Sashe 63
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wane irin bacci kike yi haka Halima sai kace wacce ta mutu kusan minti ashirin yaro a kusa da ke yana kuka amma baki farka ba".
Karɓar sa na yi na fara ƙoƙarin bashi nono amma yaƙi karɓa sai ƙara ware murya ya ke yana canyara kuka kamar wanda ake wa wani abu, tun ina lallashin sa daga zaune har na miƙe na fara jele a cikin ɗaki sai lokacin na ga ashe ƙarfe goma da rabi ma sannan ban fi awa ɗaya da kwanciya ba gaba ɗaya.
Tun Bilal na karɓar sa idan na gaji daga ƙarshe ya zare system ɗin sa daga jikin socket na ɗauka ɗaki zai kaita ya dawo shiru shiru ban ji shi ba lokacin sha biyu har ta gota na saka dogon Hijab na saɓa Al'amin a kafaɗa na bishi dan ba ze gudu ya barni ni kaɗai da rainon ɗan sa ba ga bacci da ke cin ido na kamar zan tuntsira, ina murɗa ƙofar falon na fahimci ya rufe ta da muƙulli. Bugun duniya kamar babu mai rai a ɗakin ga sauro na ta cizo na har na gaji na koma ciki ina kuka Al'amin na yi, ranar naga rayuwa ban samu sararin runtsawa ba sai ƙarfe huɗu da mintoci dan har an fara kiraye kirayen sallah a wasu masallatan.
Daƙyar na buɗe ido na da na ke jin sa kamar an watsa mun barkono, ƙwaƙwalwa ta har wani yaji yaji take mun tsabar bacci da gajiyar da ke tattare da ni. In da na kwantar da Al'amin na fara dubawa a zato na ko yanzun ma kukan yake ta yi ban ji ba irin na daren jiya amma na ganshi yana baccin sa lakadan kamar ba shi ya gama wujijjiga ni cikin dare ba. Ɗaya gefen na kalla in da Bilal ke tsaye fuska babu yabo babu fallasa, shi ya tashe ni kenan.
"Amma kin san yau Monday ko?" Ya faɗa yana kallo na. Rufe ido na nayi kafin na sake buɗewa ina ƙoƙarin tuna me za'a yi ranar Monday ɗin da yake tuna mun amma babu abin da ya zo mun a ƙwaƙwalwa ta. Ya yi tsaki ya ce
"Ki tashi ki samar mun abin da zan ci fita zan yi".
Kallon sa na yi kamar ban fahimci abin da yake nufi ba, in tashi na samar masa abin da zai ci sai ka ce bai san yanda na raba dare ina raino ba shi kuma ya kulle ƙofa ya sha baccin sa, ƙaramin tsaki na yi na juya ba tare da na bashi amsa ba na mayar da haƙarƙari na dan ni kam bacci na ke ji. Ban kai ga rufe ido na ba ya daka mun tsawar da na jita har tsakiyar kaina ta sake haɗe mun da gigitaccen kukan da Al'amin ya fasa da alama kuma tsawar Bilal ɗin ce ta tsorata shi shima.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 26*
Ko ba'a faɗa mun ba na san da wahala idan jini na bai hau ba, daƙyar na lallaɓa Al'amin ya yi shiru na goya shi kafin na fita samawa Bilal abin da zai ci. Bamu da komai da zai ciyu da safe ban da taliya. Ita na yi jollof da sauran miyar da ta rage na dafa masa baƙin shayi. Ya ringa kallon abincin kamar wanda na aje wa mugun abu kafin cikin faɗa faɗa ya shiga tambayar babu nama a gidan ne da zan dafa masa tsurar taliya ko me?
Haka na koma na ɗebo masa naman ina ajiyewa ya sake balbale ni da wata masifar wai ina kayan tea, na kalle shi kawai, sai ka ce ua siyo ya ajiye. Ciwon da kai na ya ke mun ba ze bar ni na yi doguwar magana ba Allah Allah kawai na ke yi ya fita na koma na kwanta amma naga alama shi jan magana ma yake so ya yi. Wucewa na yi na koma ɗaki na ba tare da na bashi amsar kayan shayin da ya buƙata ba, ban san ya ya ƙare ba dan bai biyo ni ba ina shiga na kwanta rubda ciki da Al'amin a baya na dan ba zan yi gangancin sauke shi ya farka na shiga uku ba. Allah ya taimake ni har ƙarfe goma muna bacci kafin ya farka, ba wai baccin ya ishe ni ba amma na rage, nauyin da kai na ya yi mun ma ya ragu.
Sauran taliyar na ɗumama na ci, babu wuta ni kuma gaskiya ba zan iya kunna ita ce ba, da ya ke garwar wankan ta mu irin wacce ake haɗawa da gwangwani ce mara nauyi sai kawai na ɗora ta akan gas, na sake goya Al'amin da yake ƙananun koke koke na shiga gyaran gidan ina gamawa ruwan ya tafasa. A bokiti na ɗiba da zummar na fara yi masa kafin nan sauran ya sarara sai na yi kar na sake ƙona kaina irin na jiya.
Duk abin da zan buƙata na ɗakko na ajiye zuciya ta cike da tsoro na zauna, a bokitin na surka ruwan na shimfiɗa towel a cikin bahon wankan yanda na ke ganin turawa a TikTok su na yi ba irin wankan da Baba Jummai ta ke yi masa ta cika baho da ruwa ta saka shi a ciki ba.
Cikin ikon Allah na masa wankan ba tare da na shaƙa masa sabulu ko ruwa a hanci ba abin da na ke tsoro, kafin na gama shirya shi ya koma bacci. Na yi hamdala, na juye sauran ruwan na yi wankan soso da sabulu kawai dan na aje wankan ganye gaskiya.
Na shirya daƙyar saboda wani irin ciwon baya da kwankwaso da suka tasar mun lokaci ɗaya kamar ba wanka na yi da ruwan zafi ba, saida na sha paracetamol sannan na kwanta baccin ni ma.
Bamu farka ba sai bayan azahar tukunna na kuma samu sauƙin gajiya da baccin da yake damuna har ciwo jikin duk na samu sauƙin su. Haka nan muka wuni ni da Al'amin mu kwanta can mu ta shi can muka sha hotuna abun mu, da yamma ma a Gas na sake ɗora ruwa na yi wanka na fesa kwalliya tun da gida ya zama namu daga ni sai miji na Baba Jummai ta tafi balle ta fara mun kwakwazo idan na yi kwalliya.
Cikin canjin hannu na na bawa almajiri ya yiwo mun cefane na yi masa sakwara da miyar agusi, a food processor na niƙa doyar tayi luƙai bayan na gama na gama komai na turare gidan da ƙamshi sannan na canzawa Al'amin kaya muka kame a falo abun mu muna jiran Dady. Sai da aka idar da sallar magriba ya shigo gidan, fuska ba yabo ba fallasa ya yi sallama na miƙe tare da Al'amin a kafaɗa ta na nufe shi ina masa sannu da zuwa. Takaddun hannun sa ya miƙa mun na karɓa shi kuma ya karɓi Al'amin ɗin na wuce ɗaki jiki a sanyaye na ajiye masa su.
Duk kwalliyar da na yi amma ko kyakkyawan kallo ban samu daga gare shi ba. Haka na wuce kitchen na ɗakko ruwa da lemo na fito, ban tarar da shi a falon ba na ajiye na leƙa ɗaki nan ma baya nan har can ɗakin sa na leƙa duk ban tarar da su ba. Tunanin ina suka shige na tsaya ina yi?
Daga tsakar gida na jiyo muryar sa da wani, na leƙa na gan su su uku sun nufo falon hakan ya sa na koma ciki da sauri na shiga ɗaki na lalubo mayafi. Mutum biyun duk ban san fuskar su ba yanayin su da harshen su ma kamar ba hausawa ba ko ma in ce ba Musulmai ba. Ya gabatar mun da su a matsayin abokanan aikin sa Patrick da Joshua sun zo ganin Al'amin.
Na haɗo ruwa da lemo na kawo musu, har zan tafi ɗaki kuma na fasa na koma kitchen ɗin na zubo nama na sake kai musu. Ban kawo komai a raina ba da irin kallon da naga Bilal ya yi mun na karɓi Al'amin da ya fara gungini nawuce ɗaki na bar su.
Shiru shiru ina jiran ya kira ni ya ce zasu tafi na ga har takwas ta yi babu alama sai ma tashar Ball da suka kunna, sakwarar da na yi bata da yawa sosai leda uku ce kawai amma akwai sauran doyar da na dafa na ga tayi yawa na saka a fridge, fito da ita na yi na mayar kan wuta ta sake tafasa kafin na niƙa ta na haɗa kayan abincin na jera musu akan dining. Daga yanda Bilal ya watso mun ido sanda na musu tayin abincin na san na kwafsa, ina kallo ya yi ƙwafa haɗi da ɗauke kai gefe. A raina na ce ikon Allah, ni a haka ma ina gudun ya ce ban karrama su ba shi yasa na ƙara yawan abincin amma naga alamar kamar laifi na yi a maimakon na yi gwaninta. Su da basu san dawar garin ba kamar dama jiran abincin suke suka tashi suka zubo, ina tsaye suka gama duk suka kwashe manyan naman cikin miyar haka dai na zubawa Bilal sauran na ɗakko ƙaramin try na ɗora masa akai na kai gaban sa na ajiye.
Indomie na koma na dafa na soya ƙwai kamar na san za'a yi haka da zan yi aiken na bada aka siyo mun na wuce ɗaki na ci. Ko sallama bamu yi da baƙin ba na dai ji sanda suke sallama da Bilal ɗin bai kira ni ba nima ban fita sai da ya kullo ƙofa ya dawo ya fara kwarara mun kira tun daga tsakar gida.
Karɓar sa na yi na fara ƙoƙarin bashi nono amma yaƙi karɓa sai ƙara ware murya ya ke yana canyara kuka kamar wanda ake wa wani abu, tun ina lallashin sa daga zaune har na miƙe na fara jele a cikin ɗaki sai lokacin na ga ashe ƙarfe goma da rabi ma sannan ban fi awa ɗaya da kwanciya ba gaba ɗaya.
Tun Bilal na karɓar sa idan na gaji daga ƙarshe ya zare system ɗin sa daga jikin socket na ɗauka ɗaki zai kaita ya dawo shiru shiru ban ji shi ba lokacin sha biyu har ta gota na saka dogon Hijab na saɓa Al'amin a kafaɗa na bishi dan ba ze gudu ya barni ni kaɗai da rainon ɗan sa ba ga bacci da ke cin ido na kamar zan tuntsira, ina murɗa ƙofar falon na fahimci ya rufe ta da muƙulli. Bugun duniya kamar babu mai rai a ɗakin ga sauro na ta cizo na har na gaji na koma ciki ina kuka Al'amin na yi, ranar naga rayuwa ban samu sararin runtsawa ba sai ƙarfe huɗu da mintoci dan har an fara kiraye kirayen sallah a wasu masallatan.
Daƙyar na buɗe ido na da na ke jin sa kamar an watsa mun barkono, ƙwaƙwalwa ta har wani yaji yaji take mun tsabar bacci da gajiyar da ke tattare da ni. In da na kwantar da Al'amin na fara dubawa a zato na ko yanzun ma kukan yake ta yi ban ji ba irin na daren jiya amma na ganshi yana baccin sa lakadan kamar ba shi ya gama wujijjiga ni cikin dare ba. Ɗaya gefen na kalla in da Bilal ke tsaye fuska babu yabo babu fallasa, shi ya tashe ni kenan.
"Amma kin san yau Monday ko?" Ya faɗa yana kallo na. Rufe ido na nayi kafin na sake buɗewa ina ƙoƙarin tuna me za'a yi ranar Monday ɗin da yake tuna mun amma babu abin da ya zo mun a ƙwaƙwalwa ta. Ya yi tsaki ya ce
"Ki tashi ki samar mun abin da zan ci fita zan yi".
Kallon sa na yi kamar ban fahimci abin da yake nufi ba, in tashi na samar masa abin da zai ci sai ka ce bai san yanda na raba dare ina raino ba shi kuma ya kulle ƙofa ya sha baccin sa, ƙaramin tsaki na yi na juya ba tare da na bashi amsa ba na mayar da haƙarƙari na dan ni kam bacci na ke ji. Ban kai ga rufe ido na ba ya daka mun tsawar da na jita har tsakiyar kaina ta sake haɗe mun da gigitaccen kukan da Al'amin ya fasa da alama kuma tsawar Bilal ɗin ce ta tsorata shi shima.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 26*
Ko ba'a faɗa mun ba na san da wahala idan jini na bai hau ba, daƙyar na lallaɓa Al'amin ya yi shiru na goya shi kafin na fita samawa Bilal abin da zai ci. Bamu da komai da zai ciyu da safe ban da taliya. Ita na yi jollof da sauran miyar da ta rage na dafa masa baƙin shayi. Ya ringa kallon abincin kamar wanda na aje wa mugun abu kafin cikin faɗa faɗa ya shiga tambayar babu nama a gidan ne da zan dafa masa tsurar taliya ko me?
Haka na koma na ɗebo masa naman ina ajiyewa ya sake balbale ni da wata masifar wai ina kayan tea, na kalle shi kawai, sai ka ce ua siyo ya ajiye. Ciwon da kai na ya ke mun ba ze bar ni na yi doguwar magana ba Allah Allah kawai na ke yi ya fita na koma na kwanta amma naga alama shi jan magana ma yake so ya yi. Wucewa na yi na koma ɗaki na ba tare da na bashi amsar kayan shayin da ya buƙata ba, ban san ya ya ƙare ba dan bai biyo ni ba ina shiga na kwanta rubda ciki da Al'amin a baya na dan ba zan yi gangancin sauke shi ya farka na shiga uku ba. Allah ya taimake ni har ƙarfe goma muna bacci kafin ya farka, ba wai baccin ya ishe ni ba amma na rage, nauyin da kai na ya yi mun ma ya ragu.
Sauran taliyar na ɗumama na ci, babu wuta ni kuma gaskiya ba zan iya kunna ita ce ba, da ya ke garwar wankan ta mu irin wacce ake haɗawa da gwangwani ce mara nauyi sai kawai na ɗora ta akan gas, na sake goya Al'amin da yake ƙananun koke koke na shiga gyaran gidan ina gamawa ruwan ya tafasa. A bokiti na ɗiba da zummar na fara yi masa kafin nan sauran ya sarara sai na yi kar na sake ƙona kaina irin na jiya.
Duk abin da zan buƙata na ɗakko na ajiye zuciya ta cike da tsoro na zauna, a bokitin na surka ruwan na shimfiɗa towel a cikin bahon wankan yanda na ke ganin turawa a TikTok su na yi ba irin wankan da Baba Jummai ta ke yi masa ta cika baho da ruwa ta saka shi a ciki ba.
Cikin ikon Allah na masa wankan ba tare da na shaƙa masa sabulu ko ruwa a hanci ba abin da na ke tsoro, kafin na gama shirya shi ya koma bacci. Na yi hamdala, na juye sauran ruwan na yi wankan soso da sabulu kawai dan na aje wankan ganye gaskiya.
Na shirya daƙyar saboda wani irin ciwon baya da kwankwaso da suka tasar mun lokaci ɗaya kamar ba wanka na yi da ruwan zafi ba, saida na sha paracetamol sannan na kwanta baccin ni ma.
Bamu farka ba sai bayan azahar tukunna na kuma samu sauƙin gajiya da baccin da yake damuna har ciwo jikin duk na samu sauƙin su. Haka nan muka wuni ni da Al'amin mu kwanta can mu ta shi can muka sha hotuna abun mu, da yamma ma a Gas na sake ɗora ruwa na yi wanka na fesa kwalliya tun da gida ya zama namu daga ni sai miji na Baba Jummai ta tafi balle ta fara mun kwakwazo idan na yi kwalliya.
Cikin canjin hannu na na bawa almajiri ya yiwo mun cefane na yi masa sakwara da miyar agusi, a food processor na niƙa doyar tayi luƙai bayan na gama na gama komai na turare gidan da ƙamshi sannan na canzawa Al'amin kaya muka kame a falo abun mu muna jiran Dady. Sai da aka idar da sallar magriba ya shigo gidan, fuska ba yabo ba fallasa ya yi sallama na miƙe tare da Al'amin a kafaɗa ta na nufe shi ina masa sannu da zuwa. Takaddun hannun sa ya miƙa mun na karɓa shi kuma ya karɓi Al'amin ɗin na wuce ɗaki jiki a sanyaye na ajiye masa su.
Duk kwalliyar da na yi amma ko kyakkyawan kallo ban samu daga gare shi ba. Haka na wuce kitchen na ɗakko ruwa da lemo na fito, ban tarar da shi a falon ba na ajiye na leƙa ɗaki nan ma baya nan har can ɗakin sa na leƙa duk ban tarar da su ba. Tunanin ina suka shige na tsaya ina yi?
Daga tsakar gida na jiyo muryar sa da wani, na leƙa na gan su su uku sun nufo falon hakan ya sa na koma ciki da sauri na shiga ɗaki na lalubo mayafi. Mutum biyun duk ban san fuskar su ba yanayin su da harshen su ma kamar ba hausawa ba ko ma in ce ba Musulmai ba. Ya gabatar mun da su a matsayin abokanan aikin sa Patrick da Joshua sun zo ganin Al'amin.
Na haɗo ruwa da lemo na kawo musu, har zan tafi ɗaki kuma na fasa na koma kitchen ɗin na zubo nama na sake kai musu. Ban kawo komai a raina ba da irin kallon da naga Bilal ya yi mun na karɓi Al'amin da ya fara gungini nawuce ɗaki na bar su.
Shiru shiru ina jiran ya kira ni ya ce zasu tafi na ga har takwas ta yi babu alama sai ma tashar Ball da suka kunna, sakwarar da na yi bata da yawa sosai leda uku ce kawai amma akwai sauran doyar da na dafa na ga tayi yawa na saka a fridge, fito da ita na yi na mayar kan wuta ta sake tafasa kafin na niƙa ta na haɗa kayan abincin na jera musu akan dining. Daga yanda Bilal ya watso mun ido sanda na musu tayin abincin na san na kwafsa, ina kallo ya yi ƙwafa haɗi da ɗauke kai gefe. A raina na ce ikon Allah, ni a haka ma ina gudun ya ce ban karrama su ba shi yasa na ƙara yawan abincin amma naga alamar kamar laifi na yi a maimakon na yi gwaninta. Su da basu san dawar garin ba kamar dama jiran abincin suke suka tashi suka zubo, ina tsaye suka gama duk suka kwashe manyan naman cikin miyar haka dai na zubawa Bilal sauran na ɗakko ƙaramin try na ɗora masa akai na kai gaban sa na ajiye.
Indomie na koma na dafa na soya ƙwai kamar na san za'a yi haka da zan yi aiken na bada aka siyo mun na wuce ɗaki na ci. Ko sallama bamu yi da baƙin ba na dai ji sanda suke sallama da Bilal ɗin bai kira ni ba nima ban fita sai da ya kullo ƙofa ya dawo ya fara kwarara mun kira tun daga tsakar gida.