Sashe 59
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"To ki zuba a kai musu dan Allah ba daɗi kusan rabin awa da zuwan su kuma sun shigo sun tarar da mutane na cin abinci"
"Za'a kai yanzu" ta sake bata amsa. Ta ke na ji sanyi a raina na waske na bar gurin ba tare da na ce mata komai ba duk da a ƙasan raina na ji kamar na tsaya na ɗibarwa Bilal ban sani ba ko ze bawa su Nasir da sauran abokanan sa na unguwa amma na san zata iya saka kaina a kular abincin shiyasa na haƙura ban koma ba. Se da aka kira Magriba taro ya fara watsewa, na samu alkhairi ƙwarai da gaske Abba ma ya yi goshi daga kan riguna kuɗi da kayan amfani su diaper da omon wanki da su sabulu mun same su babu adadi zamu ja lokaci sosai kafin su ƙare mana.
Tun da naji za'a kaiwa su Fadila abinci ban sake bi ta kan su ba musamman da ƙawaye na da mu kayi poly tare suka zo duk hankali na ya tafi ga maƙwafta masu shigowa da sauran yan uwa gaba ɗaya na sha'afa da su sai da su Baby Bashir zasu tafi na fito raka su kafin ido na ya sauka kan ƙofar ɗakin Bilal ɗin da na hango yara na tsere a ciki. Gaba ɗaya se na rasa nutsuwa, get na yi niyar taka musu amma na tsaya daga in da nake na bar su da Hansa'u ta tafi raka su wajen ni kuma na wuce ɗakin Bilal. Babu kowa sai yara dake wasa da wasu yan gidan su Abban mu yammata suna ɗaukar hoto. Ce musi na yi su fita na kullo ƙofar dan key ɗin ma a jiki suka bar shi na jefa shi cikin aljihun rigata zuciya ta na bubbugawa dan na san har dai zasu tafi ba tare da sun yi mun sallama ba tabbas da wuya idan ba Anty ta musu wani abun da ya sosa musu rai ba ne. Haushin kai na ya kama ni, ko me ya sa ban tsaya na ga abincin da ta zuba musu ba ko kuma na sake komawa gurin su na tabbatar an basu komai wadatacce, bana ma zaton ta basu souvenirs ɗin da naga ta bawa ƙawaye na da suka tafi yanzu ƙila ko daga baya aka kawo su.
Haka dai jama'a suka ida watsewa ya rage na jiki waɗanda suka tsaya suka gyara mun gida tsaf ba zaka ce anan aka sha didimar biki ba, abincin da yayi saura da yawa masu so sun ɗiba sun tafi da shi, ta zuzzuba mun abinda ze ajiyu na saka a fridge miya kuma da nama na saka a frizeer haka sauran ruwa da lemo kusan katan goma goma duk na lode su a store, basu bar gidan ba hatta kayayyakin da muka samu na barka se da suka taya ni na ware su komai ya koma muhallin sa kafin kowa ya wuce gidan sa. Ina tsaka da shafa mai bayan na watsa ruwa saboda jiki na da ya yi mun tsami sosai Bilal ya dawo.
Da Baba Jummai na jiyo suna gaisawa be shigo ɗaki na ba bayan na gama shiryawa kamar in share shi sai kuma wata zuciyar ta ce na dai je. Dama na ware masa abinci na sake ɗumamawa na haɗa komai a try na fito Baba Jummai ta bini da kallo ta na cewa
"Ba dai ɗakin sa zaki kai masa ba" na yi murmushi kaina a ƙasa dan na san baze wuce abin da ya faru jiya ya sa tayi tambayar ba se kawai na wuce na ajiye su tsakiyar falo kan center table ina cewa
"Aa, a nan zan ajiye masa"
"Ya dai fi miki" ta faɗa tana wucewa ɗaki. Fita na yi na tafi ɗakin Bilal, a falo na same shi yana waya bakin nan kamar ze tsage saboda farin ciki ina shiga ya yafito ni da hannu, ban matsa kusa da shi sosai ba na tsaya daga gefe ya miƙo mun wayar na karɓa duk da ban san waye ba sai da na kara a kunne na kafin na gane Hafiz ne.
Muka gaisa yana tambayar ina Dadyn sa tare da bani haƙuri akan rashin zuwan su wai uzuri ya taso musu basa ƙasar, ya ce Shahida ta ce idan ta kira ni bata samu na faɗa masa na yi setting layi na private ne idan ba ni da number kiran ba ze shigo ba se dai na ga missed call kuma tabbas na ga an kikkira ni da number waje amma ban san ita ba ce shiyasa ban bi baya ba. Jin muna yin sallama Bilal ya raɗa mun a kunne wai na yi masa godiya, ban san godiyar ta me ce ce ba amma haka na yi ya ce ba komai daga nan na mayar masa da wayar sa na fita bayan na sanar masa ga abinci can yana jiran sa.
Na zata ba ze zo ya ci ba ganin kusan minti goma har na fara gyangyaɗi kafin ya shigo. Farat farat ba zaka ce shi ya gama gasa mun maganganu jiya da daddare ba wai har yana tambaya ta ya taro an ce masa an sha bidiri a gidan nan. Na yi murmushi kawai ina kallon sa yana cin abincin yana soko mun hira, a raina na raya kenan su Fadila ba wani abu ya sa suka tafi ba tare da mun yi sallama ba ko kuma dai labarin bai iso kunnen sa ba ne. Da ya gama ci naga alamar yana so ya ja hirar da tsayi na ce masa bacci nake ji, na ringa kallon sa da mamaki jin ya ce na karanto masa account number na ya samu wasu kuɗi ni ma zai tura mun wani abu.
Na gama karanta masa ya saka muka yi sallama yana shirin rungume ni na zille na shige ɗaki, na goge ido na ya fi sau nawa a son na tabbatar da gaske kuɗin da na gani haka suke ko kuwa dai ban ga ni da kyau bane ba. Dubu ɗari Bilal ya aika mun, dubu ɗari dai a tarihin rayuwa ta da shi tun da muke dunƙulalliyar dubu goma bai taɓa ɗauka ya bani ba idan ba ta siyan kayan barka ba.
Duk baccin da nake ji sai na ji na wartsake, na rasa ma wacce kalar murna zanyi. Screenshot na yi na turawa Anty Labiba, kafin su tafi ba kalar habaicin da bata mun ba ace haihuwar fari amma abincin da za'a ci na suna se dai a dafo daga gidan ubana a kawo mun kuma a haka dan bani da kunya na cigaba da yi musu kankanba ni me miji kuma yana so na ai ko auren haɗi ba za'a kwata abinda aka mun ba.
Ni dai abin da na ke raya wa a zuciya ta Bilal na so na, duk kuma abin da a ke ganin ba ya mun da ma ce ba shi da ita ina kuma da yaƙinin wata rana zai mun ninkin abin da ma ba'a taɓa tsammata ba gashi kuwa ya fara tabbatar da hasashe na. Bacci ma kusan rabi da rabi na yi, bini bini zan farka na ja waya na duna dan in tabbatar kuɗin na nan ba su gudu ba.
GIDAN HAJJA
Tun safe suka ta shi da kacaniyar taron sunan da suka shirya zasu yi a can gidan. Ita ta ƙarfafawa Bilal akan ba wani taron suna da Halima za tayi in dai ba can gidan su zata tafi suyi a can ba, daga baya kuma ta rikiɗa ta ce ita zata yi taro a nan gidan ta, jikan ta na farko na ɗa namiji bai kamata ace ba a yi taron suna ba. Da Anty Amina ta ce mata in dai ba Halima za'a bawa kuɗi ta yi taro ba se dai a haƙura haka ta ringa faɗa ta na cewa ita ta kasa ganewa Amina, gaba ɗaya ta canza yi ta ke ma yanzu kamar Halima ce yar uwar ta ba Bilal ba to ba za'a bata ɗin ba idan ta na so ta fitar da kuɗin ta tayi taron nan itama da Fadila ta haihu ai babu ƙwandalar kowa su suka yi taron sunan su.
Da Bilal ɗin ya ce mata ba shi da kuɗi yanzu na Rago ya ke ƙoƙarin haɗawa ma ce masa ta yi ita ba damuwar ta ba ne wannan idan ya so ma ya bari se ranar sati biyu sannan ya yi musu yankan. Haka nan se da ya basu kuɗin kafin ya samu lafiya a hannun Hajjan. Da safe kuma bayan an gama raɗin suna bayan da ya je banki ya tarar da Hafiz ya aika masa saƙon da ya girgiza masa lissafi. Ya san tabbas ze yi masa abu na bajinta domin Hafiz akwai harkar girma amma be zata abun ze kai har haka ba. Babu bata lokaci ya Abubakar ya ce ya zo ya karɓi kuɗi ya siyo Ragon shi kuma ya wuce wani uzuri.
"Za'a kai yanzu" ta sake bata amsa. Ta ke na ji sanyi a raina na waske na bar gurin ba tare da na ce mata komai ba duk da a ƙasan raina na ji kamar na tsaya na ɗibarwa Bilal ban sani ba ko ze bawa su Nasir da sauran abokanan sa na unguwa amma na san zata iya saka kaina a kular abincin shiyasa na haƙura ban koma ba. Se da aka kira Magriba taro ya fara watsewa, na samu alkhairi ƙwarai da gaske Abba ma ya yi goshi daga kan riguna kuɗi da kayan amfani su diaper da omon wanki da su sabulu mun same su babu adadi zamu ja lokaci sosai kafin su ƙare mana.
Tun da naji za'a kaiwa su Fadila abinci ban sake bi ta kan su ba musamman da ƙawaye na da mu kayi poly tare suka zo duk hankali na ya tafi ga maƙwafta masu shigowa da sauran yan uwa gaba ɗaya na sha'afa da su sai da su Baby Bashir zasu tafi na fito raka su kafin ido na ya sauka kan ƙofar ɗakin Bilal ɗin da na hango yara na tsere a ciki. Gaba ɗaya se na rasa nutsuwa, get na yi niyar taka musu amma na tsaya daga in da nake na bar su da Hansa'u ta tafi raka su wajen ni kuma na wuce ɗakin Bilal. Babu kowa sai yara dake wasa da wasu yan gidan su Abban mu yammata suna ɗaukar hoto. Ce musi na yi su fita na kullo ƙofar dan key ɗin ma a jiki suka bar shi na jefa shi cikin aljihun rigata zuciya ta na bubbugawa dan na san har dai zasu tafi ba tare da sun yi mun sallama ba tabbas da wuya idan ba Anty ta musu wani abun da ya sosa musu rai ba ne. Haushin kai na ya kama ni, ko me ya sa ban tsaya na ga abincin da ta zuba musu ba ko kuma na sake komawa gurin su na tabbatar an basu komai wadatacce, bana ma zaton ta basu souvenirs ɗin da naga ta bawa ƙawaye na da suka tafi yanzu ƙila ko daga baya aka kawo su.
Haka dai jama'a suka ida watsewa ya rage na jiki waɗanda suka tsaya suka gyara mun gida tsaf ba zaka ce anan aka sha didimar biki ba, abincin da yayi saura da yawa masu so sun ɗiba sun tafi da shi, ta zuzzuba mun abinda ze ajiyu na saka a fridge miya kuma da nama na saka a frizeer haka sauran ruwa da lemo kusan katan goma goma duk na lode su a store, basu bar gidan ba hatta kayayyakin da muka samu na barka se da suka taya ni na ware su komai ya koma muhallin sa kafin kowa ya wuce gidan sa. Ina tsaka da shafa mai bayan na watsa ruwa saboda jiki na da ya yi mun tsami sosai Bilal ya dawo.
Da Baba Jummai na jiyo suna gaisawa be shigo ɗaki na ba bayan na gama shiryawa kamar in share shi sai kuma wata zuciyar ta ce na dai je. Dama na ware masa abinci na sake ɗumamawa na haɗa komai a try na fito Baba Jummai ta bini da kallo ta na cewa
"Ba dai ɗakin sa zaki kai masa ba" na yi murmushi kaina a ƙasa dan na san baze wuce abin da ya faru jiya ya sa tayi tambayar ba se kawai na wuce na ajiye su tsakiyar falo kan center table ina cewa
"Aa, a nan zan ajiye masa"
"Ya dai fi miki" ta faɗa tana wucewa ɗaki. Fita na yi na tafi ɗakin Bilal, a falo na same shi yana waya bakin nan kamar ze tsage saboda farin ciki ina shiga ya yafito ni da hannu, ban matsa kusa da shi sosai ba na tsaya daga gefe ya miƙo mun wayar na karɓa duk da ban san waye ba sai da na kara a kunne na kafin na gane Hafiz ne.
Muka gaisa yana tambayar ina Dadyn sa tare da bani haƙuri akan rashin zuwan su wai uzuri ya taso musu basa ƙasar, ya ce Shahida ta ce idan ta kira ni bata samu na faɗa masa na yi setting layi na private ne idan ba ni da number kiran ba ze shigo ba se dai na ga missed call kuma tabbas na ga an kikkira ni da number waje amma ban san ita ba ce shiyasa ban bi baya ba. Jin muna yin sallama Bilal ya raɗa mun a kunne wai na yi masa godiya, ban san godiyar ta me ce ce ba amma haka na yi ya ce ba komai daga nan na mayar masa da wayar sa na fita bayan na sanar masa ga abinci can yana jiran sa.
Na zata ba ze zo ya ci ba ganin kusan minti goma har na fara gyangyaɗi kafin ya shigo. Farat farat ba zaka ce shi ya gama gasa mun maganganu jiya da daddare ba wai har yana tambaya ta ya taro an ce masa an sha bidiri a gidan nan. Na yi murmushi kawai ina kallon sa yana cin abincin yana soko mun hira, a raina na raya kenan su Fadila ba wani abu ya sa suka tafi ba tare da mun yi sallama ba ko kuma dai labarin bai iso kunnen sa ba ne. Da ya gama ci naga alamar yana so ya ja hirar da tsayi na ce masa bacci nake ji, na ringa kallon sa da mamaki jin ya ce na karanto masa account number na ya samu wasu kuɗi ni ma zai tura mun wani abu.
Na gama karanta masa ya saka muka yi sallama yana shirin rungume ni na zille na shige ɗaki, na goge ido na ya fi sau nawa a son na tabbatar da gaske kuɗin da na gani haka suke ko kuwa dai ban ga ni da kyau bane ba. Dubu ɗari Bilal ya aika mun, dubu ɗari dai a tarihin rayuwa ta da shi tun da muke dunƙulalliyar dubu goma bai taɓa ɗauka ya bani ba idan ba ta siyan kayan barka ba.
Duk baccin da nake ji sai na ji na wartsake, na rasa ma wacce kalar murna zanyi. Screenshot na yi na turawa Anty Labiba, kafin su tafi ba kalar habaicin da bata mun ba ace haihuwar fari amma abincin da za'a ci na suna se dai a dafo daga gidan ubana a kawo mun kuma a haka dan bani da kunya na cigaba da yi musu kankanba ni me miji kuma yana so na ai ko auren haɗi ba za'a kwata abinda aka mun ba.
Ni dai abin da na ke raya wa a zuciya ta Bilal na so na, duk kuma abin da a ke ganin ba ya mun da ma ce ba shi da ita ina kuma da yaƙinin wata rana zai mun ninkin abin da ma ba'a taɓa tsammata ba gashi kuwa ya fara tabbatar da hasashe na. Bacci ma kusan rabi da rabi na yi, bini bini zan farka na ja waya na duna dan in tabbatar kuɗin na nan ba su gudu ba.
GIDAN HAJJA
Tun safe suka ta shi da kacaniyar taron sunan da suka shirya zasu yi a can gidan. Ita ta ƙarfafawa Bilal akan ba wani taron suna da Halima za tayi in dai ba can gidan su zata tafi suyi a can ba, daga baya kuma ta rikiɗa ta ce ita zata yi taro a nan gidan ta, jikan ta na farko na ɗa namiji bai kamata ace ba a yi taron suna ba. Da Anty Amina ta ce mata in dai ba Halima za'a bawa kuɗi ta yi taro ba se dai a haƙura haka ta ringa faɗa ta na cewa ita ta kasa ganewa Amina, gaba ɗaya ta canza yi ta ke ma yanzu kamar Halima ce yar uwar ta ba Bilal ba to ba za'a bata ɗin ba idan ta na so ta fitar da kuɗin ta tayi taron nan itama da Fadila ta haihu ai babu ƙwandalar kowa su suka yi taron sunan su.
Da Bilal ɗin ya ce mata ba shi da kuɗi yanzu na Rago ya ke ƙoƙarin haɗawa ma ce masa ta yi ita ba damuwar ta ba ne wannan idan ya so ma ya bari se ranar sati biyu sannan ya yi musu yankan. Haka nan se da ya basu kuɗin kafin ya samu lafiya a hannun Hajjan. Da safe kuma bayan an gama raɗin suna bayan da ya je banki ya tarar da Hafiz ya aika masa saƙon da ya girgiza masa lissafi. Ya san tabbas ze yi masa abu na bajinta domin Hafiz akwai harkar girma amma be zata abun ze kai har haka ba. Babu bata lokaci ya Abubakar ya ce ya zo ya karɓi kuɗi ya siyo Ragon shi kuma ya wuce wani uzuri.