Sashe 47
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da haka ya bawa kansa ƙwarin guiwa, da yayi niyyar zama gurin yayi gadi ko da zata ce zata fita se kuma ya fasa yayi tafiyar sa dan yasan babu in da zata je ita dai Amirah yasan dole zata bar gidan tunda Halima na gudun ɓacin ransa. A masallacin unguwar yayi sallar la'asar yana zaune ya hango gilmawar su, har ya miƙe da niyyar bin su kuma se ya fasa a ransa ya raya mafita ce ta samu. Yanzu duk inda aka je aka dawo ze juya lefin ne ya koma kanta ta fita daga gidan sa ba tare da ya bata izini ba tunda ai ba ita yace ta tafi ba. Komawa yayi ya ɗauki mashin ɗin sa cikin sa'a har ya fito bakin titi se lokacin suka samu abun hawa. Se da ya rakasu har gida yaga sun shiga kafin ya wuce gidan su yana ayyana yanda ze canza maganar idan ma ta tashi ance y zagi uban matar sa dukda yayi amanna Halima ba zata taɓa bari maganar ta fita ba yasan ma baze rasa dalilin da ya saka tabi Amiran ba kenan dan kar taje ta faɗi abin da ba shikenan ba.
Daya isa gidan suna gaisawa da Hajja abinda ta fara tambayar sa shine
"Wai yaushe matar ka zata tafi wanka ne ko kuwa kana nufin a gidan ka zata haihu su tatse maka tattalin arziƙi?"
Zancen kenan kullum yaje kamar karatu tun cikin Halima be wuce wata shida ba take surutun se ta tafi goyon ciki ai haka akeyi a al'ada, se kace ita nata yayan da cikin wata shidan suke tahowa kuma ma banda Amina Babbar Yayar su shi be sake ganin wata tazo wani wankan gida ba se Fadila itama kuma yasan dan Mijin yaƙi daɗin azanci ne dama neman tahowa gidan takeyi shi yasa suka fake da haihuwa badan haka ba da Hajjan ce zata je ta zauna mata kamar yanda ta saba yiwa sauran shine zata takura se Halima ta tafi tun da wurwuri.
Dukda dai shima yana da ra'ayin ta tafi wankan gida saboda ko babu komai za'a rage masa hidimomi da yawa na yan barka har zuwa suna da abubuwan da zasu biyo baya; duk baya jin yan uwan Halima dan tun auren su ze iya irga mutum nawa suka zo gidan kuma ko ta haihu ba zasuyi irin zuwan nan na takura ba nasa dangin yake ji dan yana ganin yanda sukeyi a sauran gidajen yan uwansa idan anyi haihuwa wata tun farar safiya zata taho se taci abincin dare sannan ta tafi gaskiya baze ɗauki wannan zaryar ba shiyasa gara ta tafi can gidan su idan tayi arba'in suka gama yawon zaga dangi se ta dawo dukda ma ya gama gane take taken Haliman bata so ta tafi gidan amma hakan ya zame mata dole tunda yana ra'ayi.
Yana ɗakin Hajja suna hira kiran Anty Labiba ya shiga wayar sa, abinda ya fara zuwar masa shine Amirah taje ta ce ya zagi Abban su shine Anty Labiba ta biyo ba'asi hakan yasa ya maida wayar sa aljihu bayan ya sakata a silent a ransa yana raya harka ta lalace musamman tunda wannan matar ta shigo ciki ko abun beyi zafi ba se ta ƙara rura wuta. Se da aka kira sallah ya fita, bayan an idar Abdurrashid ya tsayar dashi ɗaya daga cikin Yayan Baba Salahu ne kuma abokin Bilal ɗin dan suna buga ƙwallo tare. Da fara'a ya tare shi bayan sunyi musabaha yace
"Angon ƙarni ashe an samu ƙaruwa?"
Tunanin da Bilal ya tafi yana magana ne akan Halima nada ciki, se ya gimtse fuska kishi ya motsa wato kalle masa mata ma yake yi yana sa mata ido tsabar kuma bashi da ta ido har ya iya tarar sa ya masa barka wai matar sa nada ciki. Shi ko Abdurrashid bema gane sauyin fuskar Bilal ɗin ba yace
"Allah ya raya ya ɗayyaba, se munzo barka" daga haka ya saki hannun Bilal ɗin ya wuce abun sa. Sakato Bilal yayi a tsaye yana ƙoƙarin haɗa maganganun Abdurrashid ɗin na ƙarshe, idan ya fahimta barkar haihuwa ya masa ba ta samun ciki ba kenan kuma hakan yana nufin Halima ta haihu ne ko me?
Ƙarasa fita yayi daga harabar masallacin kafin ya sake samun guri ya tsaya ya riƙe ƙugu yana ƙoƙarin haɗa lissafin, Nasir ne ya iske shi fuska a washe ya shiga zolayar sa da "Angon ƙarni".
"Ta tabbata kenan" ya raya a ransa, Nasir ɗin yace
"Be kamata ma na kulaka ka ba, ace se dai muji haihuwa a gari ba zaka iya kirana ka gaya mun ba ko da yake yanzu kayi sababbin abokai yan GRA naga ai baka yayin irin mu yan ghetto".
"Ka aje maganar wasa Nasir dagaske ne wai Halima ta haihu?" Ya tambaye shi. Se Nasir ya kalle shi yace
"Bana son rainin wayau; matar ka ta haihu ka ringa tambaya ta wasa ne ko gaske? Mutuwa kayi ka dawo da zaka ce baka san meya faru a duniyar ba ko wani salon wulaƙancin ne haka?"
"Dagaske nakeyi Nasir ban san Halima ta haihu ba. Tsayuwar da kaga nayi a nan yanzu Yayanta Abdurrashid ya gama mun barka shine na tsaya ina jiran wanda ze zo ya faɗa mun gaskiya ko aka sin zancen kuma se gaka, amma lallai mutanen nan sun raina ni. Ace matar tawa ta fara naƙuda har ta haihu babu wanda ya kira ni ya gaya mun? Kenan da mutuwa tayi se dai kawai ace nazo na ga gawarta ko me?" Ya faɗa cikin ɓacin rai. Nasir ya dafa shi yace
"Kar dai kayi saurin yanke hukunci; nima yanzu Fauziyya ta kira ni take gaya mun taga Zubaida ta saka, ƙila yanzu ta haihu kuma kasan sharrin network ta yuwu ma sun kira ka be shigo ba. Tun da dai ta haihu lafiya ai anyi me wahalar yanzu se ka kirata muji suna wane asibitin ne se muje".
"Zance ma kakeyi wlh, ai har idan an ɗauke ni da muhimmanci tun kafin a fita da ita daga gida ya kamata a kira a nemi izini na kuma a gaya mun. Idan basu same ni a waya ba bani da dangi ne? Taku nawa ne tsakanin mu dasu da ba zasu aiko a gayawa mahaifiya ta ko wani ɗan uwana yaje a tafi dashi asibitin ba?. Ashe dai da ake faɗar irin wulaƙancin da masu kuɗi suke yi su mayar da mazajen yayan su ba komai ba dagaske ne tunda gashi ya biyo ta kaina se dai ni ba shashasha bane da zan ɗauka wlh se na nuna musu nasan mutunchin kaina" ya ƙarasa a fusace yana zaro wayar sa daga aljihunsa.
Lokaci ɗaya karsashin rashin mutunchin daya hau ya sake shi daya shiga jerin missed calls ɗin daya gani akan wayar sa. Kafin kiran Anty Labiba da kusan minti talatin Abban su Halima ya kira shi har sau biyu, alamar saƙon daya gani a saman wayar ya duba Abban ne dai ya aje masa saƙo yana sanar dashi Halima tana cikin halin naƙuda ya rubuta masa sunan Asibitin da suke da har da kwatancen inda ɗakin haihuwar yake. Kamar an watsawa kaza ruwa haka yayi laƙwas, Nasir yace
"Ka gani sun kira ka ko?"
Kamar mara gaskiya ya mayar da wayar aljihunsa yana gyara zaman rigar sa yace
"Oho dai koma menene ba'a mutunta ni an bani ƙima ta ta mijin ta ba tun farko ma ai ni ya kamata ta kira ta gayawa naƙuda ta kamata ba wai yan gidan su ba ai" ya faɗa tamkar bashi da masaniya akan ta fita daga gidan. Nasir dake kallon sa kawai ya girgiza kai yace
"Kaji dashi, yanzu dai idan zamu je asibitin bismillah; idan kuma ba zaka je ɗin ba ni in kama gabana ina da abinda zanyi a chemist".
"Babu in da zanje, idan ina da muhimmanci zasu zo har in da nake su buƙace ni" Bilal ya faɗa yana wani buɗa hannu, hannu biyu Nasir ya ɗaga yana cewa
"Allah ya taimaka ya bada sa'a; idan ta dawo gida se ka sanar dani idan ma kuma can gidan su ta wuce duk dai ka gaya mun, ko da yake karka damu zan ji a inda na samu labarin haihuwar kawai ba se ka kira ni ba" daga haka ya juya yayi tafiyar sa Bilal ɗin na tsayar dashi be kula shi ba ya shige motar sa daya ajiye gefeb masallacin ya tafi.
Gida Bilal ya juya, yana shiga ya tarar da Hajja na saka hijabi; da mamaki ya kalle ta yace
"Unguwa zaki je ne Hajja?"
"Yanzu Fainusa tayo waya tace mana Halima ta haihu shine zamu je mu gano su" ta bashi amsa. Se ya wani ɓata fuska yace
"Yanzu an kira ki ne an gaya miki haihuwar balle ki ɗauki ƙafa ki tafi? Ke da Fainusa waya fi zama a haƙƙu da su kira? To ki koma ɗaki kiyi zamanki ko ni da nake uban ɗan basu kira sun gaya mun ba nima a wai wai naji a gari dan haka babu in da zamu je, idan sunga muna da muhimmanci sun san inda zasu same mu ai zasu zo" ya faɗa yana shigewa ɗakin Hajjan.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 20*
Daya isa gidan suna gaisawa da Hajja abinda ta fara tambayar sa shine
"Wai yaushe matar ka zata tafi wanka ne ko kuwa kana nufin a gidan ka zata haihu su tatse maka tattalin arziƙi?"
Zancen kenan kullum yaje kamar karatu tun cikin Halima be wuce wata shida ba take surutun se ta tafi goyon ciki ai haka akeyi a al'ada, se kace ita nata yayan da cikin wata shidan suke tahowa kuma ma banda Amina Babbar Yayar su shi be sake ganin wata tazo wani wankan gida ba se Fadila itama kuma yasan dan Mijin yaƙi daɗin azanci ne dama neman tahowa gidan takeyi shi yasa suka fake da haihuwa badan haka ba da Hajjan ce zata je ta zauna mata kamar yanda ta saba yiwa sauran shine zata takura se Halima ta tafi tun da wurwuri.
Dukda dai shima yana da ra'ayin ta tafi wankan gida saboda ko babu komai za'a rage masa hidimomi da yawa na yan barka har zuwa suna da abubuwan da zasu biyo baya; duk baya jin yan uwan Halima dan tun auren su ze iya irga mutum nawa suka zo gidan kuma ko ta haihu ba zasuyi irin zuwan nan na takura ba nasa dangin yake ji dan yana ganin yanda sukeyi a sauran gidajen yan uwansa idan anyi haihuwa wata tun farar safiya zata taho se taci abincin dare sannan ta tafi gaskiya baze ɗauki wannan zaryar ba shiyasa gara ta tafi can gidan su idan tayi arba'in suka gama yawon zaga dangi se ta dawo dukda ma ya gama gane take taken Haliman bata so ta tafi gidan amma hakan ya zame mata dole tunda yana ra'ayi.
Yana ɗakin Hajja suna hira kiran Anty Labiba ya shiga wayar sa, abinda ya fara zuwar masa shine Amirah taje ta ce ya zagi Abban su shine Anty Labiba ta biyo ba'asi hakan yasa ya maida wayar sa aljihu bayan ya sakata a silent a ransa yana raya harka ta lalace musamman tunda wannan matar ta shigo ciki ko abun beyi zafi ba se ta ƙara rura wuta. Se da aka kira sallah ya fita, bayan an idar Abdurrashid ya tsayar dashi ɗaya daga cikin Yayan Baba Salahu ne kuma abokin Bilal ɗin dan suna buga ƙwallo tare. Da fara'a ya tare shi bayan sunyi musabaha yace
"Angon ƙarni ashe an samu ƙaruwa?"
Tunanin da Bilal ya tafi yana magana ne akan Halima nada ciki, se ya gimtse fuska kishi ya motsa wato kalle masa mata ma yake yi yana sa mata ido tsabar kuma bashi da ta ido har ya iya tarar sa ya masa barka wai matar sa nada ciki. Shi ko Abdurrashid bema gane sauyin fuskar Bilal ɗin ba yace
"Allah ya raya ya ɗayyaba, se munzo barka" daga haka ya saki hannun Bilal ɗin ya wuce abun sa. Sakato Bilal yayi a tsaye yana ƙoƙarin haɗa maganganun Abdurrashid ɗin na ƙarshe, idan ya fahimta barkar haihuwa ya masa ba ta samun ciki ba kenan kuma hakan yana nufin Halima ta haihu ne ko me?
Ƙarasa fita yayi daga harabar masallacin kafin ya sake samun guri ya tsaya ya riƙe ƙugu yana ƙoƙarin haɗa lissafin, Nasir ne ya iske shi fuska a washe ya shiga zolayar sa da "Angon ƙarni".
"Ta tabbata kenan" ya raya a ransa, Nasir ɗin yace
"Be kamata ma na kulaka ka ba, ace se dai muji haihuwa a gari ba zaka iya kirana ka gaya mun ba ko da yake yanzu kayi sababbin abokai yan GRA naga ai baka yayin irin mu yan ghetto".
"Ka aje maganar wasa Nasir dagaske ne wai Halima ta haihu?" Ya tambaye shi. Se Nasir ya kalle shi yace
"Bana son rainin wayau; matar ka ta haihu ka ringa tambaya ta wasa ne ko gaske? Mutuwa kayi ka dawo da zaka ce baka san meya faru a duniyar ba ko wani salon wulaƙancin ne haka?"
"Dagaske nakeyi Nasir ban san Halima ta haihu ba. Tsayuwar da kaga nayi a nan yanzu Yayanta Abdurrashid ya gama mun barka shine na tsaya ina jiran wanda ze zo ya faɗa mun gaskiya ko aka sin zancen kuma se gaka, amma lallai mutanen nan sun raina ni. Ace matar tawa ta fara naƙuda har ta haihu babu wanda ya kira ni ya gaya mun? Kenan da mutuwa tayi se dai kawai ace nazo na ga gawarta ko me?" Ya faɗa cikin ɓacin rai. Nasir ya dafa shi yace
"Kar dai kayi saurin yanke hukunci; nima yanzu Fauziyya ta kira ni take gaya mun taga Zubaida ta saka, ƙila yanzu ta haihu kuma kasan sharrin network ta yuwu ma sun kira ka be shigo ba. Tun da dai ta haihu lafiya ai anyi me wahalar yanzu se ka kirata muji suna wane asibitin ne se muje".
"Zance ma kakeyi wlh, ai har idan an ɗauke ni da muhimmanci tun kafin a fita da ita daga gida ya kamata a kira a nemi izini na kuma a gaya mun. Idan basu same ni a waya ba bani da dangi ne? Taku nawa ne tsakanin mu dasu da ba zasu aiko a gayawa mahaifiya ta ko wani ɗan uwana yaje a tafi dashi asibitin ba?. Ashe dai da ake faɗar irin wulaƙancin da masu kuɗi suke yi su mayar da mazajen yayan su ba komai ba dagaske ne tunda gashi ya biyo ta kaina se dai ni ba shashasha bane da zan ɗauka wlh se na nuna musu nasan mutunchin kaina" ya ƙarasa a fusace yana zaro wayar sa daga aljihunsa.
Lokaci ɗaya karsashin rashin mutunchin daya hau ya sake shi daya shiga jerin missed calls ɗin daya gani akan wayar sa. Kafin kiran Anty Labiba da kusan minti talatin Abban su Halima ya kira shi har sau biyu, alamar saƙon daya gani a saman wayar ya duba Abban ne dai ya aje masa saƙo yana sanar dashi Halima tana cikin halin naƙuda ya rubuta masa sunan Asibitin da suke da har da kwatancen inda ɗakin haihuwar yake. Kamar an watsawa kaza ruwa haka yayi laƙwas, Nasir yace
"Ka gani sun kira ka ko?"
Kamar mara gaskiya ya mayar da wayar aljihunsa yana gyara zaman rigar sa yace
"Oho dai koma menene ba'a mutunta ni an bani ƙima ta ta mijin ta ba tun farko ma ai ni ya kamata ta kira ta gayawa naƙuda ta kamata ba wai yan gidan su ba ai" ya faɗa tamkar bashi da masaniya akan ta fita daga gidan. Nasir dake kallon sa kawai ya girgiza kai yace
"Kaji dashi, yanzu dai idan zamu je asibitin bismillah; idan kuma ba zaka je ɗin ba ni in kama gabana ina da abinda zanyi a chemist".
"Babu in da zanje, idan ina da muhimmanci zasu zo har in da nake su buƙace ni" Bilal ya faɗa yana wani buɗa hannu, hannu biyu Nasir ya ɗaga yana cewa
"Allah ya taimaka ya bada sa'a; idan ta dawo gida se ka sanar dani idan ma kuma can gidan su ta wuce duk dai ka gaya mun, ko da yake karka damu zan ji a inda na samu labarin haihuwar kawai ba se ka kira ni ba" daga haka ya juya yayi tafiyar sa Bilal ɗin na tsayar dashi be kula shi ba ya shige motar sa daya ajiye gefeb masallacin ya tafi.
Gida Bilal ya juya, yana shiga ya tarar da Hajja na saka hijabi; da mamaki ya kalle ta yace
"Unguwa zaki je ne Hajja?"
"Yanzu Fainusa tayo waya tace mana Halima ta haihu shine zamu je mu gano su" ta bashi amsa. Se ya wani ɓata fuska yace
"Yanzu an kira ki ne an gaya miki haihuwar balle ki ɗauki ƙafa ki tafi? Ke da Fainusa waya fi zama a haƙƙu da su kira? To ki koma ɗaki kiyi zamanki ko ni da nake uban ɗan basu kira sun gaya mun ba nima a wai wai naji a gari dan haka babu in da zamu je, idan sunga muna da muhimmanci sun san inda zasu same mu ai zasu zo" ya faɗa yana shigewa ɗakin Hajjan.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 20*