Sashe 30
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Tsabar baki da mutunchi baki san darajar kuɗi ba shine zakiyi amai akan abin da za a ci kuma ba kunya ba tsoron Allah kike gaya mun kin zubar kifin dubu biyun kina zuba mun a shara, to wlh idan kin saba ɓarnatar da abinci a gidan ku saboda sangarta ba a ce miki komai ni a nan ba zan ɗauka ba dan ba sato kuɗin nake ba da gumi na nake neman su. Kin haramta kifi kin zubar sannan kin mun asarar hypo roba guda da abun wanke wanke to wlh bazan ɗauka ba ki kuma kwana da sanin se kinyi nadamar abin da kika yi" ya ja tsaki kamar ze katse harshen sa kafin ya buga murfin freezer ya wuce ni yana cewa
"Aikin banza kawai mace babu abinda ta sani se taci ta kwanta ta ɓarnatar maka da abinci".
[1/13, 7:33 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*Page 13*
Kasaƙe nayi ina kallon sa har ya fice daga kitchen ɗin lokaci ɗaya jiki na yayi sanyi lanƙwas kamar an watsa mun ruwan sanyi. A hankali na ajiye bowl ɗin hannu na na dafe drawer baya na da hannu biyu jin jiri na neman ɗiba ta. "Sam wannan ba Bilal bane, ba halin sa bane akwai wani abu da yake damun sa tabbas" abin da na furta a fili kenan cikin son ƙarfafawa kaina guiwa da kuma bawa kaina tabbacin ba cikin sani Bilal yayi mun wannan tozarcin ba. Nafi minti biyar kafin na tattara ƙarfin daya rage mun na bi bayansa zuciyata na ƙarfafa ni da naje naji me ya same shi? A bakin ƙofar ɗakin na ci burki na kasa shiga saboda yanda zuciya ta take bugawa fat fat. Ba zan iya jurewa ya sake gaya mun wasu maganganun ba zuciya ta zata iya bugawa amma kuma ina da buƙatar sanin me yake damun sa? Waye ya tunzuro shi haka ko ma im ce wasu shaiɗanu ne suka shafe shi?.
Ina kama hannun ƙofar aka buɗe daga ciki, mukayi ido huɗu ya jefe ni da kallon da na kasa mantawa kafin ya ja tsaki kamar ze ture ni ya fice, daga in da nake na jiyo yanda ya buga ƙofar get. A nan gurin na sulale na zura kaina cikin cinyoyi na se dai hawaye ko ɗis be zubo mun ba zuciyata ce kaɗai take suya wani abu me ɗaci da maƙaƙi na yawo cikin maƙoshi na. Nafi minti ashirin a zaune a gurin kamar ma ba a duniyar nake ba, kalaman Bilal na mun amsa kuwwa tamkar a lokacin yake faɗa mun su. Jin ana kiran wayata a karo na uku yasa na yunƙura daƙyar na tashi, Mama ce take kira na, na san har idan na amsa tilas zata fahimci halin da nake ciki hakan yasa na mayar da wayar na ajiye na kwanta akan kujera.
A nan na wuni sur sallah kaɗai ke tayar dani gaba ɗaya ji nayi duniyar tayi mun duhu komai ya haɗe mun na kuma rasa ta ina zan fara gyarota, wa zan kira na faɗa masa matsala ta? Ban san me yasa sam naji na kasa kiran Anty Labiba ba dukda ita ta fara zuwar mun se kuma Hansa'u amma duk su biyu dana tuna basa son Bilal se naji be kamata na kai kuka na kan abin da ya shafe su gurin sa ba daga ƙarshe na yanke shawarar na shanye ɓacin raina ni kaɗai tun da dama cikin nasihohin da aka mun an jaddada mun muhimmancin riƙe sirrin gidan aure na.
Rashin cin abinci da ɓacin ran da nake ciki suka haifar mun da ciwon kai da ciwon ciki me tsanani. Shida saura Bilal ya dawo, sama sama nake jiyo muryar sa da alama waya yakeyi yana ta raha amma dana ɗaga kai bayan daya turo ƙofa ya shigo gani nayi ya haɗe rai tamkar be taɓa dariya a rayuwar sa ba. Tsayuwa yayi a kaina yana kallo na, nayi kamar bacci nakeyi ina jin sa ya saki tsaki kafin ya wuce yana ƙunƙuni se na bishi da kallo hawaye na gangarowa ta gefen ido na, kitchen ya shige, daga can naji ya fara kiran suna na ban amsa ba se gyara kwanciya da nayi na bada baya ina goge hawayen da suka ɓalle mun.
"Wato baki ma ɗora mun abin shan ruwa ba ko? Na lura nema na kike yi da fiti na Halima. Iya asarar da kika mun bata ishe ki ha yanzu kuma hora ni kike so kiyi da yunwa ko? shikenan kiyi yanda kika so" ya faɗa ni dai ban juyo ba ya wuce ɗaki be ɗauki lokaci ba ya fito ya sake shiga kitchen ina jin sa yana haɗa tukwane yana gwarawa ƙarar tana shigar mun har tsakiyar kai. Ina kwance a gurin aka kira sallah na yunƙura na tashi da ƙyar ina dafe da kaina ga ciki na daya fara yamutsawa dalilin ƙamshin suyar ƙwai daya fara tasowa daga kitchen ɗin.
A hankali na kalli Bilal ya fito daga kitchen da plate me ɗauke da ƙwai da cup ɗin shayi. Kan center table ya ajiye su ya wuce cikin ɗaki, ganin ƙwan da ƙamshin daya sake kusanto ni ya hautsina mun zuciya. Da ƙarfin da ban san in da na same shi ba na miƙe muka ci karo a bakin ƙofa yana shirin fitowa ni kuma zan shiga ganin yanda na tafi zan kifa ya ruƙoni kafin na ƙwace aman da nake dannewa ya fi ƙarfi na na shiga kwarara masa a jiki. Irin kallon da yake mun kaɗai naji gara ya rufe ni da masifa ko ya doke ni yafi wannan kallon. A ƙasa na kwanta ina juyi cikin aman saboda wani irin yanayi da nake ji da bazan iya fasaltawa ba. Bansan ko imani ne ya shige shi tausayi na ya kama shi ba ya tsugunna dukda kallon da yake mun wanda daga baya na fahimci na ƙyamar ƙazantar aman da nayi ne be bar fuskar sa ba ya shiga kiran sunana yana tambayata menene. Da hannu na nuna masa kaina da ciki na, tashi yayi ya cire rigar jikin sa ya ajiye a gurin sannan ya ɗauke ni, se da ya ɗauraye mun jiki da ruwan ɗumin da nake jin kamar ruwan dalma yake watsamun take zazzaɓi ya rufe ni.
Yana tsaki kamar ze katse harshen sa ya gyara gurin aman tsaf ya goge ya fesa room freshener sannan ya ɗauraye kayan sa da nawa da suka ɓaci kafin ya gama bacci ya kwashe ni ban zan ya ya ƙare ba se cikin dare na farka yunwa na neman yin ajali na. A kan center table na samu sauran jallop ɗin shinkafa daya ci ya rage na cinye na haɗa da sauran wacce na gani a tukunya sannan na fara gane kaina. Ƙarfe uku da kwata lokacin, a falo nayi sallar magriba da isha'i da banyi ba ina lazumi Bilal ya fito daga ɗaya ɗakin. Kallo ɗaya ya mun ya wuce kitchen, zuciya ta ta shigan bugawa ina jira na ji ya fara masifar abincin da naci amma naji shiru se gashi ya fito da cup da ruwan zafi ya haɗa tea a kan dining ya zauna yasha da ƙaton bread ɗin sa bayan ya gama ya koma ɗaki ya canzo kayan jikin sa ba tare da yayi mun magana ba ya tayar da sallah nan kusa da in da nake.
Ina zaune gurin ya dawo daga sallar asuba, kan kujera ya kwanta ya harɗe hannunsa biyu bayan kansa yana kallon sama, na shafa addu'a na gyara zama ina kallon sa kamar me tsoro na shiga gaishe shi. Nayi mamakin yanda ya amsa ba yabo ba fallasa har ya tambaye ni jiki na na sanar masa babu abunda yake damu na a lokacin.
"Naga dankali da doya da wasu kaya a ɗakin can" ya faɗa bayan daya tashi zaune, kaina na ƙasa na ce
"Eh, Abba ne ya aiko da su shekaran jiya"
"Shine baki faɗa mun ba?" Ya faɗa cikin sautin daya fi na farko taushi. Se na ɗaga kai na kalle shi maganganun daya yaɓa mun jiya suka shiga dawo mun take ido na ya ciko da hawaye na sadda kaina ƙasa ba tare da nace komai ba.
"Zan kwanta, idan ƙarfe bakwai tayi ban farka ba ki tashe ni" ya faɗa yana komawa cikin kujerar ya kwanta. Hakan da yayi ya nuna mun ya huce daga fushin jiyan, amma ni kuma cin mutunchin da ya mun fa? Shikenan a ganin sa komai ya wuce?
"Amma Bilal abinda ka mun jiya kana ganin ka kyauta?" Na faɗa murya ta na karyewa. Se ya tashi zaune yana kallo na yace
"Kin sani bana son dawo da abinda ya wuce karki ɓata mun rai Halima" daga haka ya miƙe ya shige ɗaki ya barni a zaune na rakashi da ido. Duk yanda naso na ƙarfafi kaina na nunawa Bilal jin zafin abin da ya mun na kasa, ganin ya sakko kawai se na lallashi zuciyata nima na haƙura. A haka azumi ya fara ja har an kai na goma. Daƙyar nayi guda huɗu saboda yanda lafiya tayi mun ƙaranci. Ciwon mara da ciwon kai suke damuna ga amai ba dama na shaƙi ƙamshin abinci ko banyi aman ba nayi ta kakari kenan. Munje chemist da Bilal suka rubutamun magungunan malaria harda allura ta kwana uku an mun amma banji sauƙi ba. Ganin lokacin al'ada ta ya wuce yasa na fara zargin ko ciki ne dani.
"Aikin banza kawai mace babu abinda ta sani se taci ta kwanta ta ɓarnatar maka da abinci".
[1/13, 7:33 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*Page 13*
Kasaƙe nayi ina kallon sa har ya fice daga kitchen ɗin lokaci ɗaya jiki na yayi sanyi lanƙwas kamar an watsa mun ruwan sanyi. A hankali na ajiye bowl ɗin hannu na na dafe drawer baya na da hannu biyu jin jiri na neman ɗiba ta. "Sam wannan ba Bilal bane, ba halin sa bane akwai wani abu da yake damun sa tabbas" abin da na furta a fili kenan cikin son ƙarfafawa kaina guiwa da kuma bawa kaina tabbacin ba cikin sani Bilal yayi mun wannan tozarcin ba. Nafi minti biyar kafin na tattara ƙarfin daya rage mun na bi bayansa zuciyata na ƙarfafa ni da naje naji me ya same shi? A bakin ƙofar ɗakin na ci burki na kasa shiga saboda yanda zuciya ta take bugawa fat fat. Ba zan iya jurewa ya sake gaya mun wasu maganganun ba zuciya ta zata iya bugawa amma kuma ina da buƙatar sanin me yake damun sa? Waye ya tunzuro shi haka ko ma im ce wasu shaiɗanu ne suka shafe shi?.
Ina kama hannun ƙofar aka buɗe daga ciki, mukayi ido huɗu ya jefe ni da kallon da na kasa mantawa kafin ya ja tsaki kamar ze ture ni ya fice, daga in da nake na jiyo yanda ya buga ƙofar get. A nan gurin na sulale na zura kaina cikin cinyoyi na se dai hawaye ko ɗis be zubo mun ba zuciyata ce kaɗai take suya wani abu me ɗaci da maƙaƙi na yawo cikin maƙoshi na. Nafi minti ashirin a zaune a gurin kamar ma ba a duniyar nake ba, kalaman Bilal na mun amsa kuwwa tamkar a lokacin yake faɗa mun su. Jin ana kiran wayata a karo na uku yasa na yunƙura daƙyar na tashi, Mama ce take kira na, na san har idan na amsa tilas zata fahimci halin da nake ciki hakan yasa na mayar da wayar na ajiye na kwanta akan kujera.
A nan na wuni sur sallah kaɗai ke tayar dani gaba ɗaya ji nayi duniyar tayi mun duhu komai ya haɗe mun na kuma rasa ta ina zan fara gyarota, wa zan kira na faɗa masa matsala ta? Ban san me yasa sam naji na kasa kiran Anty Labiba ba dukda ita ta fara zuwar mun se kuma Hansa'u amma duk su biyu dana tuna basa son Bilal se naji be kamata na kai kuka na kan abin da ya shafe su gurin sa ba daga ƙarshe na yanke shawarar na shanye ɓacin raina ni kaɗai tun da dama cikin nasihohin da aka mun an jaddada mun muhimmancin riƙe sirrin gidan aure na.
Rashin cin abinci da ɓacin ran da nake ciki suka haifar mun da ciwon kai da ciwon ciki me tsanani. Shida saura Bilal ya dawo, sama sama nake jiyo muryar sa da alama waya yakeyi yana ta raha amma dana ɗaga kai bayan daya turo ƙofa ya shigo gani nayi ya haɗe rai tamkar be taɓa dariya a rayuwar sa ba. Tsayuwa yayi a kaina yana kallo na, nayi kamar bacci nakeyi ina jin sa ya saki tsaki kafin ya wuce yana ƙunƙuni se na bishi da kallo hawaye na gangarowa ta gefen ido na, kitchen ya shige, daga can naji ya fara kiran suna na ban amsa ba se gyara kwanciya da nayi na bada baya ina goge hawayen da suka ɓalle mun.
"Wato baki ma ɗora mun abin shan ruwa ba ko? Na lura nema na kike yi da fiti na Halima. Iya asarar da kika mun bata ishe ki ha yanzu kuma hora ni kike so kiyi da yunwa ko? shikenan kiyi yanda kika so" ya faɗa ni dai ban juyo ba ya wuce ɗaki be ɗauki lokaci ba ya fito ya sake shiga kitchen ina jin sa yana haɗa tukwane yana gwarawa ƙarar tana shigar mun har tsakiyar kai. Ina kwance a gurin aka kira sallah na yunƙura na tashi da ƙyar ina dafe da kaina ga ciki na daya fara yamutsawa dalilin ƙamshin suyar ƙwai daya fara tasowa daga kitchen ɗin.
A hankali na kalli Bilal ya fito daga kitchen da plate me ɗauke da ƙwai da cup ɗin shayi. Kan center table ya ajiye su ya wuce cikin ɗaki, ganin ƙwan da ƙamshin daya sake kusanto ni ya hautsina mun zuciya. Da ƙarfin da ban san in da na same shi ba na miƙe muka ci karo a bakin ƙofa yana shirin fitowa ni kuma zan shiga ganin yanda na tafi zan kifa ya ruƙoni kafin na ƙwace aman da nake dannewa ya fi ƙarfi na na shiga kwarara masa a jiki. Irin kallon da yake mun kaɗai naji gara ya rufe ni da masifa ko ya doke ni yafi wannan kallon. A ƙasa na kwanta ina juyi cikin aman saboda wani irin yanayi da nake ji da bazan iya fasaltawa ba. Bansan ko imani ne ya shige shi tausayi na ya kama shi ba ya tsugunna dukda kallon da yake mun wanda daga baya na fahimci na ƙyamar ƙazantar aman da nayi ne be bar fuskar sa ba ya shiga kiran sunana yana tambayata menene. Da hannu na nuna masa kaina da ciki na, tashi yayi ya cire rigar jikin sa ya ajiye a gurin sannan ya ɗauke ni, se da ya ɗauraye mun jiki da ruwan ɗumin da nake jin kamar ruwan dalma yake watsamun take zazzaɓi ya rufe ni.
Yana tsaki kamar ze katse harshen sa ya gyara gurin aman tsaf ya goge ya fesa room freshener sannan ya ɗauraye kayan sa da nawa da suka ɓaci kafin ya gama bacci ya kwashe ni ban zan ya ya ƙare ba se cikin dare na farka yunwa na neman yin ajali na. A kan center table na samu sauran jallop ɗin shinkafa daya ci ya rage na cinye na haɗa da sauran wacce na gani a tukunya sannan na fara gane kaina. Ƙarfe uku da kwata lokacin, a falo nayi sallar magriba da isha'i da banyi ba ina lazumi Bilal ya fito daga ɗaya ɗakin. Kallo ɗaya ya mun ya wuce kitchen, zuciya ta ta shigan bugawa ina jira na ji ya fara masifar abincin da naci amma naji shiru se gashi ya fito da cup da ruwan zafi ya haɗa tea a kan dining ya zauna yasha da ƙaton bread ɗin sa bayan ya gama ya koma ɗaki ya canzo kayan jikin sa ba tare da yayi mun magana ba ya tayar da sallah nan kusa da in da nake.
Ina zaune gurin ya dawo daga sallar asuba, kan kujera ya kwanta ya harɗe hannunsa biyu bayan kansa yana kallon sama, na shafa addu'a na gyara zama ina kallon sa kamar me tsoro na shiga gaishe shi. Nayi mamakin yanda ya amsa ba yabo ba fallasa har ya tambaye ni jiki na na sanar masa babu abunda yake damu na a lokacin.
"Naga dankali da doya da wasu kaya a ɗakin can" ya faɗa bayan daya tashi zaune, kaina na ƙasa na ce
"Eh, Abba ne ya aiko da su shekaran jiya"
"Shine baki faɗa mun ba?" Ya faɗa cikin sautin daya fi na farko taushi. Se na ɗaga kai na kalle shi maganganun daya yaɓa mun jiya suka shiga dawo mun take ido na ya ciko da hawaye na sadda kaina ƙasa ba tare da nace komai ba.
"Zan kwanta, idan ƙarfe bakwai tayi ban farka ba ki tashe ni" ya faɗa yana komawa cikin kujerar ya kwanta. Hakan da yayi ya nuna mun ya huce daga fushin jiyan, amma ni kuma cin mutunchin da ya mun fa? Shikenan a ganin sa komai ya wuce?
"Amma Bilal abinda ka mun jiya kana ganin ka kyauta?" Na faɗa murya ta na karyewa. Se ya tashi zaune yana kallo na yace
"Kin sani bana son dawo da abinda ya wuce karki ɓata mun rai Halima" daga haka ya miƙe ya shige ɗaki ya barni a zaune na rakashi da ido. Duk yanda naso na ƙarfafi kaina na nunawa Bilal jin zafin abin da ya mun na kasa, ganin ya sakko kawai se na lallashi zuciyata nima na haƙura. A haka azumi ya fara ja har an kai na goma. Daƙyar nayi guda huɗu saboda yanda lafiya tayi mun ƙaranci. Ciwon mara da ciwon kai suke damuna ga amai ba dama na shaƙi ƙamshin abinci ko banyi aman ba nayi ta kakari kenan. Munje chemist da Bilal suka rubutamun magungunan malaria harda allura ta kwana uku an mun amma banji sauƙi ba. Ganin lokacin al'ada ta ya wuce yasa na fara zargin ko ciki ne dani.