Sashe 44
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dalah na zaune Balarabe ya shigo yana zama d'an kallonsa tai tana cewa "daga ina haka na ganka afujajan tun d'azu da kace bari ka dawo sai naji shiru ko nisa kayi ne"? Shiru Balarabe yai yana sake kishingid'a kamar bazai magana sai kuma yace "daga anguwa nake" da sabon mamaki Dalah tace "anguwar gabas ko yamma wacce kaje" da yanayin fad'a yace "anguwar kudu da ta arewa naje ina ruwan ki da samun ido ko da haka kike idan na fita na dawo idan kuma yau zaki fara ki sanar dani" kasa rufe baki Dalah tai sai ido da take binsa dashi jin abinda bata saba jiba to kodai wani ne ya 'bata masa rai a waje sake kallonsa tai tana cewa "kayi hakuri bari a kawo maka abinci" zata mike yace "na 'koshi karki zuba" komawa tai ta zauna bata sake magana ba shima haka kamar kuma an taikare shi zunbur ya tashi zaune yana cewa "Dalah nifa aure zan 'kara" jiki a sanyaye Dalah tace "Allah ya sanya alkairi wacece"? "Kinsan Asabe"? Kaita girgiza "a'a ban santa ba" "to amma ai kinsan wacce ta baiwa Indo kosai kwanakin baya to itace" a d'an zabure Dalah tace "wai matar da tazo gidan nan kwanan baya" "eh ita" da mamaki Dalah ta kalleshi "amma kasan bazawararka ce harda kama ta da balbalin fad'a a gabana"? "Eh ai sannan banji ina son ta ba" sauke ajiyar zuciya Dalah tai "ai shikenan Allah yasa haka ne yafi alkairi idan kuma ba alkairi bace a tare dakai Allah ya baka wacce ta fita" caraf Balarabe yace "ai itace ma ki daina yimin fatan tsiya kodan kina ba'kin ciki zan karo miki kishiya ne" kai Dalah ta girgiza bata sake magana ba sai tsananin mamaki daya gama cika ranta mutumin daya hau fad'a ranar da tazo kamar zai daketa shine kuma yau me cewa yana sonta anya kalau ta barshi abun nan da dubawa.
Lokacin rabon da habu yake yi yayi ya sayo atamfofi da yadika kamar yadda ya saba gida gida da majalinsa haka yake rabon kaya da kud'i sosai yake shan addu'a shiyasa koda yaushe samunsa yake bun'kasa ga bikin suna ya gabato Habu yayi shirin sunan yarosa ya sayo komai da manyan raguna guda biyu ba'kin 'yan uwa kuwa har sunzo ana gobe suna jaririn ya rasu😣 innalillahi kamar babban mutum ne ya rasu haka gidan ya cika da jama'a kofar gidan ma haka sosai Habu mutuwar ta ratsa masa jiki ba shiba hatta sauran jama'a sun jajanta masa washe gari kowa cewa yake saidai a hakura da daurin auren Habu yace a'a kawai a d'aura haka akai daurin auren babu wani armashi ranar da yaron ya cika kwana bakwai da rasuwa ranar aka rako A'i.
Tashin hankali da bala'i iri iri Ramatu ta ri'ka saukewa Ilyah ta hana shi zaman lafiya har saida taga ya auri Maimuna sannan bakinta yai shiru ta 'kyale shi ya huta bayan sallar isha kad'an sai ganin tawaga Ramatu tai tana shigowa duk zaton ta masu rako Maimuna ne amma sai taga sunyi hanyar d'akin Bara'atu da gudu taje ta sha gaban su tare da cewa.
"Kai kai kai ya haka ku tsaya meye wannan daga ina zuwa ina?".
Da mamaki wata 'kanwar kandiya tace ", a'a kamar ya daga ina zuwa ina wanne wacce irin tambaya ce Bara'atu mana muku rako ta dawo d'akin mijinta" wani kallo Ramatu ta watsa mata tana cewa "ke kuma me kamar 'kanzo ki rufa min baki ban sauko dake ba da wannan asararriyar nake wato tsabar rashin zuciya ba'a je bikonki ba shine kika d'ebo wadannan murd'a murd'ar 'kafafun naki masu zubin doyar kudu kika dawo ko to wallahi bazaki shiga d'akin nan ba sai an kawo Maimuna kinji na fad'a miki dai ko"?.
Ri'ke baki Kulu tai tana kallon Ramatu tace "to ikon Allah wannan wulakancin har ina wai madai tsaya ma dai tukuna wace wannan me maganar uwarsa ce ko 'yar gayyar sod'i ce? Dan duk wacce tasan me take bazata tozarta mu haka ba"
Wata uwar harara Ramatu ta sakar mata tana sake tare kofar d'akin tace "au sannu isashshiya to uwar sace idan bakisan Ramatu ba ko kinajin labari na yau kin ganni" kai Kulu ta jinjina "tabd'ijan Allah ya sauwake wannan rashin arzikin naki har yai yawa ai da Kandiya zataji shawara ta Bara'atu bata samu gurin zama ba hartai shanya ba" kanta Ramatu tai "au jimin makirar mace dama ina ta isa samun gurin zama a gidan nan can da tsiyarta Ilyah yafi karfin aurenta dan haka zaku iya tattarawa ku juya inda kuke fito harda yin 'karyar tana da ciki wata shida ai zamu gani idan wata taran tayi kuma wallahi ba kinji nace haka ba nan gaba kikace ya 'bare sai kin ci gwafar ubanki" duk zaro ido sukai Dijalle zatai magana sukaji ana sakin gud'a alamar an kawo Maimuna matsawa Ramatu tai tana musu kallo she'ke'ke tace "to yanzu kam zaku iya shiga mayu kawai" tana fad'in haka tai gaba.
Da kallo suka bita cikin takaici Kulu tace "ke Barah baki zauna a gidan nan ba komawa zamuyi ke dama ba sonki take ba amma saboda tsabar rashin sanin ciwon kai kika yarda ki sake zama dashi" tsaki Dijalle tai tana cewa "to gashi kinga alama kuwa a gaban mu ma tana wulakanta ta balle kuma taci gaba da zama da d'anta yadda bata da mutuncin nan har dukan suruka zata iya" 'kanwar kandiya dake kallon yadda jikin Bara'atu yai sanyi tace "to yanzu me kuke so ayi zamu juya da itane"? Caraf Dijalle tace "me zai hana Ilyan wa? zata samu wanda ya fishi amma wallahi yadda uwarsa nan bata da mutunci tasa ya kara aure idan Barah tace zata zauna ma ba'kin ciki ne zai karta kuzo kawai mu tafi" juyawa sukai zasu fita Ramatu dake kallon su tace "as as as a gaida na gaba mayu kawai masu ba'kin ido" babu wanda ya kula ta a cikin su suna fita kofar gidan suka hadu da Ilyah yana shirin shiga da mamaki yace "ya na ganku haka akwai abinda ya faru"? Yai tambayar dan shi ko kad'an bai kula da Bara'atu ba ya dauka tana ciki ko Ramatu tai musu wani abu dan yasan sai ita gani ba 'kyalewa.
Kulu ce tace "to me zamuce Ilyah mahaifiyar kace ta wulakanta mu shiyasa mu kuma zamu juya da Bara'atu dan bazata zauna hawan jini ya kama ta ba tunda har mahaifiyar ka tana maganar cikin 'karya gareta".
"Subahanallahi yaushe wai duk yanzun hakan ta faru? Ai ban sani ba dan Allah kuyi hakuri abinda tai muku muje ciki" Karima 'kanwar kandiya tace "a'a Ilyasu babu cikin da zamu koma gaskiya gida zamu mayarta ba abinda Bara'atu zata d'auka a gidan ka sai wahala da damuwa dan haka kayi hakuri kuzo mu tafi" ganin da gaske tafiya zasuyi yasa a rikice Ilyah yace "dan girman Allah kuyi hakuri kuzo muje ku mayar da ita nayi muku alkawari babu abinda zai sameta bazan bari ba" shiru kowa yai Kulu tace "shikenan amma gaskiya ka kula sosai da gidan ka domin akwai matsala" zan kula karku damu ina son Bara'atu bazan bari a wulakanta taba" sun d'an ji dad'i ganin ya damu da ita ko tanan zataji sauki dan haka suka amince ya musu jagora suka mayar da ita har d'akinta tare da mata fad'a cewa duk wani abu zaisa ta tashin hankali da uwar mijin ta koda kishiyar ta ta kiyaye ta ri'ka kawar dakai akan abinda bai shafe taba tunda tasan Ramatu ba mutunci gareta ba karta shiga harkarta karta bari wani abu ya shiga tsakanin su.
Amma asubar fari gari da duhu ko assalatu ba'ai ba Ramatu ta fito daga d'akin ta tana zuwa kofar d'akin Bara'atu ta soma bukawa da karfi tana cewa "ke tsinanniya bunjinjimar asara fito ai ba barci kika dawo yiba zaki bud'e ko saina karya murfin kofar na shigo da kaina na fito dake na miki dukan tsiya yar fatararru" cikin takaici Bara'atu ta bud'e kofa tana kallon Ramatu dake tsaye zatai magana Ilyah ya fito daga d'akin maimuna cikin rashin jin dad'i yace.
"Wai dan Allah babah me yasa kike haka ne da asubar farin nan me zatai miki kika zo kina buga mata kofa duk makota na jinki".
Kansa ta koma "dambun ubanka zatai min asararre waini Ilyah kodai bankad'add'iyar matar nan asiri tai maka ban sani ba babu dama nayi magana saika mayar min bakaso a fad'i laifinta nuna Bara'atu tai da yatsa amma Allah ya tsinewa uwarki kandiya dan komai silarta ne itace ma'kasudin komai bari gari ya gama wayewa wallahi ko bari su karya cikin dad'in rai bazan ba sainaje na 'kaddamar musu bala'i iri iri dama ai tasan hadina da ita ta iya d'ebo ba'kin ido tazo a gantsara mata abinci taci zakuci gwafar ubanku ne daga ke har tsigalgalar uwar taki".
"Dan Allah babah kiyi shiru wannan fa zubar da girma ne" Ilyah yai maganar ransa a 'bace.
"Kai zanci malafar ubanka idan bakai min shiru ba so'ko'kon banza sakalin asara wanda kare ya lashewa zuciya kayi asara tunda harka za'bi matarka akan ni da nake uwarka".
Had'e rai Ilyah yai "ni bance miki na zabeta akanki ba fad'ar kice kawai daga naga kinyi ba daidai ba nayi magana gaskiya abinda kike bakya kyautawa wannan fa ba neman girma bane".
Lokacin rabon da habu yake yi yayi ya sayo atamfofi da yadika kamar yadda ya saba gida gida da majalinsa haka yake rabon kaya da kud'i sosai yake shan addu'a shiyasa koda yaushe samunsa yake bun'kasa ga bikin suna ya gabato Habu yayi shirin sunan yarosa ya sayo komai da manyan raguna guda biyu ba'kin 'yan uwa kuwa har sunzo ana gobe suna jaririn ya rasu😣 innalillahi kamar babban mutum ne ya rasu haka gidan ya cika da jama'a kofar gidan ma haka sosai Habu mutuwar ta ratsa masa jiki ba shiba hatta sauran jama'a sun jajanta masa washe gari kowa cewa yake saidai a hakura da daurin auren Habu yace a'a kawai a d'aura haka akai daurin auren babu wani armashi ranar da yaron ya cika kwana bakwai da rasuwa ranar aka rako A'i.
Tashin hankali da bala'i iri iri Ramatu ta ri'ka saukewa Ilyah ta hana shi zaman lafiya har saida taga ya auri Maimuna sannan bakinta yai shiru ta 'kyale shi ya huta bayan sallar isha kad'an sai ganin tawaga Ramatu tai tana shigowa duk zaton ta masu rako Maimuna ne amma sai taga sunyi hanyar d'akin Bara'atu da gudu taje ta sha gaban su tare da cewa.
"Kai kai kai ya haka ku tsaya meye wannan daga ina zuwa ina?".
Da mamaki wata 'kanwar kandiya tace ", a'a kamar ya daga ina zuwa ina wanne wacce irin tambaya ce Bara'atu mana muku rako ta dawo d'akin mijinta" wani kallo Ramatu ta watsa mata tana cewa "ke kuma me kamar 'kanzo ki rufa min baki ban sauko dake ba da wannan asararriyar nake wato tsabar rashin zuciya ba'a je bikonki ba shine kika d'ebo wadannan murd'a murd'ar 'kafafun naki masu zubin doyar kudu kika dawo ko to wallahi bazaki shiga d'akin nan ba sai an kawo Maimuna kinji na fad'a miki dai ko"?.
Ri'ke baki Kulu tai tana kallon Ramatu tace "to ikon Allah wannan wulakancin har ina wai madai tsaya ma dai tukuna wace wannan me maganar uwarsa ce ko 'yar gayyar sod'i ce? Dan duk wacce tasan me take bazata tozarta mu haka ba"
Wata uwar harara Ramatu ta sakar mata tana sake tare kofar d'akin tace "au sannu isashshiya to uwar sace idan bakisan Ramatu ba ko kinajin labari na yau kin ganni" kai Kulu ta jinjina "tabd'ijan Allah ya sauwake wannan rashin arzikin naki har yai yawa ai da Kandiya zataji shawara ta Bara'atu bata samu gurin zama ba hartai shanya ba" kanta Ramatu tai "au jimin makirar mace dama ina ta isa samun gurin zama a gidan nan can da tsiyarta Ilyah yafi karfin aurenta dan haka zaku iya tattarawa ku juya inda kuke fito harda yin 'karyar tana da ciki wata shida ai zamu gani idan wata taran tayi kuma wallahi ba kinji nace haka ba nan gaba kikace ya 'bare sai kin ci gwafar ubanki" duk zaro ido sukai Dijalle zatai magana sukaji ana sakin gud'a alamar an kawo Maimuna matsawa Ramatu tai tana musu kallo she'ke'ke tace "to yanzu kam zaku iya shiga mayu kawai" tana fad'in haka tai gaba.
Da kallo suka bita cikin takaici Kulu tace "ke Barah baki zauna a gidan nan ba komawa zamuyi ke dama ba sonki take ba amma saboda tsabar rashin sanin ciwon kai kika yarda ki sake zama dashi" tsaki Dijalle tai tana cewa "to gashi kinga alama kuwa a gaban mu ma tana wulakanta ta balle kuma taci gaba da zama da d'anta yadda bata da mutuncin nan har dukan suruka zata iya" 'kanwar kandiya dake kallon yadda jikin Bara'atu yai sanyi tace "to yanzu me kuke so ayi zamu juya da itane"? Caraf Dijalle tace "me zai hana Ilyan wa? zata samu wanda ya fishi amma wallahi yadda uwarsa nan bata da mutunci tasa ya kara aure idan Barah tace zata zauna ma ba'kin ciki ne zai karta kuzo kawai mu tafi" juyawa sukai zasu fita Ramatu dake kallon su tace "as as as a gaida na gaba mayu kawai masu ba'kin ido" babu wanda ya kula ta a cikin su suna fita kofar gidan suka hadu da Ilyah yana shirin shiga da mamaki yace "ya na ganku haka akwai abinda ya faru"? Yai tambayar dan shi ko kad'an bai kula da Bara'atu ba ya dauka tana ciki ko Ramatu tai musu wani abu dan yasan sai ita gani ba 'kyalewa.
Kulu ce tace "to me zamuce Ilyah mahaifiyar kace ta wulakanta mu shiyasa mu kuma zamu juya da Bara'atu dan bazata zauna hawan jini ya kama ta ba tunda har mahaifiyar ka tana maganar cikin 'karya gareta".
"Subahanallahi yaushe wai duk yanzun hakan ta faru? Ai ban sani ba dan Allah kuyi hakuri abinda tai muku muje ciki" Karima 'kanwar kandiya tace "a'a Ilyasu babu cikin da zamu koma gaskiya gida zamu mayarta ba abinda Bara'atu zata d'auka a gidan ka sai wahala da damuwa dan haka kayi hakuri kuzo mu tafi" ganin da gaske tafiya zasuyi yasa a rikice Ilyah yace "dan girman Allah kuyi hakuri kuzo muje ku mayar da ita nayi muku alkawari babu abinda zai sameta bazan bari ba" shiru kowa yai Kulu tace "shikenan amma gaskiya ka kula sosai da gidan ka domin akwai matsala" zan kula karku damu ina son Bara'atu bazan bari a wulakanta taba" sun d'an ji dad'i ganin ya damu da ita ko tanan zataji sauki dan haka suka amince ya musu jagora suka mayar da ita har d'akinta tare da mata fad'a cewa duk wani abu zaisa ta tashin hankali da uwar mijin ta koda kishiyar ta ta kiyaye ta ri'ka kawar dakai akan abinda bai shafe taba tunda tasan Ramatu ba mutunci gareta ba karta shiga harkarta karta bari wani abu ya shiga tsakanin su.
Amma asubar fari gari da duhu ko assalatu ba'ai ba Ramatu ta fito daga d'akin ta tana zuwa kofar d'akin Bara'atu ta soma bukawa da karfi tana cewa "ke tsinanniya bunjinjimar asara fito ai ba barci kika dawo yiba zaki bud'e ko saina karya murfin kofar na shigo da kaina na fito dake na miki dukan tsiya yar fatararru" cikin takaici Bara'atu ta bud'e kofa tana kallon Ramatu dake tsaye zatai magana Ilyah ya fito daga d'akin maimuna cikin rashin jin dad'i yace.
"Wai dan Allah babah me yasa kike haka ne da asubar farin nan me zatai miki kika zo kina buga mata kofa duk makota na jinki".
Kansa ta koma "dambun ubanka zatai min asararre waini Ilyah kodai bankad'add'iyar matar nan asiri tai maka ban sani ba babu dama nayi magana saika mayar min bakaso a fad'i laifinta nuna Bara'atu tai da yatsa amma Allah ya tsinewa uwarki kandiya dan komai silarta ne itace ma'kasudin komai bari gari ya gama wayewa wallahi ko bari su karya cikin dad'in rai bazan ba sainaje na 'kaddamar musu bala'i iri iri dama ai tasan hadina da ita ta iya d'ebo ba'kin ido tazo a gantsara mata abinci taci zakuci gwafar ubanku ne daga ke har tsigalgalar uwar taki".
"Dan Allah babah kiyi shiru wannan fa zubar da girma ne" Ilyah yai maganar ransa a 'bace.
"Kai zanci malafar ubanka idan bakai min shiru ba so'ko'kon banza sakalin asara wanda kare ya lashewa zuciya kayi asara tunda harka za'bi matarka akan ni da nake uwarka".
Had'e rai Ilyah yai "ni bance miki na zabeta akanki ba fad'ar kice kawai daga naga kinyi ba daidai ba nayi magana gaskiya abinda kike bakya kyautawa wannan fa ba neman girma bane".