← Book details Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 99 OF 145

Sashe 99

Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kusan wata uku nan ma aka ci amma asirin bai karye ba har malam Habu ya d'ago daga lamarin kamar abun wasa rana tsaya yana tsaye yaji hajijiya tana d'ibansa karshe ya fad'i kumfa na fita a bakinsa yana wata irin kara jikinsa na kakkarwa yana harbe harbe tun safe har dare kusan kwana yai yana buge buge harda haya'ki ne ke fita ta hancinsa sai wajajen asuba sannan jikinsa ya saki ya zama kamar gawa shiru jikinsa yayi laushi kuma sanyi qalau dukkan matansa da yayansa suna kansa suna masa addu'a suna share hawaye haka suka je kowa yai sallah suka sake dawowa kansa nan ma bai farka abun yanata basu tsoro kuma dama malamin yace kada a tasheshi saiya tashi da kansa ganin abun ya zarma tunaninsu yasa dole suka nemo Alhaji Musa yayi waya da malamin ba'a dad'e ba sai gashi yazo ya du'kufa a kansa da karatun al-qur'ani da addu'a nan wani sabon kururuwa da buge bugen ya tashi yana mummurd'ewa yana gwara kansa a bango can malamin ya mike yana zuwa inda yake ya kamashi da karfi ya daidaici tsakiyar goshinsa ya fara tofa masa addu'a da tsakiyar kansa a hankali jikinsa yake saki yana yaushi can ya zube a jikin malamin karasa kwantar dashi yai yana fita a d'akin da murmushi a fuskarsa yace sihirin dake jikinsa ya gama ficewa dukka dalilin da yasa sukaga bai farka ba wani asirin akayo masa kwanan nan kuma shima tare da aljani aka hada to alhajinin ne ya ri'ke dukkan sihirin ya hanusu fita shiyasa da ya kama barci bai farka ba amma yanxu ko minti talatiin bazaiyi zai tashi kuma kada wanda ya fad'a masa ga abinda ya sameshi suyi shiru malamin yana gama musu jawabi ya tafi.

Suna zaune a waje sai ganin Malam Habu sukai ya fito yana kalle kalle kamar wanda yai batan kai cikin basarwa Binta tace.

"Malam lafiya ko buta kake nema"?.

'Dan shiru yai yana kallon ta zuwa wani lokaci yace "eh Ina take na duba bata d'aki na kuma duk sauran kayana ma ban gansu ba ina kuka kaimin"?.

Murmushi tai tana cewa "ayya yi hakuri Malam dama mamar gida ce tace d'akinka yayi datti zata gyara maka idan suka dawo daga makaranta itace ta fara fito da komai".

Kai ya d'aga "au shikenan to aina d'auka ko sune suka fito da kansu daga d'akin" ya fad'a yana d'aukar buta yai hanyar bayi dariya Binta tai tana cewa.

"Kiji dan Allah wai kaya su kawo kansu waje uhm malam kai jama'a Allah dai ya rufa asiri Allah yasa a dace dauran tsinannun da suke kansa ma su fice mu huta ashe bada banza ba komai malam ya ta'ba sai kiga babu komai yayi sai kiga wayam duk abubuwan hannunsa suka kare komai ka d'auka ka bashi saiya narke ashe asiri ne a jikinsa.

'kwafa A'i tai tana cewa "ni abun tambayar ma anan shine wanne mitsiyacin ne yayi masa asirin a garin"?.

"To A'i wa zakace gari da yawa kuma bakasan iya ma'kiyan kaba sai kiga wanda kake tunani bashi bane wani ne dabam dan haka babu abinda xamuce fatanmu Allah ya taimaki Malam damu ya rabashi da shed'anun da suke jikinsa ko ma samu zaman lafiya".

Tsaki A'i tai tana cewa "ai wallahi Allah ya isa tsakanin mu da koma waye yayi masa haka ya cutar dashi damu ya rabashi da dukiyarsa ya hana yar sana'ar da zaiyi ya ri'ke mu komai ya ta'ba babu muna ganin laifin sa humm Allah ya tona asirin wanda yai masa haka ya tagayyara shi".

Da sauri Saude tace "Amin A'i dan gaskiya ta takin an cutar damu sosai an zalunce mu amma Allah yasa hakan ya zama mana taki sannan shi sharri dan aikene duk wanda ya aikoshi koma waye gashi nan yau zai koma kansa Allah ya sauwake" Amin sukace ganin Malam Habu ya fito daga bayin yasa sukai shiru da maganar suka d'auko wani zancen saida yai alwala ya tafiya masallaci suka d'ora a inda suka tsaya.

MRS AL'AMEEN AHMAD CE😘
Tnks so much I really appreciate it masoya.

Sai mun sake had'uwa see you next time,😉 we will meet again🤗.

TYPING📲 FRI Aug30/24 08:18AM
YUSRAH MUSA ABUBAKAR💋.

🎆✨ME KAMAR SARKI✨🎇

Story nd written
✍️Mrs Al'ameen Ahmad ce.

__________________________________
______________________
_______________
💫ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ASS💫
Haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake.

63~AL-QAYYUM
The Guardian
64~AL-WAJIDU
The Perceiver.

31~Allahumma salli wa sallim wa barik ala sayyidina muhammadin sayyidi Ahlul jannati.

🌄REACTION ND RIDICULE🌄
Episode 63&64
🏕️ QAUYE🏕️
________Zaune su Sadi suke a majilasarsu ana hira Tanko ya kalleshi yana dariya yace "Sadi ya mutumin kuwa malam Habu kana jin labarin sa ina ya tafi gudun hijirar ne ko saudiyya dan nasan acan sai yafi samo kud'i shi kuma naga qarfi da yaji so yake saiya dawo da arzikinsa humm isa tana wahalar damai kaya kara yana can yana ihu bayan hari bari da zamuga a yadda zai dawo mana garin da borin kunyar ba'a shigo da ko biyar ba harda d'iban mata da 'ya'ya kuyu-kuyu waishi gamai 'kaura hahhhh lallai ayi mu gani ai labari yazo mana da gudu ka bishi bayan gari kana kukan ya dawo gida shikuma ya'ki saura kaima nan gaba kadan za'a ga ka shirya kabi bayansa tunda naga gasa kake dashi ko ya fad'a maka inda zaije ne daga baya kaje ka sameshi"?.

Had'e rai Sadi yai cikin takaici yace "ban sani ba inace ku kuka dama kusan inda yake kuje ku binciki inda ya tafi tunda matsuwa kukai ku sani na rasa wanne irin qahon zu'ka suka kafawa malam Habu kamar wanda yai muku wata tsiyar duk girman qauyen nan babu wanda kuka sawa ido dan masifa sai shi haba aikin banza kawai" Sadi ya karasa maganar a fusace yana jan tsaki.

Kallon juna sukai cikin mamaki kafin Mudi yace "kai Sadi! kai Sadi!! kai Sadi!!! sau nawa na kira ka? Ya fad'a yana kallon sa ganin yayi danza dashi yaci gaba.

"Sau uku na Kira ka a matsayin gargad'i ina maka kashedi daf da duka ka iya bakin ka ka iya harshenka idan kuma ka'ki zakaga abinda ake Kira da jaki sha duka tunda naga kaima kanka a toshe yake".

Wani irin kallo Sadi yayi masa yana cewa "dama ka ta'ba ganin inda dabba ta had'a kanta da mutum ne"?.

Zaro ido Mudi yai ba arziki ya kalli Sadi yana cewa "miye abinda kake nufi da maganar ka waye dabban kenan"? Yai tambayar a fusace.

Dariya malam Isyaku dake gefe yana sauraron su yana cewa "haba Mudi shifa Sadi ba dakai yake yada saurin tsarguwa yasan kai mutum akan wanne dalili zaice maka dabban ai wannan ba komai bane koba haka ba Sadi" ya karasa maganar yana kallo Sadi kai ya jinjina yana cewa.

"Kai d'an gari mai kyakkyawar 'kwa'kwalwa shi harya fahimta ina Ina Mudi ai babu wani abu hakan ma ina kana da 'ya'yanka ne" ya fad'a yana sakar masa harara.

'Kwaruwa Mudi yai jin yadda Sadin ya gasa masa magana a gaban mutane yace "me kake nufi"?.

Ta'be baki Sadi yai yana cewa "babu abinda nake nufi indai irinka ne".

Baki bud'e cike da mamakin rashin fahimtar maganar Sadi Mudi yace "irina kuma"?.

Kai Sadi ya d'aga masa "eh ire-irenka nake nufi marasa amfani tozartattu masu yankakken baya gara wani idan baida arzikin komai yana da babban arzikin 'ya'ya wanda wani kuma duk dukiyarsa bai isa ta saya masa koda d'a guda d'aya ne ba dan haka a cikin wadannan mutanen waye matsiyaci mai arzikin 'ya'ya kome arzikin dukiya? Humm Mudi tirrr da halin rashin hankalin wasu mutanen masu kwakwalwa irin ta kifi wanda basa gane komai su duk abinda yazo ransu daidai ne kodan dama biri yana kama da mutum tunda jahilai ne tun farko".

Sadi na rufe baki Mudi yai tsalle ya cukumi wuyan rigarsa yana cewa "ni kake cewa me yankakken baya saboda bani da d'a kuma ka kirani jahili"?.

A fusace Sadi yace "eh na fad'a kai jahili ne Mudi ko karya nayi sannan ba yankakken bayan gareka ba ka fad'a min ko yanxu ka mutu kana da d'an da idan an ganshi za'a tunaka babu saidai idan zance ya tashi a ambace ka dukiyar da kake tunkaho da ita 'yan uwanka ne zasu rabata a junansu su cinye babu wanda zaiyi maka sadakar ko naira biyar balle suyi maka addu'a kenan amma wanda kake magana a kansa talakan fa mai 'ya'ya shine mai babban arziki mai wadataccen baya wanda koda bayan ransa za'a tuna dashi bawan Allah mai kyakkyawar zuciya ko kunya bakwa ji kun d'auki tsana kun d'ora masa ba laifin tsaya ba na zauna wanda yayiku yana kallon ku shine mai hisabi tsakanin ku xaku gani a 'kwaryarku" .

Jin abinda yake cewa yasa Tanko Shima ya daina rabiyar fad'an ya cakumo Sadin suka tarar masa su biyu suna dambe dambe ganin haka yasa d'an uwan dake gurin Sadi Malam Sabo shima ya nad'e qafar wando ya shiga fad'an nan hayaniya da tashin hankali ta 6arke harda yage yagen kaya abun dai saida ya kaisu gaban mai gari akai shira'a mai gari ya tsiga tsaka akai musu iyaka babu su ba Sadi kada wani abu ya sake faruwa makamancin haka domin anan sune basu da gaskiya koma me Sadi ya fad'a musu da badu tsokane Shiba hakan bazai faru ba saida sukai kaca kaca da Sadi dasu Tanko sannan ya samu zaman lafiya a majilasar suka daina kulashi ba su bashi ba wanda yake shiga safgar wani Babu ruwan wani da wani basu sake tunkararsa da maganar malam Habu ba.

Zaune Ilyah yake akan tabarma ya jingina da bango ranar baije kasuwa ba yana gida yana shan iska Bara'atu tana gefensa sai zance suke suna 'bab'baka dariya duniya tasu lahira ko a gidan haya sa zauna😳 Maimuna itakuma taje anguwa su Nafisa duk basa gida sai iya su biyun ya saki baki yana faffad'a mata yawan dukiyarsa da kadarorinsa harda zancen saye gonar malam Habu da gidansa dayai a gurin mutanen nan.
Chapter 99 · 0% Book details