Sashe 77
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Banji waya ta a tareda ni ba na tuna sanda na koma ɗakin a gefe na na ajiye ta ba cikin aljihu ba dan haka na koma da sauri ina waigen motar da ta tashi har sun fice daga harabar gurin ajiye motocin. Yanda kasan anyi ruwan sama an ɗauke haka sukayi shiru ina shiga ɗakin, ni ba ta su nakeyi dan ko sunyi maganar ba bana zaton zan fahimci abinda suke cewa. Na ɗauki waya ta na fita ina jiyo yanda Fadila da Hadiza suka sheƙe da dariya kamar wasu taɓaɓɓu harda tafawa. Ina kiran layin sa aka ce mun a kashe yake ba tareda na koma nayi musu sallama ba kawai na fice daga Asibitin na wuce gida.
I wanted to summarize it in one or 2 chapters but i was overruled
Nagode da masoya na haƙiƙa waɗanda ko sunyi fushi basu manta tunanin su, waɗanda suke yiwa Marubuci kallon Mutum ba wai Bawa da suka siya da kuɗi ba.
[4/1, 9:08 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 08142548705* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 32*
*Barkanmu da Sallah yan uwa* 🙏🏽
Sai da na fita kofar asibitin kafin na tsaya ina raba ido, ina zan nufa ne ma? Gida zan tafi ko kuwa gari zan shiga cigiyar inda Bilal ya tafi? Na kai hannu na share laimar da naji akan fuskata wadda ban tantance hawaye bane ko zufa kafin na shiga tare abin hawa, gidanmu na wuce, ban ko karɓi canji ba bayan na sauka na shige gidan a bakin ƙofa na zauna kamar wata zararriya na fasa kukan da ya saka Mama ta fito daga falo kamar zata hantsila da Sharifa a hannunta ta shiga tambayata mai ya faru?
"Mutuwa Hajjan tayi?" Ta faɗa tana kallona sai na girgiza kai ina turza ƙafa kamar ƙaramar yarinya na sake gyara zama ina cigaba da kukan. Sai ta buga mun tsawa tace
"Bana son iskanci Halima haka nan zakizo ki faɗar mun da gaba na tambaye ki menene kuma kinƙi faɗa to tashi ki fita tun ban rufeki da duka ba". Ganin ta ajiye Sharifa na san zata iya dukan nawa kamar yanda ta faɗa hakan yasa na miƙe na shige falon da sauri ina cigaba da kukan. Bata sake bi ta kaina ba, sai da nayi mai isata kafin na kama hanyar gida ba tareda nayiwa Mama sallama ko na ɗauki su Sharifa ba na tafi.
Ina ƙoƙarin buɗe gida naji muryar Maman Yusuf tana kirana, na waiga ganin ta nufoni yasa na tura ƙofar na shiga itama ta biyo bayana.
"Kin dawo kenan" ta faɗa tana kallona ba tareda mun haɗa ido ba dan bana son ta fara tuhumata mai ya sameni na bata amsa da "eh na dawo".
"Ai har zan shigo ɗazun sai kuma naga kina da baƙi sai kawai na wuce dama can gidan Hajiya Zainab zan ce miki ko zamu leƙa ta gamu da tsautsayi ta karye a hannu" ta sake faɗa, sai nayi jimm dalilin cewar da tayi wai ɗazu taga nayi baƙi, su wa ta gani ko in ce suwaye suka zo gidan tunda no dai nasan kafin na fita babu wanda yazo mun amma saboda bana son dogon surutu sai kawai nace mata
"Allah sarki Allah ya bata lafiya nima surukata ce bata da lafiya tana Aminu Kano a kwance". Jajantawa tayi haɗi da yiwa Hajjan fatan samun sauƙi kafin tace zata yiwa su Amina magana in zasu samu dama ko zuwa gobe su leƙa su dubata. A raina Allah Allah nake ta wuce shiyasa ma na tsaya ban bari mun shiga falo ba, ganin bani da niyyar bata gurin zama ya saka tayi mun sallama akan in zasu samu zuwa dubiyar gobe zata kirani nace mata toh.
Na ringa kallon tarkacen dana tarar cikin falona, daga kan kofunan da aka sha lemo da robobi har zuwa disposable packs wanda ke ɗauke da sauran abinci ga kaza da aka yiwa cin wulaƙanci duk anyi mun kaca kaca da gurin dana gyara tsaf na saka turare kafin na fita daga gidan. Ko ba'a faɗa mun ba nasan Bilal ne, wani abu ya taso daga ƙasan zuciyata ya tokare mun maƙogaro. Kenan nan ya kawo su ya buɗe musu ɗakina suka shiga ba tareda izinina ba? A hankali na ringa takawa saboda yanda nakejin tamkar zan faɗi saboda ƙuncin daya mamayemun zuciya. Ɗaki na wuce na samu gefen gado ma zauna lokaci ɗaya hawaye masu tsananin zafi suka ɓalle mun. Bansan adadin lokacin dana ɗauka zaune ba saida na jiyo ana kiran sallar magriba lokacin kuma naji ana bugun ƙofa kamar za'a ɓalla ta.
Tun daga ƙofar falo na fara jiyo ihun kukan Sharifa, na ƙarasa da sauri na buɗe naci karo da Mu'azzam fuskar nan kamar zeyi aman wuta yana ganin na buɗe ya direta a ƙasa ya juya ba tareda ya ce mun komai ba haka na jasu muka shige cikin gidan Al'amin na gaya mun sun daɗe a tsaye suna ta buga ƙofa ba'a buɗe ba.
"Mami me akayi miki kike kuka ko baki da lafiya?" Ya faɗa yana kallona dan guri na sake nema na zauna ina shayar da Sharifan ina hawaye. Maganar sa ta saka na shiga goge fuskata can ƙasan zuciyata wani ɓangare yana tunasar dani cewa
"Kuka ba zai miki maganin damuwarki ba Halima".
Sai ƙarfe sha ɗaya da mintuna Bilal ya dawo gidan ina zaune a falon da ban ɗaga ko tsinke daga abinda na dawo na tarar ba naji motsin buɗe ƙofa, ban motsa ba saida naji an cire kwaɗon dake jikin get ana ƙoƙarin zugeshi kafin na miƙe a tsorace saboda tun da aka ƙwace Mashin ɗin Bilal ba'a buɗe get ɗin amma dana hangoshi ta window sai hankalina ya kwanta na koma na zauna, gunjin mota da naji ana ƙoƙarin shigowa da ita gidan ya saka na sake miƙewa da sauri na tafi bakin ƙofa. Ina tsaye har ya gama daidaita parking ya fita ya kulle get ua sake komawa cikin motar, motar da suka tafi daga Asibitin a ciki ce ɗazu.
Sai da ya kwashi kusan minti biyar a ciki kafin ya fito waya kare a kunnensa ya wuce part ɗin sa ba tareda ya nuna koda alamar yaga tsayuwata ba dukda nasan cewar ya ganni dan ƙofa a buɗe take. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka na koma na zauna ƙwaƙwalwata da zuciyata cunkushe har na rasa wane tunani ya kamata nayi a lokacin, ina nan zaune ya sake fitowa ina jiyo takunsa kan barander nayi saurin kwanciya kan kujera haɗi da lumshe idanuwana tamkar me bacci. Har raina naji tsakin daya ja bayan daya shigo falon ya tsaya a kaina kafin ya shiga jijjiga ƙafata yana kiran sunana.
Na tashi na zauna ina kare idona tamkar daga baccin gaske na farka, da ido ya nuna mun tsakiyar falon kafin ya ce
"Menene haka? Amma dai kin san na tsani kwana da datti a cikin gida ko?"
Na bi gurin da kallo nima kafin cikin zafin ran da ban taɓa sanin ina da shi ba na ce
"Mai ya hana ka faɗawa waɗanda suka ɓata gurin su gyara ko kuwa haka suka zo suka tarar dashi?"
Ga mamakina sai gani nayi ya saki murmushin dake narkar da zuciyata a duk sanda nayi katarin arba dashi kafin ya zaune gefena harda ɗora ƙafafu akan cinyarsa cikin murya mai cike da annashuwa ya ce
"Kuma kin san saida tace in bari ta gyara amma na hana".
Ji nayi tamkar ya daɓa mun wuƙa a ƙahon zuci, na janye ƙafafu na daga jikinsa haɗi da gyara zamana ina kallonsa, sau biyu ina buɗe baki amma sautin muryata yaƙi bani haɗin kai gurin furta kalaman dake kan harshe na sai kawai na fashe da kuka, abinda ya sake karyar mun da zuciya yanda ya miƙe tamkar baiga hawayen da nakeyi ba ya wuce kitchen ya ɗakko tsintsiya da dustbin ya shiga tattare gurin, saida ya share tas ya gyara gurin sannan ya dawo kusa dani ya zauna haɗi da jana jikinsa. Duk yanda na so na ƙwaci kaina yaƙi bani dama.
Ban taɓa jin na tsani tarayya da Bilal ba irin na wannan daren, nayi kuka tamkar raina zai fita shi kuwa ko a jikinsa daga ƙarshe da yaga zan ɓata masa lokaci ma ƙarfi ya sakamun yayi yanda yaga dama dani kafin ya tsallake ya barni a nan falon ya koma part ɗinsa. Saida idanuwana suka daina kawo ruwa suka fara mun raɗaɗi tamkar na yi kwalli da yaji kafin na haƙurewa kaina kukan na tashi na gyara jikina. Ranar yanda naga rana haka naga dare, ina zaune inda na idar da sallar asuba ya shigo falon, kan kujera ya zauna yana danna qayar dake hannun sa nayi masa kallo ɗaya na mayar da kaina ƙasa ba tareda nace masa komai kusan minti biyar kafin ya ce
"Ga kaya can a kitchen ki haɗa abin kari na mutum uku ƙarfe takwas zan fita dashi ba sai kinyi wanda za'a kai Asibiti ba" yayi maganar cikin sigar bayar da umarni. Sai na ɗaga kai na kalle shi, so nakeyi nace ba zanyi ba amma kamar wadda aka ɗinkewa baki na kasa furta hakan, kusan minti goma bayan fitarsa ya sake dawowa har lokacin kuma ina zaune a inda ya barni, a gabana ya tsugunna ya kama hannayena yana murzawa cikin salon da yake yaudarar zuciyata da shi yace
"Kada ki fara abinda ba halinki ba Halima, tun jiya na lura shaiɗan yana yawo a cikin kanki idan kika biye masa zai saka ki aikata abinda zakizo kina dana sani daga baya alhalin baki da wata hujja akan hakan".
I wanted to summarize it in one or 2 chapters but i was overruled
Nagode da masoya na haƙiƙa waɗanda ko sunyi fushi basu manta tunanin su, waɗanda suke yiwa Marubuci kallon Mutum ba wai Bawa da suka siya da kuɗi ba.
[4/1, 9:08 AM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 08142548705* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 32*
*Barkanmu da Sallah yan uwa* 🙏🏽
Sai da na fita kofar asibitin kafin na tsaya ina raba ido, ina zan nufa ne ma? Gida zan tafi ko kuwa gari zan shiga cigiyar inda Bilal ya tafi? Na kai hannu na share laimar da naji akan fuskata wadda ban tantance hawaye bane ko zufa kafin na shiga tare abin hawa, gidanmu na wuce, ban ko karɓi canji ba bayan na sauka na shige gidan a bakin ƙofa na zauna kamar wata zararriya na fasa kukan da ya saka Mama ta fito daga falo kamar zata hantsila da Sharifa a hannunta ta shiga tambayata mai ya faru?
"Mutuwa Hajjan tayi?" Ta faɗa tana kallona sai na girgiza kai ina turza ƙafa kamar ƙaramar yarinya na sake gyara zama ina cigaba da kukan. Sai ta buga mun tsawa tace
"Bana son iskanci Halima haka nan zakizo ki faɗar mun da gaba na tambaye ki menene kuma kinƙi faɗa to tashi ki fita tun ban rufeki da duka ba". Ganin ta ajiye Sharifa na san zata iya dukan nawa kamar yanda ta faɗa hakan yasa na miƙe na shige falon da sauri ina cigaba da kukan. Bata sake bi ta kaina ba, sai da nayi mai isata kafin na kama hanyar gida ba tareda nayiwa Mama sallama ko na ɗauki su Sharifa ba na tafi.
Ina ƙoƙarin buɗe gida naji muryar Maman Yusuf tana kirana, na waiga ganin ta nufoni yasa na tura ƙofar na shiga itama ta biyo bayana.
"Kin dawo kenan" ta faɗa tana kallona ba tareda mun haɗa ido ba dan bana son ta fara tuhumata mai ya sameni na bata amsa da "eh na dawo".
"Ai har zan shigo ɗazun sai kuma naga kina da baƙi sai kawai na wuce dama can gidan Hajiya Zainab zan ce miki ko zamu leƙa ta gamu da tsautsayi ta karye a hannu" ta sake faɗa, sai nayi jimm dalilin cewar da tayi wai ɗazu taga nayi baƙi, su wa ta gani ko in ce suwaye suka zo gidan tunda no dai nasan kafin na fita babu wanda yazo mun amma saboda bana son dogon surutu sai kawai nace mata
"Allah sarki Allah ya bata lafiya nima surukata ce bata da lafiya tana Aminu Kano a kwance". Jajantawa tayi haɗi da yiwa Hajjan fatan samun sauƙi kafin tace zata yiwa su Amina magana in zasu samu dama ko zuwa gobe su leƙa su dubata. A raina Allah Allah nake ta wuce shiyasa ma na tsaya ban bari mun shiga falo ba, ganin bani da niyyar bata gurin zama ya saka tayi mun sallama akan in zasu samu zuwa dubiyar gobe zata kirani nace mata toh.
Na ringa kallon tarkacen dana tarar cikin falona, daga kan kofunan da aka sha lemo da robobi har zuwa disposable packs wanda ke ɗauke da sauran abinci ga kaza da aka yiwa cin wulaƙanci duk anyi mun kaca kaca da gurin dana gyara tsaf na saka turare kafin na fita daga gidan. Ko ba'a faɗa mun ba nasan Bilal ne, wani abu ya taso daga ƙasan zuciyata ya tokare mun maƙogaro. Kenan nan ya kawo su ya buɗe musu ɗakina suka shiga ba tareda izinina ba? A hankali na ringa takawa saboda yanda nakejin tamkar zan faɗi saboda ƙuncin daya mamayemun zuciya. Ɗaki na wuce na samu gefen gado ma zauna lokaci ɗaya hawaye masu tsananin zafi suka ɓalle mun. Bansan adadin lokacin dana ɗauka zaune ba saida na jiyo ana kiran sallar magriba lokacin kuma naji ana bugun ƙofa kamar za'a ɓalla ta.
Tun daga ƙofar falo na fara jiyo ihun kukan Sharifa, na ƙarasa da sauri na buɗe naci karo da Mu'azzam fuskar nan kamar zeyi aman wuta yana ganin na buɗe ya direta a ƙasa ya juya ba tareda ya ce mun komai ba haka na jasu muka shige cikin gidan Al'amin na gaya mun sun daɗe a tsaye suna ta buga ƙofa ba'a buɗe ba.
"Mami me akayi miki kike kuka ko baki da lafiya?" Ya faɗa yana kallona dan guri na sake nema na zauna ina shayar da Sharifan ina hawaye. Maganar sa ta saka na shiga goge fuskata can ƙasan zuciyata wani ɓangare yana tunasar dani cewa
"Kuka ba zai miki maganin damuwarki ba Halima".
Sai ƙarfe sha ɗaya da mintuna Bilal ya dawo gidan ina zaune a falon da ban ɗaga ko tsinke daga abinda na dawo na tarar ba naji motsin buɗe ƙofa, ban motsa ba saida naji an cire kwaɗon dake jikin get ana ƙoƙarin zugeshi kafin na miƙe a tsorace saboda tun da aka ƙwace Mashin ɗin Bilal ba'a buɗe get ɗin amma dana hangoshi ta window sai hankalina ya kwanta na koma na zauna, gunjin mota da naji ana ƙoƙarin shigowa da ita gidan ya saka na sake miƙewa da sauri na tafi bakin ƙofa. Ina tsaye har ya gama daidaita parking ya fita ya kulle get ua sake komawa cikin motar, motar da suka tafi daga Asibitin a ciki ce ɗazu.
Sai da ya kwashi kusan minti biyar a ciki kafin ya fito waya kare a kunnensa ya wuce part ɗin sa ba tareda ya nuna koda alamar yaga tsayuwata ba dukda nasan cewar ya ganni dan ƙofa a buɗe take. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka na koma na zauna ƙwaƙwalwata da zuciyata cunkushe har na rasa wane tunani ya kamata nayi a lokacin, ina nan zaune ya sake fitowa ina jiyo takunsa kan barander nayi saurin kwanciya kan kujera haɗi da lumshe idanuwana tamkar me bacci. Har raina naji tsakin daya ja bayan daya shigo falon ya tsaya a kaina kafin ya shiga jijjiga ƙafata yana kiran sunana.
Na tashi na zauna ina kare idona tamkar daga baccin gaske na farka, da ido ya nuna mun tsakiyar falon kafin ya ce
"Menene haka? Amma dai kin san na tsani kwana da datti a cikin gida ko?"
Na bi gurin da kallo nima kafin cikin zafin ran da ban taɓa sanin ina da shi ba na ce
"Mai ya hana ka faɗawa waɗanda suka ɓata gurin su gyara ko kuwa haka suka zo suka tarar dashi?"
Ga mamakina sai gani nayi ya saki murmushin dake narkar da zuciyata a duk sanda nayi katarin arba dashi kafin ya zaune gefena harda ɗora ƙafafu akan cinyarsa cikin murya mai cike da annashuwa ya ce
"Kuma kin san saida tace in bari ta gyara amma na hana".
Ji nayi tamkar ya daɓa mun wuƙa a ƙahon zuci, na janye ƙafafu na daga jikinsa haɗi da gyara zamana ina kallonsa, sau biyu ina buɗe baki amma sautin muryata yaƙi bani haɗin kai gurin furta kalaman dake kan harshe na sai kawai na fashe da kuka, abinda ya sake karyar mun da zuciya yanda ya miƙe tamkar baiga hawayen da nakeyi ba ya wuce kitchen ya ɗakko tsintsiya da dustbin ya shiga tattare gurin, saida ya share tas ya gyara gurin sannan ya dawo kusa dani ya zauna haɗi da jana jikinsa. Duk yanda na so na ƙwaci kaina yaƙi bani dama.
Ban taɓa jin na tsani tarayya da Bilal ba irin na wannan daren, nayi kuka tamkar raina zai fita shi kuwa ko a jikinsa daga ƙarshe da yaga zan ɓata masa lokaci ma ƙarfi ya sakamun yayi yanda yaga dama dani kafin ya tsallake ya barni a nan falon ya koma part ɗinsa. Saida idanuwana suka daina kawo ruwa suka fara mun raɗaɗi tamkar na yi kwalli da yaji kafin na haƙurewa kaina kukan na tashi na gyara jikina. Ranar yanda naga rana haka naga dare, ina zaune inda na idar da sallar asuba ya shigo falon, kan kujera ya zauna yana danna qayar dake hannun sa nayi masa kallo ɗaya na mayar da kaina ƙasa ba tareda nace masa komai kusan minti biyar kafin ya ce
"Ga kaya can a kitchen ki haɗa abin kari na mutum uku ƙarfe takwas zan fita dashi ba sai kinyi wanda za'a kai Asibiti ba" yayi maganar cikin sigar bayar da umarni. Sai na ɗaga kai na kalle shi, so nakeyi nace ba zanyi ba amma kamar wadda aka ɗinkewa baki na kasa furta hakan, kusan minti goma bayan fitarsa ya sake dawowa har lokacin kuma ina zaune a inda ya barni, a gabana ya tsugunna ya kama hannayena yana murzawa cikin salon da yake yaudarar zuciyata da shi yace
"Kada ki fara abinda ba halinki ba Halima, tun jiya na lura shaiɗan yana yawo a cikin kanki idan kika biye masa zai saka ki aikata abinda zakizo kina dana sani daga baya alhalin baki da wata hujja akan hakan".