Sashe 83
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ban taɓa riskar dare mai tsayi irin na ranar ba, na ringaji inama ina da ikon janyo safiya ko kuma na fito da masu abin hawa domin na samu wanda zai kaini gida? A cikin dare na haɗa mana kaya na fitar dasu barander na ajiye dan na ƙudurce ko da jinin jaka Bilal ya tsafance ni da yardar Allah sai na karya asirin yau na bar masa gidan sa koda kuwa hakan yana nufin tsayawar numfashi na a doron ƙasa. Ƙarfe shida na goya Sharifa daƙyar dan tun cikin dare ciwon kai da zafin ƙirji ya sake dawo mun, na riƙe hannun Al'amin dake tafiya daƙyar dan ko farkawa baiyi daga bacci ba ni na ɗaga shi na aje shi kan ƙafafunsa. Muna fitowa falo naji ƙarar buɗe Get, wani dunƙule ya taso daga cikina ya tsaya mun a maƙogaro.
Haka na ringa jansa muka fito daga falon lokacin har ya fita da mota ya dawo yana zuge Get ɗin na kalli kan Barander inda na aje kaya basa nan sai ji nayi ya ce
"Gasu can a mota muje na kaiku tunda kin san babu yanda za'a yi ku fita da sassafen nan da kaya duk yan unguwa suna kallonki".
Nayi murmushin da yafi kuka ciwo, wato maganar yan unguwa yake gudu amma baya kunyar ubangijin sa yake kiran Zina da Normal abu. Ina buƙatar na isa gidan da wuri na san kuma tafiyar tawa bata dame shi ba zai ma fi farin ciki da hakan shiyasa na yarda na shiga motar muka tafi. Har muka isa gidan babu wanda ya cw uffan a tsakaninmu har muka isa ƙofar gidanmu. Ina ƙoƙarin buɗe motar naji ya ce
"Ina sake jaddada miki dariyar da za'a miki sai tafi laifina da zasu gani yawa, infact sai kin tsani kanki Halima muddin aibu na ya fita daga bakinki" sai na waiwaya na kalle shi na ce
"Barazana kake yi mun kenan?" Ya ɗage kafaɗa n ƙarasa ɓalle murfin motar na fita ban ko lura da Abba dake tsaye bakin Get da maƙwafcinmu Alhaji Bala suna magana ba na shige ciki.
A tsakiyar falo na kwance goyon Sharifa dan ji nake kamar zan faɗi na mutu a gurin kai tsaye kuma na shige tsohon ɗaki na sama sama ina jiyo kamar muryar Amirah tana kiran sunana amma ban tsaya ba.
[4/6, 10:24 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 35*
Amirah ta ɗaga Sharifa data saka kuka daidai lokacin da Mama ta fito daga kitchen lokacin kuma Al'amin shima ya shigo Suraj na biye dashi da akwatin mu.
"Ku kuma daga ina haka da sassafe?" Mama ta tambaya, Suraj ya ajiye kayan yana cewa
"Tareda Babansu suke" ya juya ya fita sai Amirah tace
"Yaya Haliman tana ciki itama". Tsaye Mama tayi kafin tace
"Toh lafiya dai?"
"Gaskiya ba lafiya ba kinga fa jefar da Sharifa tayi ta wuce ina mata magana ko saurarona ma batayi ba" Amirah ta amsa mata. Jumm tayi tana kallon Al'amin daya haye kan kujera ya kwanta alamar baccin sa zai cigaba, sai ta juya kitchen ba tareda tace komai ba amma zuciyarta cike da saƙe saƙe.
Kan gado na faɗa bayan dana shiga ɗakin dafe da ƙirjina da nake ji tamkar an ɗaure ni da igiya, daƙyar nake fuzgar numfashi, na ringa juyi a kan gado ni kaɗai tsayin lokaci kafin ubangiji ya kawo mun rangwamen abinda nakeji ta hanyar rabani da numfashina na wani lokaci.
A waya Mama ta kira Abba, tambayar sa tayi ko Bilal yace masa wani abu ne tunda ance tare muka zo sai ya ce mata
"Bai tsaya ba yana sauke musu kayan su ya juya ko gaisawa bamuyi ba"
"Ikon Allah, to mai ya faru?" Ta sake tambaya cikin jimami. Daga can yace
"Ni kam ina zan sani ne Amina? Ba gata nan a cikin gidan ki tambayeta mana", jin kamar ya fara fusata ua saka tace
"Toh shikenan sai ka dawo" ba tareda ya bata amsa ba ya katse wayar dan ransa y sosu matuƙa da ko in kulan da Bilal ya musu. Sosai yaji ba daɗi sanda Alhaji Bala da suke tsaye yace masa
"Wannan ba Mijin Halima bane naga yaja mota bai ko tsaya ya gaida mu ba? Koda yake yanda ta shige itama kamar dai akwai matsala dan na lura bata ma ga tsayuwarmu ba, amma shi ai idan ɗan arziƙi ne yaci ko matsala suka samu ya tsaya nan ya maka bayani ba yaja mota ya tafi ba".
Wannan maganar ta dame shi har ta saka ya fasa komawa cikin gidan da yayi niyya ya sallami Alhaji Balan kawai ya wuce inda zashi ya a tafe kuma yana tunanin dalilin zuwan Halima da sassafen nan.
Sai gurin ƙarfe tara Mama tace Amirah ta shiga ta kirawo Halima ta karya lokacin har tayiwa su Al'amin wanka sun ƙoshi sun shiga sabgogin su, ihun da Amirah ta fasa bayan shigar ta ɗakin ya saka Maman tashi da sauri tamkar zata hantsila ta shiga ɗakin, gabanta ya yanke ya faɗi ganin Amirah tsugunne kan Halima tana girgiza ta haditda kiran sunanta amma ko gezau bata motsa ba, cikin tashin hankali ta isa gaban gadon ta ɗagota jikinta ta shiga jijjigata da ƙarfi amma bata koyi alamar zata farka ba.
"Ta mutu innalillahi mun shiga uku Yaya Halima ta mutu" Amirah ta faɗa hannu biyu akai cikin matsanancin kuka Mama dake rungume da Halima ta ɗaga mata hannu tana cewa
"Bata mutu ba fita ki kira Mu'azzam, kiyi sauri dan Allah yazo mu kaita asibiti" ta ƙarasa tana ƙoƙarin buɗe idanun Haliman. Da gudu Amirah ta nufi ƙofa sai kuma ta juyo cikin kuka tace
"Kin manta ya tafi makaranta tun ɗazu yana da exam yau?"
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Amirah ki fita kowa kika gani ki kira mu kaita Asibiti" Mama ta faɗa tana fashewa da kuka itama. Tareda Samari biyu Amirah ta dawo wanda a waje ta taresu sun taho a mota su suka ɗauki Haliman suka fito da ita daga Mama har Amiran babu wanda ya tsaya neman koda Takalmi suka biyo su Zainab na kuka riƙe da Sharifa haka Al'amin dukda ba wai sanin mai yake faruwa yayi ba kawai ganin sunayi ya saka shima ya kama. Suna ƙoƙarin sakata a motarsu Suraj ya iso ƙofar gidan dan dama tare suka fita da Abba ya kaishi Airport zai tafi Lagos, motar sa Mama tace su sakata suka shiga ita da Amirah ya ja motar da gudun gaske suka nufi asibiti.
Bayan tsayin lokacin dana ɗauka tsakanin mutuwa da rayuwa na farka, na buɗe idanuwana da naji tamkar an manne mun su da super glue daƙyar na iya buɗe su na kalli in da nake saidai ban fahimci komai ba hakan ya saka na sake mayar da idanuwan nawa na kulle ina jin sautuka sama sama kamar daga can nesa. Mama dake zaune kan kujerar dake kusa dani ta miƙe da sauri saboda ƙafata dana motsa, ta kira sunana, dukda ba wai na fahimci mai ta faɗa ba sautin da naji ya saka na sake buɗe idona na sauke akan fuskarta. Ta kama hannuna hawaye na ziraro mata tace
"Kin farka Halima?" A hankali tamkar mai koyon magana na kira sunanta a rarrabe "Ma..ma" haɗi da matsa hannunta data riƙe nawa dashi. Cikin kuka mai haɗe da dariya ta amsa da
"Na'am Halima kin farka? Alhamdulillah". Ji nayi maganganunta suna hau mun kai sai na sake mayar da idona na rufe tayi azamar kamo fuskata tana cewa
"Ki tashi dan Allah kada ki sake komawa Halima dan Allah ki buɗe idonki ko hankalina zai kwanta" ta ƙarasa cikin kuka. Na sake buɗe idona na kalleta, tabbas naga ƙauna mai tsanani haɗi da tausayi cikin ƙwayar idanunta dake tsiyayar da hawaye, kalaman Bilal da ya ce "Da uwarki nayi zina" suka dirar mun tamkar saukar mashi take wani abu ya taso ya sake tokare mun maƙogaro, ban iya yin abinda ta buƙata ba na sake mayar da idanuna ruf na rufe su sai ta saki hannuna ta nufi ƙofa kusan da gudu ta fice daga ɗakin ba jimawa suka dawo tareda likita da Nurses biyu. Sai da ya gama dubani kafin ya kalleta cikin kalaman kwantar da hankali yace
"Kiyi haƙuri Hajiya na faɗa miki jikinta yana da buƙatar hutu sosai zata farka idan lokacin hakan yayi in sha Allahu ki daina damuwa zata samu lafiya da yardar Allah"
"Likita ta farka fa, ta buɗe idonta har magana tayi mun kafin ta sake komawa dan Allah likita kayi wani abun yarinya ta ta farka kaifa kace mun awanni kaɗan amma gashi kwana biyu kenan bata farka ba". Kwana biyun data ambata ya saka na sake buɗe idona na kalle su, hannu biyu ta ɗaga tana cewa
"Alhamdulillah, ka gani ko idonta biyu". Ganin tana ƙoƙarin ɗago ni ya saka ya dakatar da ita, a hankali ya kira sunana na kalle shi yace
"Kina jina Halima?" Nayi shiru badan bana jin sa ba sai dan bansan ta yanda zan amsa masa ba. Bakina yayi mun nauyi tamkar an ɗaure mun harshe. Cikin taushi ya sake kiran sunana da maimaita tambaya ina jinsa amma na kasa amsawa. Mama ta fashe da kuka tana cewa
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Dr mai ya samu yarinyata dan Allah kayi mun bayani ni Musulma ce koma menene zanyi haƙuri na karɓi ƙaddarar data samemu".
Haka na ringa jansa muka fito daga falon lokacin har ya fita da mota ya dawo yana zuge Get ɗin na kalli kan Barander inda na aje kaya basa nan sai ji nayi ya ce
"Gasu can a mota muje na kaiku tunda kin san babu yanda za'a yi ku fita da sassafen nan da kaya duk yan unguwa suna kallonki".
Nayi murmushin da yafi kuka ciwo, wato maganar yan unguwa yake gudu amma baya kunyar ubangijin sa yake kiran Zina da Normal abu. Ina buƙatar na isa gidan da wuri na san kuma tafiyar tawa bata dame shi ba zai ma fi farin ciki da hakan shiyasa na yarda na shiga motar muka tafi. Har muka isa gidan babu wanda ya cw uffan a tsakaninmu har muka isa ƙofar gidanmu. Ina ƙoƙarin buɗe motar naji ya ce
"Ina sake jaddada miki dariyar da za'a miki sai tafi laifina da zasu gani yawa, infact sai kin tsani kanki Halima muddin aibu na ya fita daga bakinki" sai na waiwaya na kalle shi na ce
"Barazana kake yi mun kenan?" Ya ɗage kafaɗa n ƙarasa ɓalle murfin motar na fita ban ko lura da Abba dake tsaye bakin Get da maƙwafcinmu Alhaji Bala suna magana ba na shige ciki.
A tsakiyar falo na kwance goyon Sharifa dan ji nake kamar zan faɗi na mutu a gurin kai tsaye kuma na shige tsohon ɗaki na sama sama ina jiyo kamar muryar Amirah tana kiran sunana amma ban tsaya ba.
[4/6, 10:24 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 35*
Amirah ta ɗaga Sharifa data saka kuka daidai lokacin da Mama ta fito daga kitchen lokacin kuma Al'amin shima ya shigo Suraj na biye dashi da akwatin mu.
"Ku kuma daga ina haka da sassafe?" Mama ta tambaya, Suraj ya ajiye kayan yana cewa
"Tareda Babansu suke" ya juya ya fita sai Amirah tace
"Yaya Haliman tana ciki itama". Tsaye Mama tayi kafin tace
"Toh lafiya dai?"
"Gaskiya ba lafiya ba kinga fa jefar da Sharifa tayi ta wuce ina mata magana ko saurarona ma batayi ba" Amirah ta amsa mata. Jumm tayi tana kallon Al'amin daya haye kan kujera ya kwanta alamar baccin sa zai cigaba, sai ta juya kitchen ba tareda tace komai ba amma zuciyarta cike da saƙe saƙe.
Kan gado na faɗa bayan dana shiga ɗakin dafe da ƙirjina da nake ji tamkar an ɗaure ni da igiya, daƙyar nake fuzgar numfashi, na ringa juyi a kan gado ni kaɗai tsayin lokaci kafin ubangiji ya kawo mun rangwamen abinda nakeji ta hanyar rabani da numfashina na wani lokaci.
A waya Mama ta kira Abba, tambayar sa tayi ko Bilal yace masa wani abu ne tunda ance tare muka zo sai ya ce mata
"Bai tsaya ba yana sauke musu kayan su ya juya ko gaisawa bamuyi ba"
"Ikon Allah, to mai ya faru?" Ta sake tambaya cikin jimami. Daga can yace
"Ni kam ina zan sani ne Amina? Ba gata nan a cikin gidan ki tambayeta mana", jin kamar ya fara fusata ua saka tace
"Toh shikenan sai ka dawo" ba tareda ya bata amsa ba ya katse wayar dan ransa y sosu matuƙa da ko in kulan da Bilal ya musu. Sosai yaji ba daɗi sanda Alhaji Bala da suke tsaye yace masa
"Wannan ba Mijin Halima bane naga yaja mota bai ko tsaya ya gaida mu ba? Koda yake yanda ta shige itama kamar dai akwai matsala dan na lura bata ma ga tsayuwarmu ba, amma shi ai idan ɗan arziƙi ne yaci ko matsala suka samu ya tsaya nan ya maka bayani ba yaja mota ya tafi ba".
Wannan maganar ta dame shi har ta saka ya fasa komawa cikin gidan da yayi niyya ya sallami Alhaji Balan kawai ya wuce inda zashi ya a tafe kuma yana tunanin dalilin zuwan Halima da sassafen nan.
Sai gurin ƙarfe tara Mama tace Amirah ta shiga ta kirawo Halima ta karya lokacin har tayiwa su Al'amin wanka sun ƙoshi sun shiga sabgogin su, ihun da Amirah ta fasa bayan shigar ta ɗakin ya saka Maman tashi da sauri tamkar zata hantsila ta shiga ɗakin, gabanta ya yanke ya faɗi ganin Amirah tsugunne kan Halima tana girgiza ta haditda kiran sunanta amma ko gezau bata motsa ba, cikin tashin hankali ta isa gaban gadon ta ɗagota jikinta ta shiga jijjigata da ƙarfi amma bata koyi alamar zata farka ba.
"Ta mutu innalillahi mun shiga uku Yaya Halima ta mutu" Amirah ta faɗa hannu biyu akai cikin matsanancin kuka Mama dake rungume da Halima ta ɗaga mata hannu tana cewa
"Bata mutu ba fita ki kira Mu'azzam, kiyi sauri dan Allah yazo mu kaita asibiti" ta ƙarasa tana ƙoƙarin buɗe idanun Haliman. Da gudu Amirah ta nufi ƙofa sai kuma ta juyo cikin kuka tace
"Kin manta ya tafi makaranta tun ɗazu yana da exam yau?"
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Amirah ki fita kowa kika gani ki kira mu kaita Asibiti" Mama ta faɗa tana fashewa da kuka itama. Tareda Samari biyu Amirah ta dawo wanda a waje ta taresu sun taho a mota su suka ɗauki Haliman suka fito da ita daga Mama har Amiran babu wanda ya tsaya neman koda Takalmi suka biyo su Zainab na kuka riƙe da Sharifa haka Al'amin dukda ba wai sanin mai yake faruwa yayi ba kawai ganin sunayi ya saka shima ya kama. Suna ƙoƙarin sakata a motarsu Suraj ya iso ƙofar gidan dan dama tare suka fita da Abba ya kaishi Airport zai tafi Lagos, motar sa Mama tace su sakata suka shiga ita da Amirah ya ja motar da gudun gaske suka nufi asibiti.
Bayan tsayin lokacin dana ɗauka tsakanin mutuwa da rayuwa na farka, na buɗe idanuwana da naji tamkar an manne mun su da super glue daƙyar na iya buɗe su na kalli in da nake saidai ban fahimci komai ba hakan ya saka na sake mayar da idanuwan nawa na kulle ina jin sautuka sama sama kamar daga can nesa. Mama dake zaune kan kujerar dake kusa dani ta miƙe da sauri saboda ƙafata dana motsa, ta kira sunana, dukda ba wai na fahimci mai ta faɗa ba sautin da naji ya saka na sake buɗe idona na sauke akan fuskarta. Ta kama hannuna hawaye na ziraro mata tace
"Kin farka Halima?" A hankali tamkar mai koyon magana na kira sunanta a rarrabe "Ma..ma" haɗi da matsa hannunta data riƙe nawa dashi. Cikin kuka mai haɗe da dariya ta amsa da
"Na'am Halima kin farka? Alhamdulillah". Ji nayi maganganunta suna hau mun kai sai na sake mayar da idona na rufe tayi azamar kamo fuskata tana cewa
"Ki tashi dan Allah kada ki sake komawa Halima dan Allah ki buɗe idonki ko hankalina zai kwanta" ta ƙarasa cikin kuka. Na sake buɗe idona na kalleta, tabbas naga ƙauna mai tsanani haɗi da tausayi cikin ƙwayar idanunta dake tsiyayar da hawaye, kalaman Bilal da ya ce "Da uwarki nayi zina" suka dirar mun tamkar saukar mashi take wani abu ya taso ya sake tokare mun maƙogaro, ban iya yin abinda ta buƙata ba na sake mayar da idanuna ruf na rufe su sai ta saki hannuna ta nufi ƙofa kusan da gudu ta fice daga ɗakin ba jimawa suka dawo tareda likita da Nurses biyu. Sai da ya gama dubani kafin ya kalleta cikin kalaman kwantar da hankali yace
"Kiyi haƙuri Hajiya na faɗa miki jikinta yana da buƙatar hutu sosai zata farka idan lokacin hakan yayi in sha Allahu ki daina damuwa zata samu lafiya da yardar Allah"
"Likita ta farka fa, ta buɗe idonta har magana tayi mun kafin ta sake komawa dan Allah likita kayi wani abun yarinya ta ta farka kaifa kace mun awanni kaɗan amma gashi kwana biyu kenan bata farka ba". Kwana biyun data ambata ya saka na sake buɗe idona na kalle su, hannu biyu ta ɗaga tana cewa
"Alhamdulillah, ka gani ko idonta biyu". Ganin tana ƙoƙarin ɗago ni ya saka ya dakatar da ita, a hankali ya kira sunana na kalle shi yace
"Kina jina Halima?" Nayi shiru badan bana jin sa ba sai dan bansan ta yanda zan amsa masa ba. Bakina yayi mun nauyi tamkar an ɗaure mun harshe. Cikin taushi ya sake kiran sunana da maimaita tambaya ina jinsa amma na kasa amsawa. Mama ta fashe da kuka tana cewa
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Dr mai ya samu yarinyata dan Allah kayi mun bayani ni Musulma ce koma menene zanyi haƙuri na karɓi ƙaddarar data samemu".