Sashe 50
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama ta nisa tace
"Ban taɓa ganin ɓacin ran Abban su irin na wannan karon ba. Abinda yake ta nanata mun ya kira yaron nan da kansa har sau biyu be amsa ba ya kuma aika masa da saƙo dukda haka be biyo baya ba, kenan da ace mutuwa ma Haliman tayi haka ze wofantar da ita har ayi mata sutura a bunneta babu shi babu wani nasa a gurin kome? Rantsuwa fa yayi akan ba zata zauna ba, duk ƙaunar dake tsakaninsa da Halima ya yanke wannan hukuncin ai dole na ɗaga masa ƙafa idan ya huce nasan da kansa zeyi duk abinda ya kamata. Ni yanzu damuwata ma wanda za'a tura matan. Na kira Gwaggo Habi tunda ita tace in dai tana raye aka aurar da Halima ta haihu zata je mata zaman jego amma karkiji tijarar data mun wai na kira Yaya Salamatun data ɗaure ƙugun ayi auren taje ta zauna mata.
Na yi tunanin ko Yabi ta gidan Alhaji Salahu to daga maganganun da suka ringayi jiya da suka dawo daga asibitin ma kawai na fasa karma taje ta sake samo zancen da za'a yi yawo dashi a dangi, se dai ko Zainab taje ta kama mata ayyukan gida idan yaso tayi masa magana can a dangin sa ya nemo musu me saka ruwa da wankan jinjirin kafin ta iya".
"Oh Allah, yanzu Halima da gatan ta da komai ace ana kame kamen wanda ze mata zaman jego? Allah dai ya wadaran kunnen ƙashi irin na yayan zamani. Shikenan; ki tura mata Zainab ɗin idan yaso ni na ringa zuwa ina mata wankan mu gani daga nan dai zuwa kwana uku shi kuma Abban nasu kiyi ƙoƙari ki lallaɓa shi ya barta ta dawo gida dan Allah. Ni badan bama se nacewa Abban su Sadam ya kira shi ya taushe shi dan gaskiya Yaya Amina aka bar yarinyar nan a gidan can wlh zata lalace ne kawai ga jego ga damuwar miji kar muje ya ɗora mata depression a kawai". Akan haka suka rabu dama Anty Labiba bata ma zauna a ɗakin ba balle ayi tattaunawar da ita. Har cikin ranta tana tausayawa Halima, se dai rashin sanin ciwon kan da Haliman take gwadawa yasa take danne duk wani tausayin ta take so a barta da wayonta tunda tana ganin ze fishsheta.
WASHE GARI
Da wuri Nasir yazo yayiwa Bilal sauran allura guda ɗaya cikin ukun da aka ce za'a yi masa. Anty Amina ce tamun wanka sama sama da ruwan heater shi kuma babyn ta dafa a gas ta masa a wani ɗan baho na saitin kayan robobi na dan ba'a siya masa saitin baho ba. Cikin kayayyakin dana ɗan siya na ɗakko mata riga ta saka masa mai ma se stella da nake shafawa na bata ta shafa masa dan haka nan na rasa ɓoye duk kayan sa da muka taho dasu daga gidan mu. Tana shafa masa man take tambayata bamu siyi man jarirai bane ko yaya da za'a shafa masa stella? Ni dai murmushi kawai nayi na ɗakko mata ledar da yan kayan dana tsinta suke da dubu goman daya bani sanda zeyi tafiya nace mata
"Iya kuɗin daya bani kenan yace nayi siyayya waɗannan ma cikin kuɗin da ake bani a gida nake ragewa ina siyan su".
Sak tayi, bata kuma sake cewa komai ba ta ƙarasa shirya yaron ta fita dashi nima na shiga shirya kaina. Yini guda yan uwan sa nata zuwa jaje, a ya da na fahimci abun dai kamar dai ɓata Bilal yayi se jiya aka ganshi. Wai duk wanda yazo se su ringa tambayar yaushe na haihu? Kamar dai labarin be iske su ba suke nufi har da ita kanta Hajjan bayan tijarar data so ta mun daren jiyan data dawo yau ba kunya ta ɗauki ɗan tana ta wata murna wai jiya duk hankalinta ba'a jikinta yake ba shiyasa bata fahimci komai ba.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 21*
Ina ɗaki, hayaniyar yan dubiya duk ta cika mun kunne, tun da Anty Amina ta tambaye ni abinda za'a dafa da rana na nuna mata shinkafa da mai wanda su kaɗai suka suka rage mana a gidan, ina ganin Hajja ta shiga kitchen ɗin na fito na barsu. Ta biyo ni ɗaki tana tambaya ta sauran kayan girki nace mata iya abinda muke dashi kenan, zata yi magana Anty Aminan ta jata waje shikenan nayi zamana a ɗakin ban sake fita ba suma kuma babu wadda ta sake leƙa ni. Da yaron yana gurin su ma aka maido mun dashi shikenan naja ƙofa ta na kulle duk da yunwar da nake ji dan da safe shayi kawai nasha su suka cinye sauran abincin jiya dana dawo dashi yanzun ma dana rasa mafita shayin na sake haɗawa na sha da cake, duk da ba wai na ƙoshi bane amma na rage hanya, ina gamawa na tattara komai na mayar cikin wardrobe har ina mamakin kaina wai yau ni ce nake ɓoyon abinci?
Da yamma Mama Fauziyya da Anty Labiba da Anty Mimi se wasu ƙawayen Mama su biyu suka zo tare. Tun da safe da Mama Fauziyyan ta kira ni akan zata zo tayi mana wanka na gaya mata yayar Bilal tana nan se tace zasu shigo da yamma toh.
Zuwan su ne ya fito da ni na tsaya daga bakin ƙofa jin suna gaisawa da yan uwan Bilal. Duk su biyar ɗin naji sun masa sannu, amma babu wacce ta tambayi ba'asin meya same shi suka tsallake suka shiga ɗaki na. Se da muka gaisa na fita na ɗakko musu ruwa, ina shiga kitchen Fadila ta biyo baya na. Ban ko kalli in da take ba na ɗebi ruwan a faranti na fita na barta a tsaye.
Ƙawayen Maman basu jima ba suka tafi bayan kowacce ta ajiye mu. Abin barka. Anty Labiba ce ta tafi rakasu, bayan fitar su Anty Mimi tace
"Me kuma ya samu mijin naki Halima?" Mama Fauziyya dai na ta faman juya yaron kafin ita kuma tace
"Amma dai tun safe ba'a canzawa yaron nan kaya ba ko? Ga rigarsa nan har da stain ɗin manja a jiki".
Ƙasa na yi da kai na kafin na ce
"Nima ban san abin da ya same shi ba, bayan kun tafi jiya suka dawo dashi har yanzu kuma basu ce mun komai ba" na faɗa bayan da Anty Labiba ta dawo ta sake maimaita mun tambayar Anty Mimi. Su ukun suka haɗa baki gurin cewa
"Allah ya rufa asiri" kafin Anty Labiba ta wuce banɗaki ta haɗo ruwan zafi a bahon da aka ma yaron wanka da safe ta fito tana cewa
"Se ki tashi kema kiyi wankan duk da wannan ruwan ɗauraye jiki kawai za kiyi ba wani wankan kirki ba. Bari na kira Mu'azzam idan ze kawo Zainab ɗin su taho da babbar tukunyar nan da murhu, ki dai tsaya kiyi wankan gaske wlh in ba haka na jikin ki zaki lalata".
Se da nayi jira ruwan heater ya ƙara tafasa kafin nan naci tuwon da Mama Fauziyya ta taho dashi. Ina jin yanda suke kallo na amma na ɗauke kai na ci gaba da cin abincin dan yunwa nake ji sosai, kowa dai yasan cikin jego babu yanda za ayi shayi ya riƙe ni tun safe dan da suka dafa shinkafar ko tayi basu mun ba. Anty Mimi da bakin ta be fiya shiru ba ce ta kasa daurewa tace
"Baki ci abincin rana bane Halima?"
"Na ci mana Anty" na bata amsa ina ɗauke kwanon gaba na, kafin kuma wani ya sake cewa komai na fice dan kai kwanon kitchen. Motsin da naji a bayana yasa na juya da sauri naga Hajja ce. Fuska ba yabo ba falla sa tace
"Naga sun zo miki da abinci ko? Se ki ɗebo a bawa mijin ki idan ma mu ba zaki bamu ba". Nayi shiru na rasa abinda zan ce mata. Wato idon su na kana duk abinda ake wucewa dashi. Ganin ta juya ta fita yasa na sauke ajiyar zaciya na bi bayan ta. Tunanin ta yanda zan ɗebo abincin na fito dashi ba tare da sun mun surutu ba na shiga yi.
Cikin sa'a, ina komawa ɗakin na tarar da Anty Labiba na cin sauran tuwon dama malmala ɗaya ne tun da uku ne na ci biyu. Se na wuce sum sum na shiga cire kaya na a raina naji daɗi ta wani gefen amma kuma yanzu ban san ya zamu kaya da Hajja ba. Sanda na fito wanka Anty Mimi ta ce suruka ta na kira na, se da na shirya kafin na fita. Duk jama'ar yan dubiyar sun watse se ita kaɗai a falon Bilal ɗin ma an mayar dashi can falon sa yana tare da Abubakar.
"Wato saboda kin raina ni Halima nayi miki magana kiyi shigewar ki ɗaki ki bar ni ina zaman jiran ki ko?" Ta faɗa fuska cike da fushi. Kafin na bata amsa Anty Labiba ta fito da kwanukan tuwon bata ko kalli in da muke tsaye ba ta shige kitchen; se na yi ƙasa da kai nace
"Wlh mantawa nayi Hajja, se da na fito daga wanka suka ce kina kira na kafin na tuna kuma na tarar sun cinye sauran abincin dama bashi da yawa".
"Ban taɓa ganin ɓacin ran Abban su irin na wannan karon ba. Abinda yake ta nanata mun ya kira yaron nan da kansa har sau biyu be amsa ba ya kuma aika masa da saƙo dukda haka be biyo baya ba, kenan da ace mutuwa ma Haliman tayi haka ze wofantar da ita har ayi mata sutura a bunneta babu shi babu wani nasa a gurin kome? Rantsuwa fa yayi akan ba zata zauna ba, duk ƙaunar dake tsakaninsa da Halima ya yanke wannan hukuncin ai dole na ɗaga masa ƙafa idan ya huce nasan da kansa zeyi duk abinda ya kamata. Ni yanzu damuwata ma wanda za'a tura matan. Na kira Gwaggo Habi tunda ita tace in dai tana raye aka aurar da Halima ta haihu zata je mata zaman jego amma karkiji tijarar data mun wai na kira Yaya Salamatun data ɗaure ƙugun ayi auren taje ta zauna mata.
Na yi tunanin ko Yabi ta gidan Alhaji Salahu to daga maganganun da suka ringayi jiya da suka dawo daga asibitin ma kawai na fasa karma taje ta sake samo zancen da za'a yi yawo dashi a dangi, se dai ko Zainab taje ta kama mata ayyukan gida idan yaso tayi masa magana can a dangin sa ya nemo musu me saka ruwa da wankan jinjirin kafin ta iya".
"Oh Allah, yanzu Halima da gatan ta da komai ace ana kame kamen wanda ze mata zaman jego? Allah dai ya wadaran kunnen ƙashi irin na yayan zamani. Shikenan; ki tura mata Zainab ɗin idan yaso ni na ringa zuwa ina mata wankan mu gani daga nan dai zuwa kwana uku shi kuma Abban nasu kiyi ƙoƙari ki lallaɓa shi ya barta ta dawo gida dan Allah. Ni badan bama se nacewa Abban su Sadam ya kira shi ya taushe shi dan gaskiya Yaya Amina aka bar yarinyar nan a gidan can wlh zata lalace ne kawai ga jego ga damuwar miji kar muje ya ɗora mata depression a kawai". Akan haka suka rabu dama Anty Labiba bata ma zauna a ɗakin ba balle ayi tattaunawar da ita. Har cikin ranta tana tausayawa Halima, se dai rashin sanin ciwon kan da Haliman take gwadawa yasa take danne duk wani tausayin ta take so a barta da wayonta tunda tana ganin ze fishsheta.
WASHE GARI
Da wuri Nasir yazo yayiwa Bilal sauran allura guda ɗaya cikin ukun da aka ce za'a yi masa. Anty Amina ce tamun wanka sama sama da ruwan heater shi kuma babyn ta dafa a gas ta masa a wani ɗan baho na saitin kayan robobi na dan ba'a siya masa saitin baho ba. Cikin kayayyakin dana ɗan siya na ɗakko mata riga ta saka masa mai ma se stella da nake shafawa na bata ta shafa masa dan haka nan na rasa ɓoye duk kayan sa da muka taho dasu daga gidan mu. Tana shafa masa man take tambayata bamu siyi man jarirai bane ko yaya da za'a shafa masa stella? Ni dai murmushi kawai nayi na ɗakko mata ledar da yan kayan dana tsinta suke da dubu goman daya bani sanda zeyi tafiya nace mata
"Iya kuɗin daya bani kenan yace nayi siyayya waɗannan ma cikin kuɗin da ake bani a gida nake ragewa ina siyan su".
Sak tayi, bata kuma sake cewa komai ba ta ƙarasa shirya yaron ta fita dashi nima na shiga shirya kaina. Yini guda yan uwan sa nata zuwa jaje, a ya da na fahimci abun dai kamar dai ɓata Bilal yayi se jiya aka ganshi. Wai duk wanda yazo se su ringa tambayar yaushe na haihu? Kamar dai labarin be iske su ba suke nufi har da ita kanta Hajjan bayan tijarar data so ta mun daren jiyan data dawo yau ba kunya ta ɗauki ɗan tana ta wata murna wai jiya duk hankalinta ba'a jikinta yake ba shiyasa bata fahimci komai ba.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 21*
Ina ɗaki, hayaniyar yan dubiya duk ta cika mun kunne, tun da Anty Amina ta tambaye ni abinda za'a dafa da rana na nuna mata shinkafa da mai wanda su kaɗai suka suka rage mana a gidan, ina ganin Hajja ta shiga kitchen ɗin na fito na barsu. Ta biyo ni ɗaki tana tambaya ta sauran kayan girki nace mata iya abinda muke dashi kenan, zata yi magana Anty Aminan ta jata waje shikenan nayi zamana a ɗakin ban sake fita ba suma kuma babu wadda ta sake leƙa ni. Da yaron yana gurin su ma aka maido mun dashi shikenan naja ƙofa ta na kulle duk da yunwar da nake ji dan da safe shayi kawai nasha su suka cinye sauran abincin jiya dana dawo dashi yanzun ma dana rasa mafita shayin na sake haɗawa na sha da cake, duk da ba wai na ƙoshi bane amma na rage hanya, ina gamawa na tattara komai na mayar cikin wardrobe har ina mamakin kaina wai yau ni ce nake ɓoyon abinci?
Da yamma Mama Fauziyya da Anty Labiba da Anty Mimi se wasu ƙawayen Mama su biyu suka zo tare. Tun da safe da Mama Fauziyyan ta kira ni akan zata zo tayi mana wanka na gaya mata yayar Bilal tana nan se tace zasu shigo da yamma toh.
Zuwan su ne ya fito da ni na tsaya daga bakin ƙofa jin suna gaisawa da yan uwan Bilal. Duk su biyar ɗin naji sun masa sannu, amma babu wacce ta tambayi ba'asin meya same shi suka tsallake suka shiga ɗaki na. Se da muka gaisa na fita na ɗakko musu ruwa, ina shiga kitchen Fadila ta biyo baya na. Ban ko kalli in da take ba na ɗebi ruwan a faranti na fita na barta a tsaye.
Ƙawayen Maman basu jima ba suka tafi bayan kowacce ta ajiye mu. Abin barka. Anty Labiba ce ta tafi rakasu, bayan fitar su Anty Mimi tace
"Me kuma ya samu mijin naki Halima?" Mama Fauziyya dai na ta faman juya yaron kafin ita kuma tace
"Amma dai tun safe ba'a canzawa yaron nan kaya ba ko? Ga rigarsa nan har da stain ɗin manja a jiki".
Ƙasa na yi da kai na kafin na ce
"Nima ban san abin da ya same shi ba, bayan kun tafi jiya suka dawo dashi har yanzu kuma basu ce mun komai ba" na faɗa bayan da Anty Labiba ta dawo ta sake maimaita mun tambayar Anty Mimi. Su ukun suka haɗa baki gurin cewa
"Allah ya rufa asiri" kafin Anty Labiba ta wuce banɗaki ta haɗo ruwan zafi a bahon da aka ma yaron wanka da safe ta fito tana cewa
"Se ki tashi kema kiyi wankan duk da wannan ruwan ɗauraye jiki kawai za kiyi ba wani wankan kirki ba. Bari na kira Mu'azzam idan ze kawo Zainab ɗin su taho da babbar tukunyar nan da murhu, ki dai tsaya kiyi wankan gaske wlh in ba haka na jikin ki zaki lalata".
Se da nayi jira ruwan heater ya ƙara tafasa kafin nan naci tuwon da Mama Fauziyya ta taho dashi. Ina jin yanda suke kallo na amma na ɗauke kai na ci gaba da cin abincin dan yunwa nake ji sosai, kowa dai yasan cikin jego babu yanda za ayi shayi ya riƙe ni tun safe dan da suka dafa shinkafar ko tayi basu mun ba. Anty Mimi da bakin ta be fiya shiru ba ce ta kasa daurewa tace
"Baki ci abincin rana bane Halima?"
"Na ci mana Anty" na bata amsa ina ɗauke kwanon gaba na, kafin kuma wani ya sake cewa komai na fice dan kai kwanon kitchen. Motsin da naji a bayana yasa na juya da sauri naga Hajja ce. Fuska ba yabo ba falla sa tace
"Naga sun zo miki da abinci ko? Se ki ɗebo a bawa mijin ki idan ma mu ba zaki bamu ba". Nayi shiru na rasa abinda zan ce mata. Wato idon su na kana duk abinda ake wucewa dashi. Ganin ta juya ta fita yasa na sauke ajiyar zaciya na bi bayan ta. Tunanin ta yanda zan ɗebo abincin na fito dashi ba tare da sun mun surutu ba na shiga yi.
Cikin sa'a, ina komawa ɗakin na tarar da Anty Labiba na cin sauran tuwon dama malmala ɗaya ne tun da uku ne na ci biyu. Se na wuce sum sum na shiga cire kaya na a raina naji daɗi ta wani gefen amma kuma yanzu ban san ya zamu kaya da Hajja ba. Sanda na fito wanka Anty Mimi ta ce suruka ta na kira na, se da na shirya kafin na fita. Duk jama'ar yan dubiyar sun watse se ita kaɗai a falon Bilal ɗin ma an mayar dashi can falon sa yana tare da Abubakar.
"Wato saboda kin raina ni Halima nayi miki magana kiyi shigewar ki ɗaki ki bar ni ina zaman jiran ki ko?" Ta faɗa fuska cike da fushi. Kafin na bata amsa Anty Labiba ta fito da kwanukan tuwon bata ko kalli in da muke tsaye ba ta shige kitchen; se na yi ƙasa da kai nace
"Wlh mantawa nayi Hajja, se da na fito daga wanka suka ce kina kira na kafin na tuna kuma na tarar sun cinye sauran abincin dama bashi da yawa".