Sashe 52
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amma Bilal na haihu ka kasa zuwa, Abba na ya kira ka nima na kira ka kuma na san ko ba'a faɗa maka ba ba zaka kasa jin labari a unguwa ba" na faɗa cikin shassheƙa. Ya sake rungume ni yace
"Na ga kiran Abba Halima; nayi zaton ƙarata kika kai akan abin da na yi wa Amirah shi ya sa na kasa ɗagawa. San da naga saƙon sa na kin haihu a lokacin dare yayi sosai, na so na bari se da safe na zo amma na kasa jurewa. Tunanin halin da kike ciki da kuma taraddadin kin haihu ko akasin haka yasa na kasa jurewa. Ban san me ya faru ba, nayan na fito daga gida wasu suka tare ni daga nan ban sake gane kai na ba kawai na tashi na ganni a asibiti kuma duk ƙoƙarin da na yi akan nayi magana na kasa. Se daga baya na samu labarin wasu ne suka tsince ni suka kaini asibitin" yayi maganar ba tare da ya bari mun haɗa ido ba.
Wani irin tausayin sa ne ya lulluɓe ni, ni dama na san Bilal baze wofantar dani haka kawai ba, ashe abin da ya same shi kenan. Kuka sosai na fashe dashi da wani tunani ya ɗarsu a raina. Yanzu da ace kuma Bilal ya rasa ransa ne fa ina zan sa kaina a duniyar nan naji sanyi?
Rungume ni yayi ina jin ɗumin hawayen sa a dokin wuya na ya ce
"Ki yafe mun Halima, ba da gayya bane".
Mun shafe kusan minti goma muna koke koken har se da yaron ya gaji da matsar da aka masa ya fara kuka kafin ya sake ni na karɓe shi daga hannun sa na shiga jijjiga shi yaƙi shiru dole se da na shiga shayar dashi kafin yayi shirun alamar har da yunwa ta dame shi. Se bayan da ya ƙoshi ya sake karɓar sa yana kallo na yace
"Da ni yake kama, hancin sa ne kawai irin na ki".
Shafa hanci na nayi ina murmushi na ce
"Irin na ka dai, ai ban kai ka hanci ba"
"Amma na so ace dake yayi kama se ya fi kyau" ya faɗa yana kwantar da yaron a jikin sa. Na buɗe ido ina dariya na ce "Haba dai, ka fito fili kawai kace da baze ganu ba"
"Allah da gaske na keyi ke kyakkyawa ce Halima. Kina da kyau me sanyi irin wanda a duk kallo yake ƙara ƙawata idanuwan me kallon ki; babbar ni'imar da ubangiji ya yi miki ita ce kyakkyawar zuciya, kin ga ko kwatantan kyawun ki da nawa ma ai ɓata baki ne kawai. Ina addu'ar yanda yaron nan yayi kama ta zahiri da ni, ya yi kama dake ta baɗini" Bilal ya faɗa yana kafe ni da ido. Murmushi na ringa yi kamar wawuya. Ina kallon sa ya ɗago yaron bayan ya tashi zaune sosai ya shiga yi masa kiran sallah a kunnen sa. Se da ya kammala kafin ya kalle ni ya ce
"Wane suna kike so a saka masa?"
Nayi ƙasa da kaina ina murmushi, idan son rai na ne bani da zaɓin daya wuce sunan Abba na, amma na san ƙila a ransa ze zo ya mayar da sunan mahaifin sa ne tun da ya rasu. Hakan ya sa na ce masa
"Duk sunan da yayi maka shi ne zaɓi na". Murmushi me kyau yayi mun kafin ya kammala masa huɗubar kafin ya miƙo mun shi yana cewa
"Allah ya raya Muhammad Al'amin"
"Abba na?" Na faɗa cikin tsananin murna. Ya ɗaga mun kai ya ce
"Na daɗe da sanin burin ki na sakawa yaron ki na fari sunan Abba, ko kin manta kin sha faɗa mun kafin mu yi aure?"
Rungume shi na yi ina cewa
"Na gode Bilal, na gode ƙwarai da wannan karar da kayi mun"
"Ni ne da godiya Halima kin yi mun abubuwa da dama a rayuwa da bazan iya biyan ki ba. Naji daɗi da kika yi farin ciki, Allah ya raya mana shi ya sa ya gaji takwaran sa"
Da "Amin" na amsa ina sake rungume Abba na a jiki na. Badan dare yayi ba da yanzu zan kira Abba na gaya masa ya samu takwara amma Allah ya kaimu safiya.
A ɗakin muka kwana rungume da juna cikin farin cikin da muka kwana biyu bamu samu kamar sa ba. Hatta Abba na be yi koke koken da yake mana kwanaki ukun zuwan sa duniya ba da safe har Anty Amina se da ta ringa masa tsiya wai ya ji ɗumin Dady yayi lif kamar babu jinjiri a gidan.
*******
A hanyar komawa gida Mama Fauziyya ta kalli Anty Labiba ta ce
"Allah sarki Bilal, ashe abin da ya same shi kenan duk mun ɗauki alhakin sa mun zata wulaƙanta yarinyar nan kawai ya so yi". Anty Mimi ta ce
"Wlh fa Anty, ni ma duk se jiki na yayi sanyi tun da muka shiga, ana kallon sa zaka gane yaji jiki wlh. Kamar fa harda ɗinki na gani a gefen kan sa, gaskiya ya daku sosai da alama".
"Amma dai kun bani mamaki wlh, ku yanzu har kun kama ƙaryar waɗancan mutanen kenan?" Anty Labiba ta faɗa se Mama Fauziyya ta ce
"Aa Labiba, wannan fa ba zancen ƙarya bane. Idan sun yi ƙarya akan ainihin abin da ya same shi wannan daban amma a zahiri dai duk wanda ya kalle shi yasan wani abu na rashin daɗi ya faru dashi, gaskiyar me ya faru kuma wannan se Allah. Kuma dama karki kuskura ki ce zaki sake zuga Yaya akan maganar Halima, dan Allah ki bari yarinyar nan ta dawo gida dan ganin idon ki dai gashi abinci ma babu a gidan yini guda jegon kwana uku amma ace sun kasa samar mata abin da zata ci da jikin ta yake buƙata ina ga an sake kwana biyu? Gara ta taho tayi arba'in se ta koma".
Shiru Anty Labiba tayi bata ce komai ba, ita ta san halin Bilal ko da yanayin sa ya nuna da gaske bashi da lafiya amma a yanda ta sanshi ba wani abun mamaki bane ace shirya wa yayi. Duk se da ta sauke su a gida tunda a motar ta suka fita kafin ta wuce nata gidan, a hanya ta kira Mama taji ko Zainab ɗin ta tafi Maman tace mata aa, Haliman tace mata Yayar Bilal da mahaifiyar sa suna gidan shi yasa ta dakata da tura Zainab ɗin kar kuma suyi yawa. Idan sun tafi se taje in ma kuma su zasu zauna mata shikenan daga nan sukayi sallama akan se washe gari zata je gidan su ƙarasa magana akan yanda za'ayi da kayan barka.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 22*
"Dagaske ne Anty, masu ƙwacen mashin ne suka bige shi; waɗan da suka kai shi asibitin ma na san ɗaya daga cikin su tare muka fara Maitama Sule" Mu'azzam ya faɗa jin Anty Labiba ta dage akan ƙarya kawai Bilal ya shirga ba wani abu daya same shi. Zuwan ta kenan ta tarar suna jimamin abun, Na kira Abba na gaya masa an masa takwara sannan na ƙara da faɗa masa dalilin da ya saka Bilal be duba mu ba har na bawa Bilal ɗin waya suka gaisa da Abban ya sake bashi haƙuri. Bayan mun gama wayar ne ya fito yake gaya wa Mama yan da mu ka yi se ga Anty Labiban.
"Ƙarya ya ke yi, saboda maganar ma bata kama kunne na ba shi yasa tun jiyan ban faɗa miki ba, na ɗauka ma su Yaya Fauziyya zasu gaya miki tun da naga se jiman ta abun suke yi. Haɗin baki ne kawai shi da yan uwan sa saboda su goge laifin wofantar da Halima da suka yi" ta faɗa sanda Mama ta maimaita mata abin da Abban ya gaya mata.
"Yanzu kai ka san haka ta faru da shi amma shi ne ka yi shiru baka faɗawa kowa ba?" Abba ya faɗa yana kallon sa, se ya yi ƙasa da kai ya ce
"Ni ma ai se daga baya na sani Abba. Lokacin da muka mayar da ita gida bayan na dawo aboki na Najib ya kira ni yake gaya mun masu ƙwacen mashin sun bige mai gidan da yaga mota ta a gurin kuma su suka kai shi asibiti ma".
"Ikon Allah, toh Allah ya rufa asiri. Amma wasu irin mutane ne su da irin haka zata faru ba zasu sanar mana ba tun da ai yanzu mun zama abu guda?" Abban ya sake faɗa. Anty Labiba da ta zabga wa Mu'azzam harara ta ce
"In ma da gaske ne ba komai ya ja masa ba illah haƙƙin iyalin sa da baya saukewa kaga an wasu can a banza sun ƙwata ta ƙarfi ai, Allah ya ƙara"
"Haba Labiba ya kuma da irin wannan maganar? Idan da abun ya zo da tsautsayi fa suka hallaka shi ko suka masa wata illar da za'a gwammaci ma mutuwa ya yi fa? Wannan al'amari na masu ƙwacen waya da mashin dai ya fara yawa se dai fatan Allah ya shirye su kawai" Mama ta faɗa cikin jimami.
"Bari na gani idan na fita se mu biya mu duba shi" Abba ya faɗa yana miƙewa, kafin ya zaro kuɗi a aljihun sa ya miƙawa Anty Labiba yana cewa
"Gashi se ku ƙara kayan, kin san yanzu lissafi ya canza aboki ne kuma takwara. Ke ma ya kama ta ki ware akwatin ki daban; idan kuma kin barwa su Fauziyya auren shikenan" ya ƙarasa cikin sigar raha. Ta karɓi kuɗin ta na ɗan murmushi Mama kuma ta taka masa zuwa gurin mota.
"Na ga kiran Abba Halima; nayi zaton ƙarata kika kai akan abin da na yi wa Amirah shi ya sa na kasa ɗagawa. San da naga saƙon sa na kin haihu a lokacin dare yayi sosai, na so na bari se da safe na zo amma na kasa jurewa. Tunanin halin da kike ciki da kuma taraddadin kin haihu ko akasin haka yasa na kasa jurewa. Ban san me ya faru ba, nayan na fito daga gida wasu suka tare ni daga nan ban sake gane kai na ba kawai na tashi na ganni a asibiti kuma duk ƙoƙarin da na yi akan nayi magana na kasa. Se daga baya na samu labarin wasu ne suka tsince ni suka kaini asibitin" yayi maganar ba tare da ya bari mun haɗa ido ba.
Wani irin tausayin sa ne ya lulluɓe ni, ni dama na san Bilal baze wofantar dani haka kawai ba, ashe abin da ya same shi kenan. Kuka sosai na fashe dashi da wani tunani ya ɗarsu a raina. Yanzu da ace kuma Bilal ya rasa ransa ne fa ina zan sa kaina a duniyar nan naji sanyi?
Rungume ni yayi ina jin ɗumin hawayen sa a dokin wuya na ya ce
"Ki yafe mun Halima, ba da gayya bane".
Mun shafe kusan minti goma muna koke koken har se da yaron ya gaji da matsar da aka masa ya fara kuka kafin ya sake ni na karɓe shi daga hannun sa na shiga jijjiga shi yaƙi shiru dole se da na shiga shayar dashi kafin yayi shirun alamar har da yunwa ta dame shi. Se bayan da ya ƙoshi ya sake karɓar sa yana kallo na yace
"Da ni yake kama, hancin sa ne kawai irin na ki".
Shafa hanci na nayi ina murmushi na ce
"Irin na ka dai, ai ban kai ka hanci ba"
"Amma na so ace dake yayi kama se ya fi kyau" ya faɗa yana kwantar da yaron a jikin sa. Na buɗe ido ina dariya na ce "Haba dai, ka fito fili kawai kace da baze ganu ba"
"Allah da gaske na keyi ke kyakkyawa ce Halima. Kina da kyau me sanyi irin wanda a duk kallo yake ƙara ƙawata idanuwan me kallon ki; babbar ni'imar da ubangiji ya yi miki ita ce kyakkyawar zuciya, kin ga ko kwatantan kyawun ki da nawa ma ai ɓata baki ne kawai. Ina addu'ar yanda yaron nan yayi kama ta zahiri da ni, ya yi kama dake ta baɗini" Bilal ya faɗa yana kafe ni da ido. Murmushi na ringa yi kamar wawuya. Ina kallon sa ya ɗago yaron bayan ya tashi zaune sosai ya shiga yi masa kiran sallah a kunnen sa. Se da ya kammala kafin ya kalle ni ya ce
"Wane suna kike so a saka masa?"
Nayi ƙasa da kaina ina murmushi, idan son rai na ne bani da zaɓin daya wuce sunan Abba na, amma na san ƙila a ransa ze zo ya mayar da sunan mahaifin sa ne tun da ya rasu. Hakan ya sa na ce masa
"Duk sunan da yayi maka shi ne zaɓi na". Murmushi me kyau yayi mun kafin ya kammala masa huɗubar kafin ya miƙo mun shi yana cewa
"Allah ya raya Muhammad Al'amin"
"Abba na?" Na faɗa cikin tsananin murna. Ya ɗaga mun kai ya ce
"Na daɗe da sanin burin ki na sakawa yaron ki na fari sunan Abba, ko kin manta kin sha faɗa mun kafin mu yi aure?"
Rungume shi na yi ina cewa
"Na gode Bilal, na gode ƙwarai da wannan karar da kayi mun"
"Ni ne da godiya Halima kin yi mun abubuwa da dama a rayuwa da bazan iya biyan ki ba. Naji daɗi da kika yi farin ciki, Allah ya raya mana shi ya sa ya gaji takwaran sa"
Da "Amin" na amsa ina sake rungume Abba na a jiki na. Badan dare yayi ba da yanzu zan kira Abba na gaya masa ya samu takwara amma Allah ya kaimu safiya.
A ɗakin muka kwana rungume da juna cikin farin cikin da muka kwana biyu bamu samu kamar sa ba. Hatta Abba na be yi koke koken da yake mana kwanaki ukun zuwan sa duniya ba da safe har Anty Amina se da ta ringa masa tsiya wai ya ji ɗumin Dady yayi lif kamar babu jinjiri a gidan.
*******
A hanyar komawa gida Mama Fauziyya ta kalli Anty Labiba ta ce
"Allah sarki Bilal, ashe abin da ya same shi kenan duk mun ɗauki alhakin sa mun zata wulaƙanta yarinyar nan kawai ya so yi". Anty Mimi ta ce
"Wlh fa Anty, ni ma duk se jiki na yayi sanyi tun da muka shiga, ana kallon sa zaka gane yaji jiki wlh. Kamar fa harda ɗinki na gani a gefen kan sa, gaskiya ya daku sosai da alama".
"Amma dai kun bani mamaki wlh, ku yanzu har kun kama ƙaryar waɗancan mutanen kenan?" Anty Labiba ta faɗa se Mama Fauziyya ta ce
"Aa Labiba, wannan fa ba zancen ƙarya bane. Idan sun yi ƙarya akan ainihin abin da ya same shi wannan daban amma a zahiri dai duk wanda ya kalle shi yasan wani abu na rashin daɗi ya faru dashi, gaskiyar me ya faru kuma wannan se Allah. Kuma dama karki kuskura ki ce zaki sake zuga Yaya akan maganar Halima, dan Allah ki bari yarinyar nan ta dawo gida dan ganin idon ki dai gashi abinci ma babu a gidan yini guda jegon kwana uku amma ace sun kasa samar mata abin da zata ci da jikin ta yake buƙata ina ga an sake kwana biyu? Gara ta taho tayi arba'in se ta koma".
Shiru Anty Labiba tayi bata ce komai ba, ita ta san halin Bilal ko da yanayin sa ya nuna da gaske bashi da lafiya amma a yanda ta sanshi ba wani abun mamaki bane ace shirya wa yayi. Duk se da ta sauke su a gida tunda a motar ta suka fita kafin ta wuce nata gidan, a hanya ta kira Mama taji ko Zainab ɗin ta tafi Maman tace mata aa, Haliman tace mata Yayar Bilal da mahaifiyar sa suna gidan shi yasa ta dakata da tura Zainab ɗin kar kuma suyi yawa. Idan sun tafi se taje in ma kuma su zasu zauna mata shikenan daga nan sukayi sallama akan se washe gari zata je gidan su ƙarasa magana akan yanda za'ayi da kayan barka.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 22*
"Dagaske ne Anty, masu ƙwacen mashin ne suka bige shi; waɗan da suka kai shi asibitin ma na san ɗaya daga cikin su tare muka fara Maitama Sule" Mu'azzam ya faɗa jin Anty Labiba ta dage akan ƙarya kawai Bilal ya shirga ba wani abu daya same shi. Zuwan ta kenan ta tarar suna jimamin abun, Na kira Abba na gaya masa an masa takwara sannan na ƙara da faɗa masa dalilin da ya saka Bilal be duba mu ba har na bawa Bilal ɗin waya suka gaisa da Abban ya sake bashi haƙuri. Bayan mun gama wayar ne ya fito yake gaya wa Mama yan da mu ka yi se ga Anty Labiban.
"Ƙarya ya ke yi, saboda maganar ma bata kama kunne na ba shi yasa tun jiyan ban faɗa miki ba, na ɗauka ma su Yaya Fauziyya zasu gaya miki tun da naga se jiman ta abun suke yi. Haɗin baki ne kawai shi da yan uwan sa saboda su goge laifin wofantar da Halima da suka yi" ta faɗa sanda Mama ta maimaita mata abin da Abban ya gaya mata.
"Yanzu kai ka san haka ta faru da shi amma shi ne ka yi shiru baka faɗawa kowa ba?" Abba ya faɗa yana kallon sa, se ya yi ƙasa da kai ya ce
"Ni ma ai se daga baya na sani Abba. Lokacin da muka mayar da ita gida bayan na dawo aboki na Najib ya kira ni yake gaya mun masu ƙwacen mashin sun bige mai gidan da yaga mota ta a gurin kuma su suka kai shi asibiti ma".
"Ikon Allah, toh Allah ya rufa asiri. Amma wasu irin mutane ne su da irin haka zata faru ba zasu sanar mana ba tun da ai yanzu mun zama abu guda?" Abban ya sake faɗa. Anty Labiba da ta zabga wa Mu'azzam harara ta ce
"In ma da gaske ne ba komai ya ja masa ba illah haƙƙin iyalin sa da baya saukewa kaga an wasu can a banza sun ƙwata ta ƙarfi ai, Allah ya ƙara"
"Haba Labiba ya kuma da irin wannan maganar? Idan da abun ya zo da tsautsayi fa suka hallaka shi ko suka masa wata illar da za'a gwammaci ma mutuwa ya yi fa? Wannan al'amari na masu ƙwacen waya da mashin dai ya fara yawa se dai fatan Allah ya shirye su kawai" Mama ta faɗa cikin jimami.
"Bari na gani idan na fita se mu biya mu duba shi" Abba ya faɗa yana miƙewa, kafin ya zaro kuɗi a aljihun sa ya miƙawa Anty Labiba yana cewa
"Gashi se ku ƙara kayan, kin san yanzu lissafi ya canza aboki ne kuma takwara. Ke ma ya kama ta ki ware akwatin ki daban; idan kuma kin barwa su Fauziyya auren shikenan" ya ƙarasa cikin sigar raha. Ta karɓi kuɗin ta na ɗan murmushi Mama kuma ta taka masa zuwa gurin mota.