar wani abun take rubutawa. Kiran sallar la'asar da aka farayi yasa ta miƙe kamar wacce aka tsikara tana kallon Hafiz tace
"Muje ko?"
"Wai mai ya faru ne gaba ɗaya kin canza ba kamar yanda muka fito ba?" Hafiz ya tambayeta. Ta kalli Bilal kafin ta mayar da kallonta kan Hafiz tayi murmushi tace
"Na gaya maka maganar kayan da aka satar mana a store shine duk ya canza mun mood" ta faɗa tana langwaɓar da gefe kai. Mota ya rakasu basu ja sallamar da nisa ba suka wuce shi kuma ya jingina da ƙofa yana mayar da numfashi. Ta faru ta ƙare anyi wa mai dami ɗaya sata, shi dama ya daɗe yana hasashen shigo shigo ba zurfi kawai Hafiz yake yi masa da yakeyi kamar bashida masaniyar komai akan alaƙarsu, idan ma kuna dagaske ne bai sani ba toh yau kam ya san Jalilah ta gama farke masa laya shiyasa suka haɗo kai suka zo su ƙureshi amma ba zaiyi saurin kaiwa ƙasa ba dole ya nemi mafita domin shirun da Jalilah tayi ya sani tabbas ba alkhairi bane.
Ciki ya koma yana zura kai sukayi karo da Zulaiha dake shirin fitowa, tayi baya ta dafe kai kafin tayi tsaki ta raɓeshi har tana tureshi ta fice ya bi bayanta da kallo. Ɗakinsa ya shiga ya ringa safa da marwa tunani kamar kansa zaiyi bindiga ya tarwatse, yanzu ina zai kama? Jalilah tasan yayi aure da alama kuma tana da masaniya akan shi ya ɗauki kayan idan ma kuma bata sani ba toh tabbatas tana dabda sani bai kuma san irin matakin da zata ɗauka akan hakan ba, ga Alhaji Lawan ya makashi a kotu shi yanzu ina zai tsoma ransa yaji daɗi a faɗin ƙasar nan?
Tsabar ruɗin da yake ciki bai tuna baiyi sallar la'asar ba sai da yaji ana kiran sallar magriba tukunna yayi alwala ya haɗa su yayi. Yana nan zaune gida shi kaɗai har ƙarfe goma Hajja harta gaji da kiransa tun magriba wai suzo suyiwa Fadila faɗa kafin a tafi rakata ko faɗan mai zaiyi mata oho?
Ganin har ƙarfe goman Zulaiha bata dawo ba ya sa ya kirata tace masa suna gidan Amarya ba'a tafi kaita da wuri bane amma yanzu zasu taho. Haka nan zuciyarsa ta raya masa wani abu take kuma yayi na'am da hakan nan da nan ya shiga haɗa abinda zai buƙata a yar jaka, yana haɗa kayan yaji tsayuwar mota a ƙofar gidan, yanda kasan mara gaskiya ya fita da sauri ya leƙa.
A ƙofar gidan motar ta tsaya, ganin an buɗe ƙofa kuma ya saka mai motar yayi gaba, tsaki ya koma ciki amma bai rufe ƙofa ba yana kallon motar dake kunne har sannan. Kusan minti uku yana tsaye kafin ya koma ciki ya ɗauko jakar ya saka a mota ya buɗe Get ya fice.
A daren ya kama hanyar Minjibir, sai da ya nemi abinci yaci dan yunwa yake ji sosai kafin ya karɓi key ɗin ɗaki ya shiga. Wayarsa ya fara kashewa ya saka a cikin drawer bayan ya turawa da Zulaiha saƙo akan tafiyar gaggawa ta sameshi ta tafi gida idan ya dawo zaizo ya ɗauketa sannan yayi wanka ya kwanta bacci.
JALILAH
Tun daga sanda ta tabbatar da yayi blocking ɗin ta ta gasgata abinda zuciyarta ta daɗe tana raya mata akan Bilal yana so yayi amfani da ita ne kawai ya cimma burinsa sannan ya watsar da ita kamar yanda ya yiwa matarsa Halima. Harga Allah da aure take son Bilal dukda banbancin matsayi da yake tsakaninsu amma da yake shi So babu ruwansa da wannan tunda ta ganshi taji yayi mata, tayi masa uzuri a lokacin daya nuna mata cewar ba zai iya aurenta ba wannan dalilin ya saka ta buɗe masa bakin aljihunta a ganinta rashin wadatace ta saka yace ba zai aureta ɗin a lokacin ba amma a maimakon aure sai ya bijiro mata da abinda take ƙoƙarin bari harta yanke hukuncin auren nasa.