Sashe 114
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya zare wayar daga kunnensa ya duba screen ɗin ga sunanta nan ya fito yanzu DUNIYATA kafin ya sake mayar da ita kunne mamaki na neman kashe shi da jin abinda ta faɗa, ita kuwa ko a jikinta ta balbale shi da masifa akan me y kashe waya gashi nan ya janyo Kawunta ya kira yana ta musu tijara su da Ummansu akan rashin zuwan da bai yi ba.
"Ya ce kazo ka same shi a nan gidan bayan sallar magriba idan kaga dama karka zo na rantse da girman Allah sai ka gane baka da wayo sai na nuna maka kai ƙaramin yen yen ne" ta ƙarƙare maganar kafin ta ja dogon tsaki ta kashe wayar.
Bilal dai kasa cire tasa wayar yayi daga kunne yayi sakato kamar wani wawa tsabar mamaki. Nasir daya gama jin komai, duk yanda ya so ya hana kansa yin dariyar data taso masa dole ya saketa jin tana nema ta shaƙe masa maƙogaro, Bilal ya kalle shi da idon sa da suka kaɗa sukayi jajir sai kawai ya ɓalle murfin motar ya fita waje ya ringa sheƙa dariya kamar wani taɓaɓɓe.
Bilal ya sauke ajiyar zuciya bayan daya ajiye wayar maganganun Zulaihan na masa amsa kuwwa a kunne, a fili ya ce
"Ba ita bace, aljanunta ne suka motsa"
"Aljanu ko?" Nasir daya buɗe kofar motar ya faɗa yana sake sheƙewa da dariyar data fi ta farko. Sai da yayi da gaske kafin ya iya riƙe kansa ganin Bilal ɗin ya cika yayi fam kamar zai fashe. Suna tafi Nasir na cewa
"Amarya, Amarya bata laifi ko ta kashe ɗan masu gida" shi dai Bilal tafi ka mutu bai ce masa ba har ya sauke shi a ƙofar gidansa.
"Dan Allah ka shirya da wuri" Bilal ya faɗa bayan Nasir ɗin ya sauka, Nasir ya danne dariyarsa kafin ya ce
"Baka da matsala mutumina sai ka zo" ya wuce ciki yana sake tuntsurewa da dariya.
"Daɗi na da gobe saurin zuwa" ya faɗa a fili yana shiga gida.
Bilal kuwa gida ya wuce, sai da ya shiga gidan ya tuna ashe ko breakfast bai yi ba yau ɗin. Sai lokacin ya haɗa tea ya sha da ya ringa jin sa kamar maɗaci, yanzu Allah kaɗai ya san mutum nawa suka san halin da yake ciki. Ƙila har yan unguwar ma sun sani yanzu da ya shigo sai ya ga kamar masu gadin layin daya wuce sunyi gulmar sa gaba ɗaya ya tsargu ji yake kamar duk in da ya wuce kawai kallonsa akeyi amma labari ya gama baza ko ina ga halin sa.
Zuciyarsa ta raya masa komai zai wuce da zarar Halima ta dawo kuma Zulaiha ta tare, musamman tunda dama maganar daga ɓangaren Haliman ta fita idan aka ga ta dawo gidansa hakan zai aka kokonto a zukatan mutane domin da wahala ace bayan wannan abun ya faru kuma ta sake komawa gidansa amma idan akayi haka kuma gashi yayi aure za'a iya cewa ma saboda ƙarin auren ya saka tayi masa yarfe yanda mata suka saba yiwa mazajensu idan zasuyi aure.
Wannan tunanin da yayi ya sanyaya masa zuciya har ya ɗan samu nutsuwa ya shiga kiran Agent ɗin daya bawa tallar shagunan Jalilah. Duk ma abinda zai faru a ƙalla ya tsira da abinda zai riƙe kansa surutun mutane mai wucewa ne da sunyi sun gaji zasuyi shiru. Agent ɗin ya sanar masa an samu mai siyan gurin kuma da daraja sosai dan haka gobe yaje a ƙarƙare magana dan dagaske suke kuma da kuɗin su a hannu.
Wannan labarin ya sake faranta masa rai, yana kashe wayar ya kira Engineer dake aikin gyaran sabon gidan da ya siya wanda Zulaiha zata zauna a ciki. Sabon gini ne bene na zamani wanda har plaster anyi matsuwa ta saka mai shi siyarwa kuma ya same shi kwasha kwasha, ɗan gyara kaɗan akayi na abinda baiyi masa ba, jiya da ya je an gama komai ƙwayayen wuya ake ƙarasa sakawa dan har yaran da zasu share gidan su wanke ya tarar an samo yana kiran Engineer kuwa ya gaya masa ai an gama komai yanzu ya bar gidan muƙullin yana hannun maigadin gidan da yake jikin nasan dama shi ake barwa ya ma tura masa video ta WhatsApp tun ɗazu.
Godiya ya masa, a ransa ya ayyana da gidan zaiyi bikon Halima. In dai ta yarda kawai ita ta koma can idan ya so a canzawa Zulaihan penti ta shiga nan ita tunda babu abinda gidan yayi a matsayinta kuma ko wanda bai kaishi ta samu ba ai sai dai ta godewa Allah ita kuwa Halima dama gidan bene shi ya dace da ita tunda daga cikinsa ta fito.
Ƙarfe shida ya fesa wanka ya tafi gidan Nasir daga can zasu wuce gidansu Zulaiha dukda idan ya tuna abinda ta faɗa masa ɗazun sai ya ji kamar kar ya je sai kuma zuciyarsa ta tuna masa ba laifinta bane iskokin da Ummansu ta faɗa ne suke taɓa ta sa wannan ya taushi zuciyarsa ya isa gidan Nasir ɗin.
"Kaga na Halima angon Zulaiha ga kuma Jalilah a gefe" Nasir ya tsokane shi bayan ya fito, ya haɗe rai tam ya ce
"Bana so"
Nasir ya ɗaga hannu biyu sama ya ce
"Na bari Allah ya baka haƙuri". Suna tafe suna yar hira har suka isa unguwar, sai da suka tsaya sukayi sallar magriba a masallacin layin su Anty Jalilah kafin suka fara wucewa gidansu Zulaiha dan yana sallah ta turo masa text wai ga Kawun fa ya iso.
A tsakar gida suka zaune, Zulaihan da Ummansu sai Nuratu sun sha hijabai kamar masu takaba kowacce ta raɓe a gefe tana zare ido sai Kawun nasu dake zaune kan farar kujerar roba yana girgiza ƙafa. Tare suka isa da Mijin Nuratu wanda shima suka zo tareda wani abokinsa, suka gaisa gaba ɗaya kafin akayi musu iso suka zauna kan tabarmar da aka tanadar musu.
Cewa Kawun yayi Nasir da abokin Faruk Mijin Nuratu su ɗan basu guri.
"Ai komai yana son sirri, dukda ku aminanku ne amma ai akwai abinda ba zaku so suji akan matanku ba ko?" Kawun ya faɗa, Ummansu Zulaiha tayi saurin cewa
"Ai babu wani abu ma"
"Ni dai ban sako bakinki ba idan kuma ba zaki iya yin shiru ba kema ki tashi ki bamu guri" Kawun ya taso mata. Hannunta Zulaiha ta kama cikin alamar tayi shiru, Kawun ya ja tsaki ya ce
"Na san dai dukkaninku ba yara bane tunda kuma kuka yarda har kuka ɗaura aure da yaran nan toh kunji kun gani kuna son su a yanda suke ne musamman kai" ya nuna Bilal. Kallonsa Bilal ɗin yayi yana jira yaji ƙarin bayani Kawu ya cigaba da cewa
"Tone tone dai babu kyau tunda abinda ya faru ya rigada ya wuce amma dukda haka dole in ja musu kunne shiyasa na taraku gaba ɗaya, babu kawo ƙara dan iya shari'ar da nayi a baya masa Allah ya bani lada na gaji. Duk wacce ta muku ba dai dai ba kuci ubanta dai dai gwargwado amma banda dawowa gida iya gatan da zaku musu kenan dan wlh duk wacce ta kuskura aurenta ya mutu ta sani ba sake auruwa zatayi ba dan suma ɗin ba ƙaramin jahadi sukayi ba da suka.... "
"Haba Shafi'u wannan wane irin abu ne?" Ummansu ta sake katse shi. Zulaiha ta ruƙo ta ganin tana shirin miƙewa Nuratu dai na gefe kanta a ƙasa Kawun ya ce
"Mariya, ko dai rufa rufa kuka yiwa yaran nan shiyasa kike ta katseni kar in faɗi gaskiya?"
"Rufa rufar me? Ai duk cikinsu babu wanda bai san tsanar da ka mana ba da irin sharrin da kake bibiyarmu da shi kullum. Kai nake so na rufawa asiri karka zubar da mutunchin ka a gabansu amma ka saki baki bayan duk wanda yake sauraronka yasan tsantsar hassada da baƙin cikin Allah yayiwa yara gata ya basu mazaje irin wanda yayanka basu samu ba shiyasa kake so ka ɓata su toh ta Allah ba taka ba" Umman ta faɗa cikin masifa.
Kawun ma baiyi shiru ba ya ce
"Sai dai ki naɗe tabarmar haukarki da kunya amma ni ɗan gaskiya da gaskiya ne kin sani kuma dole in tabbatar ba'ayi kitso da kwarkwata ba".
Bilal dai kallonsu kawai yake, shi dai Umman da ya sani sama da shekara goma idan aka saka mata hannu ba zata ciza ba amma yau ita ce take tada jijiyar wuya haka tana masifa ana riƙeta kamar zata daki Kawun?
Faruk ne ya ce
"Dan Allah kuyi haƙuri, ni dai a ɓangarena babu wata matsala dan babu abinda Nuratu ta ɓoye mun kuma iyayena basu nema mun aurenta ba sai da sukayi bincike kuma da yardarsu da komai na aureta dan haka ni dai a gurina babu wata matsala In sha Allahu".
Bilal ya kalle shi, kansa ya fara kullewa. Wai toh meye ake cewa an sani da shi bai sani ba?
Zungurinsa Faruk ɗin yayi yayi diriri kafin ya ce
"Nima haka".
"Toh madallah Allah ya taya ku ruƙo sai aje ayita haƙuri. Ranar Asabar in Allah ya kaimu aka ce tariya ko? Dama babu wani taro da za'ayi, mutum biyu sun isa daga kowanne ɓangare suzo su ɗauki amaren" Kawun ya sake faɗa.
Umma ta zauna tana sauke numfashi kamar wacce tayi gudun tsira, daga nan Kawu ya miƙe ya musu sallama Faruk ma ya fita bayan ya ce Nuratu ta biyo shi aka bar Bilal da Umma sai Zulaiha data sunkuyar da kai kamar wacce take gaban Alƙali. Yafi minti goma ya gagara ce musu komai suma haka sai da Nasir ya kira shi a waya kafin ya miƙe yana musu sallama ko motsi Zulaihan batayi ba Umman ma kamar a tsorace ta masa Allah ya tsare ya fita, a soro ya tarar da su Nuratu tana rungume jikin Faruk tana kuka ya giftasu yaa jin sa yana cewa
"Ya ce kazo ka same shi a nan gidan bayan sallar magriba idan kaga dama karka zo na rantse da girman Allah sai ka gane baka da wayo sai na nuna maka kai ƙaramin yen yen ne" ta ƙarƙare maganar kafin ta ja dogon tsaki ta kashe wayar.
Bilal dai kasa cire tasa wayar yayi daga kunne yayi sakato kamar wani wawa tsabar mamaki. Nasir daya gama jin komai, duk yanda ya so ya hana kansa yin dariyar data taso masa dole ya saketa jin tana nema ta shaƙe masa maƙogaro, Bilal ya kalle shi da idon sa da suka kaɗa sukayi jajir sai kawai ya ɓalle murfin motar ya fita waje ya ringa sheƙa dariya kamar wani taɓaɓɓe.
Bilal ya sauke ajiyar zuciya bayan daya ajiye wayar maganganun Zulaihan na masa amsa kuwwa a kunne, a fili ya ce
"Ba ita bace, aljanunta ne suka motsa"
"Aljanu ko?" Nasir daya buɗe kofar motar ya faɗa yana sake sheƙewa da dariyar data fi ta farko. Sai da yayi da gaske kafin ya iya riƙe kansa ganin Bilal ɗin ya cika yayi fam kamar zai fashe. Suna tafi Nasir na cewa
"Amarya, Amarya bata laifi ko ta kashe ɗan masu gida" shi dai Bilal tafi ka mutu bai ce masa ba har ya sauke shi a ƙofar gidansa.
"Dan Allah ka shirya da wuri" Bilal ya faɗa bayan Nasir ɗin ya sauka, Nasir ya danne dariyarsa kafin ya ce
"Baka da matsala mutumina sai ka zo" ya wuce ciki yana sake tuntsurewa da dariya.
"Daɗi na da gobe saurin zuwa" ya faɗa a fili yana shiga gida.
Bilal kuwa gida ya wuce, sai da ya shiga gidan ya tuna ashe ko breakfast bai yi ba yau ɗin. Sai lokacin ya haɗa tea ya sha da ya ringa jin sa kamar maɗaci, yanzu Allah kaɗai ya san mutum nawa suka san halin da yake ciki. Ƙila har yan unguwar ma sun sani yanzu da ya shigo sai ya ga kamar masu gadin layin daya wuce sunyi gulmar sa gaba ɗaya ya tsargu ji yake kamar duk in da ya wuce kawai kallonsa akeyi amma labari ya gama baza ko ina ga halin sa.
Zuciyarsa ta raya masa komai zai wuce da zarar Halima ta dawo kuma Zulaiha ta tare, musamman tunda dama maganar daga ɓangaren Haliman ta fita idan aka ga ta dawo gidansa hakan zai aka kokonto a zukatan mutane domin da wahala ace bayan wannan abun ya faru kuma ta sake komawa gidansa amma idan akayi haka kuma gashi yayi aure za'a iya cewa ma saboda ƙarin auren ya saka tayi masa yarfe yanda mata suka saba yiwa mazajensu idan zasuyi aure.
Wannan tunanin da yayi ya sanyaya masa zuciya har ya ɗan samu nutsuwa ya shiga kiran Agent ɗin daya bawa tallar shagunan Jalilah. Duk ma abinda zai faru a ƙalla ya tsira da abinda zai riƙe kansa surutun mutane mai wucewa ne da sunyi sun gaji zasuyi shiru. Agent ɗin ya sanar masa an samu mai siyan gurin kuma da daraja sosai dan haka gobe yaje a ƙarƙare magana dan dagaske suke kuma da kuɗin su a hannu.
Wannan labarin ya sake faranta masa rai, yana kashe wayar ya kira Engineer dake aikin gyaran sabon gidan da ya siya wanda Zulaiha zata zauna a ciki. Sabon gini ne bene na zamani wanda har plaster anyi matsuwa ta saka mai shi siyarwa kuma ya same shi kwasha kwasha, ɗan gyara kaɗan akayi na abinda baiyi masa ba, jiya da ya je an gama komai ƙwayayen wuya ake ƙarasa sakawa dan har yaran da zasu share gidan su wanke ya tarar an samo yana kiran Engineer kuwa ya gaya masa ai an gama komai yanzu ya bar gidan muƙullin yana hannun maigadin gidan da yake jikin nasan dama shi ake barwa ya ma tura masa video ta WhatsApp tun ɗazu.
Godiya ya masa, a ransa ya ayyana da gidan zaiyi bikon Halima. In dai ta yarda kawai ita ta koma can idan ya so a canzawa Zulaihan penti ta shiga nan ita tunda babu abinda gidan yayi a matsayinta kuma ko wanda bai kaishi ta samu ba ai sai dai ta godewa Allah ita kuwa Halima dama gidan bene shi ya dace da ita tunda daga cikinsa ta fito.
Ƙarfe shida ya fesa wanka ya tafi gidan Nasir daga can zasu wuce gidansu Zulaiha dukda idan ya tuna abinda ta faɗa masa ɗazun sai ya ji kamar kar ya je sai kuma zuciyarsa ta tuna masa ba laifinta bane iskokin da Ummansu ta faɗa ne suke taɓa ta sa wannan ya taushi zuciyarsa ya isa gidan Nasir ɗin.
"Kaga na Halima angon Zulaiha ga kuma Jalilah a gefe" Nasir ya tsokane shi bayan ya fito, ya haɗe rai tam ya ce
"Bana so"
Nasir ya ɗaga hannu biyu sama ya ce
"Na bari Allah ya baka haƙuri". Suna tafe suna yar hira har suka isa unguwar, sai da suka tsaya sukayi sallar magriba a masallacin layin su Anty Jalilah kafin suka fara wucewa gidansu Zulaiha dan yana sallah ta turo masa text wai ga Kawun fa ya iso.
A tsakar gida suka zaune, Zulaihan da Ummansu sai Nuratu sun sha hijabai kamar masu takaba kowacce ta raɓe a gefe tana zare ido sai Kawun nasu dake zaune kan farar kujerar roba yana girgiza ƙafa. Tare suka isa da Mijin Nuratu wanda shima suka zo tareda wani abokinsa, suka gaisa gaba ɗaya kafin akayi musu iso suka zauna kan tabarmar da aka tanadar musu.
Cewa Kawun yayi Nasir da abokin Faruk Mijin Nuratu su ɗan basu guri.
"Ai komai yana son sirri, dukda ku aminanku ne amma ai akwai abinda ba zaku so suji akan matanku ba ko?" Kawun ya faɗa, Ummansu Zulaiha tayi saurin cewa
"Ai babu wani abu ma"
"Ni dai ban sako bakinki ba idan kuma ba zaki iya yin shiru ba kema ki tashi ki bamu guri" Kawun ya taso mata. Hannunta Zulaiha ta kama cikin alamar tayi shiru, Kawun ya ja tsaki ya ce
"Na san dai dukkaninku ba yara bane tunda kuma kuka yarda har kuka ɗaura aure da yaran nan toh kunji kun gani kuna son su a yanda suke ne musamman kai" ya nuna Bilal. Kallonsa Bilal ɗin yayi yana jira yaji ƙarin bayani Kawu ya cigaba da cewa
"Tone tone dai babu kyau tunda abinda ya faru ya rigada ya wuce amma dukda haka dole in ja musu kunne shiyasa na taraku gaba ɗaya, babu kawo ƙara dan iya shari'ar da nayi a baya masa Allah ya bani lada na gaji. Duk wacce ta muku ba dai dai ba kuci ubanta dai dai gwargwado amma banda dawowa gida iya gatan da zaku musu kenan dan wlh duk wacce ta kuskura aurenta ya mutu ta sani ba sake auruwa zatayi ba dan suma ɗin ba ƙaramin jahadi sukayi ba da suka.... "
"Haba Shafi'u wannan wane irin abu ne?" Ummansu ta sake katse shi. Zulaiha ta ruƙo ta ganin tana shirin miƙewa Nuratu dai na gefe kanta a ƙasa Kawun ya ce
"Mariya, ko dai rufa rufa kuka yiwa yaran nan shiyasa kike ta katseni kar in faɗi gaskiya?"
"Rufa rufar me? Ai duk cikinsu babu wanda bai san tsanar da ka mana ba da irin sharrin da kake bibiyarmu da shi kullum. Kai nake so na rufawa asiri karka zubar da mutunchin ka a gabansu amma ka saki baki bayan duk wanda yake sauraronka yasan tsantsar hassada da baƙin cikin Allah yayiwa yara gata ya basu mazaje irin wanda yayanka basu samu ba shiyasa kake so ka ɓata su toh ta Allah ba taka ba" Umman ta faɗa cikin masifa.
Kawun ma baiyi shiru ba ya ce
"Sai dai ki naɗe tabarmar haukarki da kunya amma ni ɗan gaskiya da gaskiya ne kin sani kuma dole in tabbatar ba'ayi kitso da kwarkwata ba".
Bilal dai kallonsu kawai yake, shi dai Umman da ya sani sama da shekara goma idan aka saka mata hannu ba zata ciza ba amma yau ita ce take tada jijiyar wuya haka tana masifa ana riƙeta kamar zata daki Kawun?
Faruk ne ya ce
"Dan Allah kuyi haƙuri, ni dai a ɓangarena babu wata matsala dan babu abinda Nuratu ta ɓoye mun kuma iyayena basu nema mun aurenta ba sai da sukayi bincike kuma da yardarsu da komai na aureta dan haka ni dai a gurina babu wata matsala In sha Allahu".
Bilal ya kalle shi, kansa ya fara kullewa. Wai toh meye ake cewa an sani da shi bai sani ba?
Zungurinsa Faruk ɗin yayi yayi diriri kafin ya ce
"Nima haka".
"Toh madallah Allah ya taya ku ruƙo sai aje ayita haƙuri. Ranar Asabar in Allah ya kaimu aka ce tariya ko? Dama babu wani taro da za'ayi, mutum biyu sun isa daga kowanne ɓangare suzo su ɗauki amaren" Kawun ya sake faɗa.
Umma ta zauna tana sauke numfashi kamar wacce tayi gudun tsira, daga nan Kawu ya miƙe ya musu sallama Faruk ma ya fita bayan ya ce Nuratu ta biyo shi aka bar Bilal da Umma sai Zulaiha data sunkuyar da kai kamar wacce take gaban Alƙali. Yafi minti goma ya gagara ce musu komai suma haka sai da Nasir ya kira shi a waya kafin ya miƙe yana musu sallama ko motsi Zulaihan batayi ba Umman ma kamar a tsorace ta masa Allah ya tsare ya fita, a soro ya tarar da su Nuratu tana rungume jikin Faruk tana kuka ya giftasu yaa jin sa yana cewa