Sashe 12
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gida suka shiga yana kiran Bara'atu d'aki gata ga Nafisa yace "to batu ne game da zancen Nafisa ga dai yaro Nura dan gidan alhaji Tajuddeen ya ganta ya yi maganar yana sonta to ni abinda nake so anan shine ku bani goyon baya d'ari bisa d'ari mu jajirce mu tabbata Nafisa ta aure shi ta fita daga kauyen nan ina da tabbacin wata rana sai munyi zaman binni mun bar wannan karkarar tun ta iyaye da kakanu domin ban aje kowa ciki ba daga ni sai ku iyalai na bani da wani 'kani ko d'an uwa Habubakar ne kuma shi gara kare ma dashi a gurina".
Dariya Bara'atu tai tana cewa "gaskiya ne malam ka fad'i gaskiya idan muka samu Nafisa ta aure shi mun samu kofar arziki ba karama ba mutanen dake da miliyoyin kud'i a banki a boye" cikin nuna son zuciya Ilyah yace "to kin gani dai nasan 'ya'yana suna da 'kashin arziki yanzu abinda za'ai shine ke Nafisa idan sun sake dawowa kice ya sai miki waya wacce zaku ri'ka magana kinji kuma ki tabbata kina tatsar sa kudade domin baisan ciwon su ba" "to baba" Nafisa ta fad'a tana mikewa ta fita sai murmushi take ita kadai farin ciki ya ishe ta har ji take wata sabuwar iska mai launin sanyi tana shigarta.
Karo sukai da Salma zata fita tare ta Nafisa tai "ke ina zaki je haka ko gurin wancan saurayin naki me kama da tuntu'be shine kike wannan saurin kamar zaki tashi sama anji kunya" wata uwar harara Salma ta sakar mata tana cewa "akwai wanda yaji kunya irin ki kawai tsabar gidahumanci daga ganin mutun ba sanin sa kikai ba babu binkice kawai kice wai kina sonshi" rama hararar Nafisa tai tana cewa "eh haka nake kuma son kayana kuma banga abinda zai hana na aure shi ba sai mutuwa" wucewa Salma tai cikin jin haushin ta tace "au aina dauka mutuwar ma bazata hana kiba nidai yar uwarki ce ta jini a matsayi na namai sonki nake fad'a miki kibi a sannu" da kallo Nafisa ta bita tana tabe baki tace "ji shegiyar yarinya waini zatai wa wa'azi bazan bi a sannun ba da karfi zanbi sainaga wanda zai hana haba Salma na fahimci ba'kin ciki kike dani kuma saidai ki mutu domin mijin dazan aura ya kere naki kyau dan dadai ne babu inda ya zarta ba irin naki ba tudu da gangare yana tafi kamar agwagwa zaki dawo ki same ni" ta karasa maganar tana shiga d'akin su ta kwanta tare da rufe ido kawai tana tunanin Nurain a ranta.
Fatima kam daga gidan Dalah kai tsaye gidansu ta wuce Aliyah babarta na zaune ganin yadda ta shigo yasa tace "Fatima lafiya naga kamar kinyi kuka"? Zama Fatima tai sai ajiyar zuciya take saukewa cikin takaici ta soma magana hawaye na zuba "yanzu tsakani da Allah umma babu wanda zaiyi magana sai baba Balarabe ya kashe Indo da duka yau ma baki gani ba yadda ya sata a gaba yana tsine mata da debe mata albarka wai Asabe harda zuga shi idan yaje masallaci ya cewa liman yai shela duk wanda yake neman mace sadaka yazo ya aure masa ita" dafe kirji Aliyah tai tana cewa "innalillahi wa inna ilaihi raji'un yaushe hakan ta faru wai Balarabe meke damunsa ne da dai ba haka yake ba amma yanzu gabadaya ya gama canzawa kamar mai aljanu lallai da alamar tambaya kinga ki daina kuka Fatima tashi kije ki sallah maza kizo na aike ki gurin Kande ki ce ta bada kudin adashen nan ita kadai ake jira" to Fatima tace tana mikewa yayin da Aliyah tai tagumi cikin tausayawa yar uwarta Dalah da kuma halin da Indo ke ciki saidai tana fatan Allah yasa Dauda ya dawo da wuri insha Allahu tana sa ran zai auri Indo yarinyar nan ta huta da kuncin rayuwa.
Suna tafe a mota Nurain dake kallon photon Nafisa daya dauka bata sani abokinsa Yazid ne yadan daki kafadarsa yana cewa "kai mutumi na kaji tsoron Allah idan har kasan ba son yarinyar nan kake ba karka yaudare ta kaga kuna yi da mahaifinta" dariya Nurain yai yana kallon sa yace "amma ai kasan nima da yaudarar ce bazan ta'ba furtawa ba tunda tasan yadda Daddy suke da babanta kawai haka nan naji ina sha'awar ta domin tana da kayan aiki kuma zan aureta" kai Yazid ya jinjina yana yana mayar da hankalin sa kan tuki yace "amma fa baka da kirki ko kadan kasan madam din ka akwai bala'in kishi tasan da wannan maganar saita kusan kone maka gida" tabe baki Nurain yai yana cewa "dama ai ba da ita kadai zan zauna ba ni mijin mace hudu ne innaga dama a yau naso auren Nafisa zanyi" "umh umh fa Nurain banda cika baki" "to zuba ido kasha kallo muna dawowa daga tafiyar da zamuyi da ita zan auri Nafisa" Yazid dai jinsa yake amma yasan karya ne saidai kawai zai kyale shi kada yai masa magana yaga kamar ya takura shi.
Har suka isa cikin gari kai tsaye gidansa ya wuce a parlor ya samu yaransa guda biyu suna zaune da littafi a gaban su babbar tana koyawa karamar zama yai yana cewa "Amnah ina momyn ku"? D'agowa Amnah tai tana kallon sa tace "u're welcome Dad Mom na gurin aiki bata dawo ba" sauke ajiyar zuciya yai yana mikewa ya shiga part dinsa baifi minti biyar ba ta shigo cikin parlon ganin yaran basu lura da ita ba yasa tace "auta na karatu kuke ya school" duk d'agowa sukai suna kallon ta da gudu suka je suna rungumeta cikin shagwaba karamar tace "ni momy yunwa nake ji" kallon fuskarta tai "oh sorry dear ina Falmata batai lunch bane"? Ta karasa maganar tana kallon dining ga kuloli nan alamar an gama rike hannun ta tai tana cewa "muje nayi serving dinki" kafada ta ma'ke tana cewa "ni mom biscuits da ice cream nake so" daukar ta tai suna zuwa gaban fridge ta bud'e ta dauko mata kafin tace "Daddy ya dawo daga kauye ne" kai Amnah ta d'aga "eh mom ya tambaye ni ma kin dawo office nace a'a" jin haka yasa ta wuce gurin sa tabar yaran anan baya bedroom ya shiga wanka dan haka fita tai zuwa nata part din itama ta shirya kafin ya fito.
MRS AL'AMEEN AHMAD CE 😘
Yau kam nayi muku typing da yawa dan haka bazan sake yin posting ba sai ranar monday idan Allah ya kaimu da rai ya bamu aron numfashi da kwana.
YUSRAHMS.
Be good be helpful than everybody will like u to be a happy child like my daughter Fatima Ilham.
Mrs al'ameen Ahmad ce
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Ai littafin me kamar sarki bangarori ne daban daban zaku Sha labari kudai kawai ku taya ni da addu'a Allah ya bani dama da lafiyar yi muku typing da posting.
Mu kwana lafiya gaskiya zanyi kewar ku masoya ina mi'ko sakon godiya da gaisuwa ta gareku.
Batilah Abdullahi
Rakiya Abdullahi
Ruwaina Abdullahi
Surayyah magaji
Sadiya Khabeer
Ummi Ibrahim
Asma'u Abdullahi
Bintu 'Dalha.
Sai iyaye masu daraja girma hakuri kwazo Allah ya kara ri'ka muku ya tsare ku daga sharrin dukkan abun 'ki ya bamu rahmar sa duniya da lahira amin.
Mama Hauwa
Umman fati
Umman Basiru
Umman Suraj
Umman Huzaif
Umman usman
Maman baby
Maman Fadilah
Maman Maryam
Umma Habiba
Umma Addah
Sai kuma kaka mai kamar uwa kimin komai a rayuwa ta fatan Allah swt ya tsare ki ya kiyaye ki ya barmana ke ki kara tsahon kwana.
AISHATU SHU'AIBU🤣
SHU'AIBU MAI ALEWA🌹😘😘
🌹🌹🌹🌹🌹✨🌹🌹🌹🌹🌹🌹.
✍️Jinjina nake gareku yan group din mu na ANNURI marubuta Allah ya taimaka ya rikar ido yai karko basira ta karu hannu kada ya kosa alkalami yaita zayyanowa.
Safiyyah Aliyu wakili
Hajjara Abla's Glam
Rahmat A Abba Jada
Rabi'at bichi
Mrs Abubakar
Chp~ melody
Indo ce kano.
Mrs AL'AMEEN AHMAD CE mai tambarin yma dutse Jigawa new world new life and new style 👌.
5~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil 'Da'ina.
################
##############
###########
#######
####
###
##
#
TYPING 📲 {9:44AM 18/24}✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💎ME KAMAR SARKI 💎
💫 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫.
09~ AL-JABBAR
The irresistible
10~ AL-MUTAKABBIR
The majestic 🌹.
Dedicated to
Mr HAUSA EBOOKS 📚
SHURAIHU CEO📝📒📔📕
✍️YUSRAHMS ABUBAKAR
Mrs Al'ameen Ahmad ce😘
🌄SESSION ND REASSURE🌄
Episode 09 & 10
Marshall islands misalin'karfe daya da rabi na dare ko'ina da haske 🌃 gari yayi tsit ba motsin koda tsuntsu zaune Asad yake da phone a hannun shi tun karfe bakwai yake kiran wayar Mami amma bata daga ba karshe yanzu daya kira sai yaji switch up gabadaya ya damu ya sani dama za'ai haka Mami tayi fushi dashi wurgi yai da wayar daidai Isham ya fito daga bedroom cikin zafin nama yai tsalle yana cafe ta tsuka Asad yai yana zamewa ya kwanta kan lallausar cushion din tare da rufe ido.
Mamaki ne ya kama Isham me Asad keyi har yanzu bai kwanta ba zuwa yai kansa ya tsaya cikin alamun tambaya yace "buddy what is it? Said you wanted to talk, but haven't said a word, what happened"? Shiru yai bai bashi amsa ba duk da dama haka yake tunani "Asad ka fad'a min meke damunka ko akwai wani taimako dazan iya yi maka"? Batare daya d'ago ko ya bud'e ido ba yace "don't know how this happened" da mamaki Isham yace "haba buddy kamar ya bakasan me ke faruwa ba? me ne ya hana ka bacci? shine abinda nake son sani".
Tashi zaune Asad yai yana barin wurin ya koma jikin window ya tsaya yana kallon waje da ko'ina ya mamaye da haske kafin ya fara magana "nayi kiran Mami a waya amma ta'ki d'aga min" "ta'ki d'aga maka kira maybe bata kusa ne" kai ya girgiza "no tana wurin" "to kenan laifi kai mata"? Isham yai maganar yana karasawa inda yake ya dafa shi yana cewa "meyasa baka tsaya saida ka bata hakuri ba ka taho"? "Wai Isham wa ya fad'a maka laifi na mata kawai an samu sa'banin fahimta ne tsakani na da cousin dina" cikin tsokana Isham yace "tofa ashe harka fara soyayya bamu sani ba ko aure zakai n...................
Dariya Bara'atu tai tana cewa "gaskiya ne malam ka fad'i gaskiya idan muka samu Nafisa ta aure shi mun samu kofar arziki ba karama ba mutanen dake da miliyoyin kud'i a banki a boye" cikin nuna son zuciya Ilyah yace "to kin gani dai nasan 'ya'yana suna da 'kashin arziki yanzu abinda za'ai shine ke Nafisa idan sun sake dawowa kice ya sai miki waya wacce zaku ri'ka magana kinji kuma ki tabbata kina tatsar sa kudade domin baisan ciwon su ba" "to baba" Nafisa ta fad'a tana mikewa ta fita sai murmushi take ita kadai farin ciki ya ishe ta har ji take wata sabuwar iska mai launin sanyi tana shigarta.
Karo sukai da Salma zata fita tare ta Nafisa tai "ke ina zaki je haka ko gurin wancan saurayin naki me kama da tuntu'be shine kike wannan saurin kamar zaki tashi sama anji kunya" wata uwar harara Salma ta sakar mata tana cewa "akwai wanda yaji kunya irin ki kawai tsabar gidahumanci daga ganin mutun ba sanin sa kikai ba babu binkice kawai kice wai kina sonshi" rama hararar Nafisa tai tana cewa "eh haka nake kuma son kayana kuma banga abinda zai hana na aure shi ba sai mutuwa" wucewa Salma tai cikin jin haushin ta tace "au aina dauka mutuwar ma bazata hana kiba nidai yar uwarki ce ta jini a matsayi na namai sonki nake fad'a miki kibi a sannu" da kallo Nafisa ta bita tana tabe baki tace "ji shegiyar yarinya waini zatai wa wa'azi bazan bi a sannun ba da karfi zanbi sainaga wanda zai hana haba Salma na fahimci ba'kin ciki kike dani kuma saidai ki mutu domin mijin dazan aura ya kere naki kyau dan dadai ne babu inda ya zarta ba irin naki ba tudu da gangare yana tafi kamar agwagwa zaki dawo ki same ni" ta karasa maganar tana shiga d'akin su ta kwanta tare da rufe ido kawai tana tunanin Nurain a ranta.
Fatima kam daga gidan Dalah kai tsaye gidansu ta wuce Aliyah babarta na zaune ganin yadda ta shigo yasa tace "Fatima lafiya naga kamar kinyi kuka"? Zama Fatima tai sai ajiyar zuciya take saukewa cikin takaici ta soma magana hawaye na zuba "yanzu tsakani da Allah umma babu wanda zaiyi magana sai baba Balarabe ya kashe Indo da duka yau ma baki gani ba yadda ya sata a gaba yana tsine mata da debe mata albarka wai Asabe harda zuga shi idan yaje masallaci ya cewa liman yai shela duk wanda yake neman mace sadaka yazo ya aure masa ita" dafe kirji Aliyah tai tana cewa "innalillahi wa inna ilaihi raji'un yaushe hakan ta faru wai Balarabe meke damunsa ne da dai ba haka yake ba amma yanzu gabadaya ya gama canzawa kamar mai aljanu lallai da alamar tambaya kinga ki daina kuka Fatima tashi kije ki sallah maza kizo na aike ki gurin Kande ki ce ta bada kudin adashen nan ita kadai ake jira" to Fatima tace tana mikewa yayin da Aliyah tai tagumi cikin tausayawa yar uwarta Dalah da kuma halin da Indo ke ciki saidai tana fatan Allah yasa Dauda ya dawo da wuri insha Allahu tana sa ran zai auri Indo yarinyar nan ta huta da kuncin rayuwa.
Suna tafe a mota Nurain dake kallon photon Nafisa daya dauka bata sani abokinsa Yazid ne yadan daki kafadarsa yana cewa "kai mutumi na kaji tsoron Allah idan har kasan ba son yarinyar nan kake ba karka yaudare ta kaga kuna yi da mahaifinta" dariya Nurain yai yana kallon sa yace "amma ai kasan nima da yaudarar ce bazan ta'ba furtawa ba tunda tasan yadda Daddy suke da babanta kawai haka nan naji ina sha'awar ta domin tana da kayan aiki kuma zan aureta" kai Yazid ya jinjina yana yana mayar da hankalin sa kan tuki yace "amma fa baka da kirki ko kadan kasan madam din ka akwai bala'in kishi tasan da wannan maganar saita kusan kone maka gida" tabe baki Nurain yai yana cewa "dama ai ba da ita kadai zan zauna ba ni mijin mace hudu ne innaga dama a yau naso auren Nafisa zanyi" "umh umh fa Nurain banda cika baki" "to zuba ido kasha kallo muna dawowa daga tafiyar da zamuyi da ita zan auri Nafisa" Yazid dai jinsa yake amma yasan karya ne saidai kawai zai kyale shi kada yai masa magana yaga kamar ya takura shi.
Har suka isa cikin gari kai tsaye gidansa ya wuce a parlor ya samu yaransa guda biyu suna zaune da littafi a gaban su babbar tana koyawa karamar zama yai yana cewa "Amnah ina momyn ku"? D'agowa Amnah tai tana kallon sa tace "u're welcome Dad Mom na gurin aiki bata dawo ba" sauke ajiyar zuciya yai yana mikewa ya shiga part dinsa baifi minti biyar ba ta shigo cikin parlon ganin yaran basu lura da ita ba yasa tace "auta na karatu kuke ya school" duk d'agowa sukai suna kallon ta da gudu suka je suna rungumeta cikin shagwaba karamar tace "ni momy yunwa nake ji" kallon fuskarta tai "oh sorry dear ina Falmata batai lunch bane"? Ta karasa maganar tana kallon dining ga kuloli nan alamar an gama rike hannun ta tai tana cewa "muje nayi serving dinki" kafada ta ma'ke tana cewa "ni mom biscuits da ice cream nake so" daukar ta tai suna zuwa gaban fridge ta bud'e ta dauko mata kafin tace "Daddy ya dawo daga kauye ne" kai Amnah ta d'aga "eh mom ya tambaye ni ma kin dawo office nace a'a" jin haka yasa ta wuce gurin sa tabar yaran anan baya bedroom ya shiga wanka dan haka fita tai zuwa nata part din itama ta shirya kafin ya fito.
MRS AL'AMEEN AHMAD CE 😘
Yau kam nayi muku typing da yawa dan haka bazan sake yin posting ba sai ranar monday idan Allah ya kaimu da rai ya bamu aron numfashi da kwana.
YUSRAHMS.
Be good be helpful than everybody will like u to be a happy child like my daughter Fatima Ilham.
Mrs al'ameen Ahmad ce
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
Ai littafin me kamar sarki bangarori ne daban daban zaku Sha labari kudai kawai ku taya ni da addu'a Allah ya bani dama da lafiyar yi muku typing da posting.
Mu kwana lafiya gaskiya zanyi kewar ku masoya ina mi'ko sakon godiya da gaisuwa ta gareku.
Batilah Abdullahi
Rakiya Abdullahi
Ruwaina Abdullahi
Surayyah magaji
Sadiya Khabeer
Ummi Ibrahim
Asma'u Abdullahi
Bintu 'Dalha.
Sai iyaye masu daraja girma hakuri kwazo Allah ya kara ri'ka muku ya tsare ku daga sharrin dukkan abun 'ki ya bamu rahmar sa duniya da lahira amin.
Mama Hauwa
Umman fati
Umman Basiru
Umman Suraj
Umman Huzaif
Umman usman
Maman baby
Maman Fadilah
Maman Maryam
Umma Habiba
Umma Addah
Sai kuma kaka mai kamar uwa kimin komai a rayuwa ta fatan Allah swt ya tsare ki ya kiyaye ki ya barmana ke ki kara tsahon kwana.
AISHATU SHU'AIBU🤣
SHU'AIBU MAI ALEWA🌹😘😘
🌹🌹🌹🌹🌹✨🌹🌹🌹🌹🌹🌹.
✍️Jinjina nake gareku yan group din mu na ANNURI marubuta Allah ya taimaka ya rikar ido yai karko basira ta karu hannu kada ya kosa alkalami yaita zayyanowa.
Safiyyah Aliyu wakili
Hajjara Abla's Glam
Rahmat A Abba Jada
Rabi'at bichi
Mrs Abubakar
Chp~ melody
Indo ce kano.
Mrs AL'AMEEN AHMAD CE mai tambarin yma dutse Jigawa new world new life and new style 👌.
5~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil 'Da'ina.
################
##############
###########
#######
####
###
##
#
TYPING 📲 {9:44AM 18/24}✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💎ME KAMAR SARKI 💎
💫 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫.
09~ AL-JABBAR
The irresistible
10~ AL-MUTAKABBIR
The majestic 🌹.
Dedicated to
Mr HAUSA EBOOKS 📚
SHURAIHU CEO📝📒📔📕
✍️YUSRAHMS ABUBAKAR
Mrs Al'ameen Ahmad ce😘
🌄SESSION ND REASSURE🌄
Episode 09 & 10
Marshall islands misalin'karfe daya da rabi na dare ko'ina da haske 🌃 gari yayi tsit ba motsin koda tsuntsu zaune Asad yake da phone a hannun shi tun karfe bakwai yake kiran wayar Mami amma bata daga ba karshe yanzu daya kira sai yaji switch up gabadaya ya damu ya sani dama za'ai haka Mami tayi fushi dashi wurgi yai da wayar daidai Isham ya fito daga bedroom cikin zafin nama yai tsalle yana cafe ta tsuka Asad yai yana zamewa ya kwanta kan lallausar cushion din tare da rufe ido.
Mamaki ne ya kama Isham me Asad keyi har yanzu bai kwanta ba zuwa yai kansa ya tsaya cikin alamun tambaya yace "buddy what is it? Said you wanted to talk, but haven't said a word, what happened"? Shiru yai bai bashi amsa ba duk da dama haka yake tunani "Asad ka fad'a min meke damunka ko akwai wani taimako dazan iya yi maka"? Batare daya d'ago ko ya bud'e ido ba yace "don't know how this happened" da mamaki Isham yace "haba buddy kamar ya bakasan me ke faruwa ba? me ne ya hana ka bacci? shine abinda nake son sani".
Tashi zaune Asad yai yana barin wurin ya koma jikin window ya tsaya yana kallon waje da ko'ina ya mamaye da haske kafin ya fara magana "nayi kiran Mami a waya amma ta'ki d'aga min" "ta'ki d'aga maka kira maybe bata kusa ne" kai ya girgiza "no tana wurin" "to kenan laifi kai mata"? Isham yai maganar yana karasawa inda yake ya dafa shi yana cewa "meyasa baka tsaya saida ka bata hakuri ba ka taho"? "Wai Isham wa ya fad'a maka laifi na mata kawai an samu sa'banin fahimta ne tsakani na da cousin dina" cikin tsokana Isham yace "tofa ashe harka fara soyayya bamu sani ba ko aure zakai n...................