Sashe 88
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar da nayi kwana uku da fitowa daga Asibiti har lokacin tsakanina da Mama tsantsar kulawa ce tamkar zata mayar dani ciki ta sake haifoni haka take ji dani, duk sanda na kalleta tana mun hidima na tuna furucin Bilal sai naji wani abu tamkar dutse ya danne mun ƙirji. Kamar kullum bayan ta taimakamun nayi wanka na shirya ta fita ta dawo da try data ɗora mun breakfast, haka ta zauna tana tausata har saida naci da yawa kafin ta ɗauke ta sake dawowa da ruwa ta fito da magunguna na ta bani na sha sannan ta ɗakko mun wayata da jona mun a caji ta ajiye a kusada ni tana cewa
"Ga wayarki nan tayi caji sai ki kunna dan ƙila ana ta nemanki ba'a samu". Kaina yana ƙasa bance komai ba naja wayar na turata ƙasan filo, damuwa zan ƙarawa kaina idan na kunnata dan haka gara tayi ta zama a kashe kawai.
Ganin ta gyara zama tana kallona yasa naji zuciyata ta shiga bugawa da sauri dan na san da wahala idan ba zancen Bilal zata mun ba. A tsayin sati biyun da nayi a kwance ko bisa kuskure banji wani ya ambaci sunansa ba, na san kuma bai zo ba babu kuma wani nasa da yazo na san kuma dama babu yanda za'ayi su cigaba da yi mun shiru dole akwai lokacin da zasu tambayeni dalilin zuwana gida da kuma dalilin ciwo na amma bana zaton ina da amsar da zan bayar a nan kusa ko a gaba.
"Ta yaya zan faɗa musu alaƙar banza na kama Bilal yanayi da wata mace a waje? Da wanne ido zasu cigaba da kallonsa? Ba shi ba ina zaton har yayana sai martabar su ta taɓu idan wannan maganar ta fita shiyasa nayiwa kaina alƙawarin shanye baƙin ciki na ni kaɗai ba zan taɓa faɗawa kowa komai ba tunda dama damuwata tace bai kamata kuma naci gaba da raba baƙin ciki na dasu ba.
"Halima magana nake so muyi" ta faɗa hakan kuma ya saka bugun zuciyata ƙara gudu, na kalleta kafin na sakw sadda kaina ƙasa ina ji tayi murmushi mai sauti kafin ta kamo hannuna cikin nata tace
"Mai ya faru Halima?"
Nayi kamar ban fahimci mai take nufi ba hakan ya saka ta sakw cewa
"Ina nufin mai ya faru tsakaninki da Bilal?"
Jimm nayi amsoshi da yawa suna yawo a raina amma na rasa wacce ta dace da in bata, yanda take kallona kuma nasan koma me zan faɗa da yake akasin gaskiya zata amma kuma dole inyi mata ƙarya domin wannan gaskiyar ba mai faɗuwa bace. Cikin in ina nace
"Babu komai Mama"
"Babu komai kika ce?, babu komai ya kawo ki gida ƙarfe bakwai na safe kuma tunda ya tafi bai sake waiwayarki ba?" Ta faɗa tana tsareni da ido. Na ɗauke kaina gefe nace
"Tafiya zaiyi ai shiyasa ya kawo mu gida". Shiru tayi dan har saida na sace kallonta naga itama ni take kallo da alama ta rasa abun faɗa ne shiyasa tayi shiru tana kallona, can taja numfashi tace
"Ba wasa nakeyi ba Halima ki faɗa mun wace damuwa gareki a aurenki da har take barazana ga rayuwarki?"
Ɓata fuska nayi kamar zan fashe da kuka nace
"Na faɗa miki babu komai Mama idan da akwai ai kin san ba zan ɓoye miki ba zan gaya miki ko?" Shirun ta sakeyi kafin ta miƙe a sanyaye tana cewa
"Shikenan" daga haka ta fice daga ɗakin na bita da kallo jiki a sanyaye ina jin kamar na tashi na bita na faɗa mata amma kuma bazan iya ba. Cusa kaina nayi cikin pillow na fashe da kuka.
Tun daga ranar kuma Mama ta janye mun duk wata hidima da take mun da kanta ta saki sai Zainab ce takeyi ko kuma inyiwa kaina hakan kuma ba ƙaramin ƙara mun damuwa yayi akan wacce nake ciki ba duk gidan sai ya mun ba daɗi, Abba ya koma Lagos, Amirah ta koma makaranta Al'amin dama tun da aka kwantar dani Anty Labiba ta tafi dashi gidanta har ta sakashi makarantar su Inaayah ya fara zuwa Sharifa ma kuma Mama Fauziyya ta ɗauke ta da muka dawo saboda na huta karta ringa damuna da rigima dan haka dagani sai Mama da Zainab sai kuma su Suraj a bakin Gate duk sai gidan ya mun faɗi babu daɗi tarairayar da nake samu an janye mun tallafi kusan magana ma sai ta zama dole sannan take mun.
Ranar dana cika sati ɗaya da dawowa daga Asibiti wanda ya kama sati uku kenan da barowata gidan Bilal ina zaune a falo na zubawa Tv ido, gajiya nayi da zaman ɗaki na fito ina zama kuma Mama ta tashi ta fita can tsakar gida ta fara aikin da bansan na menene ba, ni dai na fahimci kawai zama tareda ni ɗin ne bata so, har nayi kamar na bita sai kuma na fasa na zauna, dama tunda Anty Labiba tazo jiya naga tana wani hararata na san sai ta sake zugata ilai kuwa gashinan.
Ina nan zaune a zahiri Tv nake kallo amma a baɗini nayi zurfi cikin tunani. Ni da kaina na san na zama wata iri, nayi rama mara fasali duk da yanda Mama take matsamun kan cin abinci amma tamkar yana bin rariya yana tsiyayewa ne dan babu abinda yake nunawa a jikina azabar tunani da ƙuncin daya cunkushe mun zuciya su suka hana sassan jikina karɓar abincin su sarrafa shi yanda ya kamata.
Daga waje na ringa jiyo kamar muryar Hansa'u suna gaisawa da Mama, ba zan iya tuna rabon da nayi magana da ita ba dan an ɗauki lokaci mai yawan gaske tun kafin na haifi Sharifa wani zuwa da tayi taje gidana ta tarar da abincin da Bilal ya auna mun zan dafa tayi mun magana akan kada na kuskura na fara rayuwar da a gaba zanzo ina kuka da kaina har tayi iƙirarin zata gayawa Mama halin da nake ciki a sannan haka na rufe ido na gaya mata maganganu son raina kuma nace ta fita a duk wata sabgatar gidan aurena ko da take ɗaga kafaɗa tana iyayi ai sai dai idan ba zata faɗi gaskiya ba amma itama tana da nata matsalar ƙila ma halin da take ciki yafi nawa dan haka kowa yaji da kansa idan gulma zata ringa kawota ni na yafe kada ta sake zuwa in da nake.
Haka muka rabu dutse a hannun riga ta kuma ɗaukar mun alƙawarin ba zan sake ganin ƙafarta a gida na ba dama kuma duk cikin ƙawayen mu ita kaɗai ce take har sannan dan su Baby su Zainab mun daɗe da yin uwaka ubanka tun bayan haihuwar Al'amin da suka sameni har gida zasu gaya mun maganar banza akan wai labari ya baza gari komai daga gidanmu aka mun nan ma na musus tatas nace nagodewa Allah inada gatan da za'a mun a gidan namu su dai da suke taƙama da miji randa bai musu ba sai in ga ina zasu kama shikenan mukayi baran baran suka fita harkata.
Idona akan ƙofa harta shigo falon cikin kyakkyawar shigar Abaya data matuƙar karɓar ta. Ko dan na jima ban ganta ba sai naga ta ƙara wani kyau da kwarjini ta sake zama bababar mace kana kallonta ba sai an gaya maka nutsuwa da kwanciyar hankali sun bi jikinta ba. Da sauri ta ƙaraso in da nake tana kallona kafin ta rungume ni lokaci ɗaya ta fashe da kuka wanda tamkar nima ina jira na fashe da kukan da na daɗe ina so nayi amma damuwar Mama ta saka nake haɗiye shi. Rungume da juna muna kukan kamar ƙananan yara muka shiga ɗaki na, kan gado muka zauna muka cigaba da kukan zuwa wani lokaci kafin ta sassauta nata ta fara rarrashi na wanda daƙyar mukayi shiru a ƙarshe.
"Halima mai ya faru? Mai yayi zafi a duniyar nan kika mayar da kanki haka Halima kina kallon mudubi kuwa?" Ta faɗa tana ɗauke sabbin hawayen da suka far zubo mata. Na kwantar da kaina a kafaɗar ta nace
"Hansa'u ƙirji na zafi yake mun zuciyata ina jin tamkar zata fashe"
"Me kika aje a zuciyar? Ki amayar da koma menene Halima zaki samu sauƙi duk wani nauyi da kika ji zai sauka" ta faɗa tana ɗagoni daga jikinta. Nayi shiru ina kallonta, tabbatas ina da buƙatar fitar da abinda yake ci mun zuciya tun bai gama yi mun illar da ba zata gyaru ba, na buɗe baki da niyyar magana sautin muryar Bilal ya shiga yawo a kunnena sanda yake cewa
"Kafin su zageni sai sun fara yi miki dariya sunce Allah ya ƙara Halima duk wanda kika faɗawa aibu na laifinki zai gani ba ni ba" tuna hakan y aka na rufe bakina ba tareda na ce komai ba na zame daga riƙon da ta mun na kwanta ina ajiyar numfashi. A hankali tace
"Bazan miki dole akan ki faɗa mun abinda yake damunki ba amma ki sani barin kashi a ciki baya taɓa maganin yunwa Halima. Meye ribarki ki rayu cikin fushin iyaye Halima? Ace da ki faɗi damuwarki wacce kulawa ce ma har ta saka aka damu da aji domin a nema miki mafita amma ke kin gwammace ki ƙara jefa kanki cikin wani bala'in ta hanyar shiga fushin iyaye?
Ni dai ban sanki a haka ba ban kuma san mai ya canza ki ba shiyasa ko da nayi fushi dake nace zan fita a sabgarki bana iyawa saboda nasan ke ɗin a yanzu ba Halimar dana sani a baya bace kuma kina da buƙatar mu domin idonki ya buɗe ki gane gaskiya a yanda take ki fita daga iziyar zaton da kike ciki amma kuma duk yanda muka so da mutaimakeki har idan baki so ba babu hali tunda ba zamu miki dole ba, amma ina so ki sani rai ɗaya ne kuma a duniyar nan babu wani namiji daya cancanci sadaukarwar rayuwa domin a yau kika mutu a gobe zai samu madadinki na sani kuma ko a yanzu kinga izina da ranki baki mutu ba to kiyi hasashen makomar yayanki a bayan ba ranki sai ki yiwa kanki Hisabi kan abinda ya kamata kiyi" ta ƙarasa tana miƙewa haɗi da ɗaukar jakarta.
"Ga wayarki nan tayi caji sai ki kunna dan ƙila ana ta nemanki ba'a samu". Kaina yana ƙasa bance komai ba naja wayar na turata ƙasan filo, damuwa zan ƙarawa kaina idan na kunnata dan haka gara tayi ta zama a kashe kawai.
Ganin ta gyara zama tana kallona yasa naji zuciyata ta shiga bugawa da sauri dan na san da wahala idan ba zancen Bilal zata mun ba. A tsayin sati biyun da nayi a kwance ko bisa kuskure banji wani ya ambaci sunansa ba, na san kuma bai zo ba babu kuma wani nasa da yazo na san kuma dama babu yanda za'ayi su cigaba da yi mun shiru dole akwai lokacin da zasu tambayeni dalilin zuwana gida da kuma dalilin ciwo na amma bana zaton ina da amsar da zan bayar a nan kusa ko a gaba.
"Ta yaya zan faɗa musu alaƙar banza na kama Bilal yanayi da wata mace a waje? Da wanne ido zasu cigaba da kallonsa? Ba shi ba ina zaton har yayana sai martabar su ta taɓu idan wannan maganar ta fita shiyasa nayiwa kaina alƙawarin shanye baƙin ciki na ni kaɗai ba zan taɓa faɗawa kowa komai ba tunda dama damuwata tace bai kamata kuma naci gaba da raba baƙin ciki na dasu ba.
"Halima magana nake so muyi" ta faɗa hakan kuma ya saka bugun zuciyata ƙara gudu, na kalleta kafin na sakw sadda kaina ƙasa ina ji tayi murmushi mai sauti kafin ta kamo hannuna cikin nata tace
"Mai ya faru Halima?"
Nayi kamar ban fahimci mai take nufi ba hakan ya saka ta sakw cewa
"Ina nufin mai ya faru tsakaninki da Bilal?"
Jimm nayi amsoshi da yawa suna yawo a raina amma na rasa wacce ta dace da in bata, yanda take kallona kuma nasan koma me zan faɗa da yake akasin gaskiya zata amma kuma dole inyi mata ƙarya domin wannan gaskiyar ba mai faɗuwa bace. Cikin in ina nace
"Babu komai Mama"
"Babu komai kika ce?, babu komai ya kawo ki gida ƙarfe bakwai na safe kuma tunda ya tafi bai sake waiwayarki ba?" Ta faɗa tana tsareni da ido. Na ɗauke kaina gefe nace
"Tafiya zaiyi ai shiyasa ya kawo mu gida". Shiru tayi dan har saida na sace kallonta naga itama ni take kallo da alama ta rasa abun faɗa ne shiyasa tayi shiru tana kallona, can taja numfashi tace
"Ba wasa nakeyi ba Halima ki faɗa mun wace damuwa gareki a aurenki da har take barazana ga rayuwarki?"
Ɓata fuska nayi kamar zan fashe da kuka nace
"Na faɗa miki babu komai Mama idan da akwai ai kin san ba zan ɓoye miki ba zan gaya miki ko?" Shirun ta sakeyi kafin ta miƙe a sanyaye tana cewa
"Shikenan" daga haka ta fice daga ɗakin na bita da kallo jiki a sanyaye ina jin kamar na tashi na bita na faɗa mata amma kuma bazan iya ba. Cusa kaina nayi cikin pillow na fashe da kuka.
Tun daga ranar kuma Mama ta janye mun duk wata hidima da take mun da kanta ta saki sai Zainab ce takeyi ko kuma inyiwa kaina hakan kuma ba ƙaramin ƙara mun damuwa yayi akan wacce nake ciki ba duk gidan sai ya mun ba daɗi, Abba ya koma Lagos, Amirah ta koma makaranta Al'amin dama tun da aka kwantar dani Anty Labiba ta tafi dashi gidanta har ta sakashi makarantar su Inaayah ya fara zuwa Sharifa ma kuma Mama Fauziyya ta ɗauke ta da muka dawo saboda na huta karta ringa damuna da rigima dan haka dagani sai Mama da Zainab sai kuma su Suraj a bakin Gate duk sai gidan ya mun faɗi babu daɗi tarairayar da nake samu an janye mun tallafi kusan magana ma sai ta zama dole sannan take mun.
Ranar dana cika sati ɗaya da dawowa daga Asibiti wanda ya kama sati uku kenan da barowata gidan Bilal ina zaune a falo na zubawa Tv ido, gajiya nayi da zaman ɗaki na fito ina zama kuma Mama ta tashi ta fita can tsakar gida ta fara aikin da bansan na menene ba, ni dai na fahimci kawai zama tareda ni ɗin ne bata so, har nayi kamar na bita sai kuma na fasa na zauna, dama tunda Anty Labiba tazo jiya naga tana wani hararata na san sai ta sake zugata ilai kuwa gashinan.
Ina nan zaune a zahiri Tv nake kallo amma a baɗini nayi zurfi cikin tunani. Ni da kaina na san na zama wata iri, nayi rama mara fasali duk da yanda Mama take matsamun kan cin abinci amma tamkar yana bin rariya yana tsiyayewa ne dan babu abinda yake nunawa a jikina azabar tunani da ƙuncin daya cunkushe mun zuciya su suka hana sassan jikina karɓar abincin su sarrafa shi yanda ya kamata.
Daga waje na ringa jiyo kamar muryar Hansa'u suna gaisawa da Mama, ba zan iya tuna rabon da nayi magana da ita ba dan an ɗauki lokaci mai yawan gaske tun kafin na haifi Sharifa wani zuwa da tayi taje gidana ta tarar da abincin da Bilal ya auna mun zan dafa tayi mun magana akan kada na kuskura na fara rayuwar da a gaba zanzo ina kuka da kaina har tayi iƙirarin zata gayawa Mama halin da nake ciki a sannan haka na rufe ido na gaya mata maganganu son raina kuma nace ta fita a duk wata sabgatar gidan aurena ko da take ɗaga kafaɗa tana iyayi ai sai dai idan ba zata faɗi gaskiya ba amma itama tana da nata matsalar ƙila ma halin da take ciki yafi nawa dan haka kowa yaji da kansa idan gulma zata ringa kawota ni na yafe kada ta sake zuwa in da nake.
Haka muka rabu dutse a hannun riga ta kuma ɗaukar mun alƙawarin ba zan sake ganin ƙafarta a gida na ba dama kuma duk cikin ƙawayen mu ita kaɗai ce take har sannan dan su Baby su Zainab mun daɗe da yin uwaka ubanka tun bayan haihuwar Al'amin da suka sameni har gida zasu gaya mun maganar banza akan wai labari ya baza gari komai daga gidanmu aka mun nan ma na musus tatas nace nagodewa Allah inada gatan da za'a mun a gidan namu su dai da suke taƙama da miji randa bai musu ba sai in ga ina zasu kama shikenan mukayi baran baran suka fita harkata.
Idona akan ƙofa harta shigo falon cikin kyakkyawar shigar Abaya data matuƙar karɓar ta. Ko dan na jima ban ganta ba sai naga ta ƙara wani kyau da kwarjini ta sake zama bababar mace kana kallonta ba sai an gaya maka nutsuwa da kwanciyar hankali sun bi jikinta ba. Da sauri ta ƙaraso in da nake tana kallona kafin ta rungume ni lokaci ɗaya ta fashe da kuka wanda tamkar nima ina jira na fashe da kukan da na daɗe ina so nayi amma damuwar Mama ta saka nake haɗiye shi. Rungume da juna muna kukan kamar ƙananan yara muka shiga ɗaki na, kan gado muka zauna muka cigaba da kukan zuwa wani lokaci kafin ta sassauta nata ta fara rarrashi na wanda daƙyar mukayi shiru a ƙarshe.
"Halima mai ya faru? Mai yayi zafi a duniyar nan kika mayar da kanki haka Halima kina kallon mudubi kuwa?" Ta faɗa tana ɗauke sabbin hawayen da suka far zubo mata. Na kwantar da kaina a kafaɗar ta nace
"Hansa'u ƙirji na zafi yake mun zuciyata ina jin tamkar zata fashe"
"Me kika aje a zuciyar? Ki amayar da koma menene Halima zaki samu sauƙi duk wani nauyi da kika ji zai sauka" ta faɗa tana ɗagoni daga jikinta. Nayi shiru ina kallonta, tabbatas ina da buƙatar fitar da abinda yake ci mun zuciya tun bai gama yi mun illar da ba zata gyaru ba, na buɗe baki da niyyar magana sautin muryar Bilal ya shiga yawo a kunnena sanda yake cewa
"Kafin su zageni sai sun fara yi miki dariya sunce Allah ya ƙara Halima duk wanda kika faɗawa aibu na laifinki zai gani ba ni ba" tuna hakan y aka na rufe bakina ba tareda na ce komai ba na zame daga riƙon da ta mun na kwanta ina ajiyar numfashi. A hankali tace
"Bazan miki dole akan ki faɗa mun abinda yake damunki ba amma ki sani barin kashi a ciki baya taɓa maganin yunwa Halima. Meye ribarki ki rayu cikin fushin iyaye Halima? Ace da ki faɗi damuwarki wacce kulawa ce ma har ta saka aka damu da aji domin a nema miki mafita amma ke kin gwammace ki ƙara jefa kanki cikin wani bala'in ta hanyar shiga fushin iyaye?
Ni dai ban sanki a haka ba ban kuma san mai ya canza ki ba shiyasa ko da nayi fushi dake nace zan fita a sabgarki bana iyawa saboda nasan ke ɗin a yanzu ba Halimar dana sani a baya bace kuma kina da buƙatar mu domin idonki ya buɗe ki gane gaskiya a yanda take ki fita daga iziyar zaton da kike ciki amma kuma duk yanda muka so da mutaimakeki har idan baki so ba babu hali tunda ba zamu miki dole ba, amma ina so ki sani rai ɗaya ne kuma a duniyar nan babu wani namiji daya cancanci sadaukarwar rayuwa domin a yau kika mutu a gobe zai samu madadinki na sani kuma ko a yanzu kinga izina da ranki baki mutu ba to kiyi hasashen makomar yayanki a bayan ba ranki sai ki yiwa kanki Hisabi kan abinda ya kamata kiyi" ta ƙarasa tana miƙewa haɗi da ɗaukar jakarta.