Sashe 24
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwanan Ramatu shida a rufe babu wanda ya leka yaga kalau take balle ace za'a je belinta saida dan uwanta ya dawo daga neman kud'i yaji labarin tana can a tsare sannan yahau mashin yaje akai shari'a ya biya kud'in suka taho yana mata fadan ta girma amma har yanzu ace bata da hankali itakam jinsa take a banza idan maganar ta shiga ta kunnen dama saita fita ta kunnen hagu.
"Kina jina Ramatu kikai shiru ko"? Hashimu ya fad'a yana hararar ta ta'be baki Ramatu tai "to me kake so nace hashimu" "ban sani ba wai Ramatu yaushe zaki hankali d'abi'ar ki kamar ba ta mutane ba"? "Au kana nufin ni dabba ce"? "Ni bance miki dabba ba inda sharri kike neman yi min gaskiya ki canza halinki haba rahma da girman ki kina abin yara ko yara bazasu buwayi gari haka ba indai sun san me suke".
Murgud'a baki tai tana kawar da kai daidai sun iso dabar mutanen gari ta tsakiyar dandali ganin idon kowa a kanta yasa ta soma masifa "to mayu meye kuka zuro min ido kowanne tsinanne yana kallo na ina munafikan da sukai karata to gani na dawo ban tabbata acan ba kuma ko yau rigima ta sake hado mu babu fashi saina ci uwar mutum na jajjaga ubansa a turmi.............
Katse ta Hashimu yai "wai dan Allah me kike haka wannan fa zubda girma ne gaban yara da manya kina matar aure harda d'a saurayi kina irin wannan abun" itama caraf tace "kai ka 'kyale ni saina fad'i abinda ke raina ko zuciya ta tayi sanyi idan na bari ni abun zai dama, kuna jina ba'a haifi wani shege a garin nan wanda ya isa ya ta'bo ni na rabu dashi ba ni bala'i da yake bacci ma Saida na tashe shi ni mace ce mai had'ari ku kiyayeni" 'bacin rai ne sosai ya kama Hashimu cikin fad'a yace "amma dai Ramatu kinyi asara kinji kunya wallahi har bansan yadda zan kwatanta miki ba saidai kawai nace Allah ya shirye ki" ganin zata magana yasa yace "bansan jin komai muje" wucewa sukai Ramatu na dawo da hannunta baya ta ware su alamar duk wanda yai zancen ta uwarsa.
Suna zuwa gida Hashimu ya hauta da fada a gaban Baffah yana cewa "mai kake kallo har Ramatu ta zama irin haka? Wato bata jin maganar ka ta rainaka bata da mafad'i kinga Ramatu kibi duniya a sannu".
Shiru Baffah yai yana kallon Ramatu zuciyar sa na suya yana matukar nadamar aurenta a rayuwa saidai kaddara ta riga fata zuwa shikam yanzu Ramatu tafi karfin sa babu abinda zaice mata sai Allah ya shirye ta, tunanin sane ya dawo jin hararramin yayan Ramatu Hashimu yana kai mata bugu da gudu tayi d'aki tsaki yai yana cewa "kana jinmu da mara mutuncin nan ko Baffah"? Sauke ajiyar zuciya Baffah yai "to me zance Hashim bani da abin fad'a fatana Allah yasa ta gane da wuri ta gyara kafin lokaci ya 'kure mata" juyawa Hashimu yai yana shirin fita yace "to ai shikenan Allah ya sauwake mata idan masifa ce sai anjima" da kallo Baffah yabi bayansa kafin ya kalli kofar d'akin Ramatu yana girgiza kai ciki damuwa ya mike yana ficewa daga gidan itakam Salamatu har ta daina mamakin abinda Ramatu take yanzu tafi tunanin kila Ramatu ba ita kadai bace akwai mutanen 'boye a jikinta.
Tun daga ranar da Ilyah ya samu goyon bayan Ramatu cewa basai kara taimakawa Baffah da aikin gonna ba sai Ilyah ya kangare ya koma bin abokai 'batattu wanda iyayensu suka sangarta su har suka koya masa munanan d'abi'u ciki harda sata da shan taba sukan rufe fuska dan kar a gane su idan yara yan mata sun tafi gona su tare su wacce tsautsayi ya fad'a kanta suyi mata fayde anyi shari'a dasu yafi sau a kirge yan sanda har sun gaji da kawo case din su ba irin azabar da basuyi musu ba amma sunki dainawa kamar kara zugasu ake har zaman gidan maza sunyi.
Lokacin kaka ma haka abun ya faru daga Baffah sai Sabi'u da Habu sukai aikin komai Ilyah ko tsinke bai dauka ba amma adalci irin na baffa daya tashi musu dinki tare ya basu ladan gona baya bambanta musu gudun rabuwar kai sai wannan shekarar ne ya zarta akan Ilyah ko kunya haka Ramatu ta rufe ido ta ri'ka zazzagawa Baffah magana wai yaji tsoron Allah dan kawai bana daya Ilyah bai masa aiki ba shine yabi ya tsane shi Baffah ci kanki baice da ita ba data dame shi ma tashi yai ya barmata gidan.
Alhamdulillah Lami ta soma karatu cikin sa'a gata da kokari sosai kuma ko kadan bata tunanin gida balle ace ta damu kawai karatun ta take saida akai jarrabawa ta kar'bo result dinta sannan Musbahu yai tunanin kaita gida taga iyayenta da danginta yasan duk tsiya yanzu kam Ramatu ta hakura ta risina bazata hana ta karatu ba ganin yadda ta dawo tayi kyau da kiba ta koshi abinta.
Suna zaune a d'aki Lami da Naja'atu suna hira mama ta shigo tana cewa "ku kam bakwa gajiya da zaman d'aki kamar munanan amare" dariya sukai Naja'atu na cewa "mama labari take bani wai tayi saurayi d'an makarantar su sunan sa Alpha shine nace zamu sha biki" bud'e baki mama tayi ita kuma Lami ta rufe ido tana cewa "mama ba haka nace mata ba sharri zatai min ba cewa yai yana sona ba kawai mutunci muke" dariya mama tay "eh ai na sani basai kince komai ba babanku yace ki fara shiri nan da sati zamuje garin ku ki gano iyayen ki" 'yar fara'ar dake fuskarta ce ta 'bace tana kallon mama jiki a sanyaye tace "to Allah ya kai mu" haka nan taji lokaci guda hankalin ta ya tashi bata tunanin kowa sai Ramatu.
Ganin yanayin ta yasa mama cewa "Lami meke damunki naga kamar canjin yanayi"? Kaita girgiza "babu komai" "shikenan to zakuje da Naja'atu ayi miki lalle da kitso" "to mama" mama na fita naja tace "aiko sai anje dani saina gano garin ku" murmushin dole Lami tayi gabadaya ta kasa sukuni batasan meyasa amma haka nan taji bata son komawa.
Washe gari suka gama shiri tsaf suka dauki hanyar 'kauye har suka isa garin Lami bata Sani ba kanta na sunkuye tana faman tunani da sa'ka da warwara saida taji mota ta tsaya sannan ta d'ago gabanta ya fad'i ganin Ramatu ta fito amma abinda daya bata mamaki ko kallon inda motar take batayi ba tai gaba abin da gyalenta mai datti kafarta ko takalimi shi kansa Musbahu bai manta da Ramatu ba amma yayi mamakin ganin ta kallesu sau daya ta kawar dakai tai gaba abinta.
Fitowa sukai suna shiga gidan Baffah na kofar d'akin sa a zaune gurin sa suka nufa suna zama shi kansa yayi mamaki sosai da annuri a fuskarsa yace "Musbahu kaine? Banyi tunanin ganinku ba sannu kuna tafe kaida iyalin"? Murmushi Musbahu yai yana gaida Baffah matarsa ma ta gaida dashi tare da yaranta.
"Ke Salamatu kawowa ba'ki ruwa da abinci yanzu" fitowa Salamatu tayi tana d'ebo ruwa tayo wajensu tana ajewa da tabarma ta zauna suka gaisa tana ta kallon Lami ba Salamatu ba hatta Baffah yanayin yadda yaga Lami tayi girma da kiba ya bashi mamaki.
Suna haka Ramatu ta dawo bata kuma kallon inda suke ba ta shige d'aki harda wa'ka itakam mama da batasan dawar garin ba batai tunanin ma wata Ramatu bace uwar Lami ta dauka Salamatu ce saida zance yai nisa sannan ta fahimta anan Musbahu ke cewa Baffah su zasu tafi amma Lami ta zauna tunda yanzu ba makaranta idan an basu hutu sai yazo ya dauketa.
"Kai Baffah ya jinjina yana cewa "naji zancen ka Musbahu kuma nagode sosai Allah ya kara arziki Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lafiya ka gaishe min da mahaifin naka" mi'kewa sukai Musbahu na cewa "to shikenan Baffah zamu tafi" mi'kewa shima Baffan yai zanyi musu rakiya shida Lami a hanya yana sake mishi godiya saida suka tafi ya dawo gida Lami zata zauna a gurin sa yace "a'a tashi maza ki shiga ku gaida da babar taki man ki bata hakuri kinji" kai Lami ta d'aga tana mi'kewa ta shiga d'akin Ramatu ganin ta tayi zaune har lokacin wa'ka take rerawa mamaki ne ya kama Lami yau Ramatu ke wa'ka kamar maro'kiya karasawa tayi tana cewa.
"Babah" d'agowa Ramatu tai tana kallon Lami zuwa wani lokaci tace "uban me ya kawo ki gurin na? Shiru Lami tayi Ramatu taci gaba "ai na dauka har abada a gunsa zaki tabbata tunda kin za'bi zama da wancan tambad'addan😲 saidai ki samu wata uwar daga yau amma badai niba".
Hawaye ne ya ciko idon Lami tana kallon Ramatu tace "dan Allah kiyi hakuri..................
Da yatsa Ramatu ta nunata "ke kada ki sake bani hakuri kinsan da hakurin kika za'bi zabin ubanki saboda kin maida ni sako tumaki 'ballo jakuna baki san wacece Ramatu amma yau zaki sani fita min a d'aki" kuka Lami keyi tace "dan Allah kiyi hakur.................
Bata karasa ba Ramatu ta bud'e kasan gado tana dauko sungumi ta mi'ke tsaye tare da cewa "dan ubanki kin dauke ni mutuniyar banza ce zaki fita ko saina rad'e ki" nufota tayi da gudu Lami ta fita a d'akin Ramatu ta rufa mata baya har gaban Baffah tana cewa "uban naki ma bai isa hani na karya miki 'kafa ba tunda kin za'bi kibi son ran ubanki na fad'a miki saidai ki nemi wata uwar" ta karasa maganar tana juyawa da sunguminta kuka sosai lami keyi ta durkusa a gaban Baffah tana cewa "dan Allah Baffah ka fahimtar da ita tayi min afuwa ita fa mahaifiya tace bazan iya jure fushinta a kaina ba hakan barazana ne ga zuciya ta da nasan abinda zai faru kenan bazan bishi ba zanyi ta hakuri ina zama cikin duhun jahilci na😔.
"Kina jina Ramatu kikai shiru ko"? Hashimu ya fad'a yana hararar ta ta'be baki Ramatu tai "to me kake so nace hashimu" "ban sani ba wai Ramatu yaushe zaki hankali d'abi'ar ki kamar ba ta mutane ba"? "Au kana nufin ni dabba ce"? "Ni bance miki dabba ba inda sharri kike neman yi min gaskiya ki canza halinki haba rahma da girman ki kina abin yara ko yara bazasu buwayi gari haka ba indai sun san me suke".
Murgud'a baki tai tana kawar da kai daidai sun iso dabar mutanen gari ta tsakiyar dandali ganin idon kowa a kanta yasa ta soma masifa "to mayu meye kuka zuro min ido kowanne tsinanne yana kallo na ina munafikan da sukai karata to gani na dawo ban tabbata acan ba kuma ko yau rigima ta sake hado mu babu fashi saina ci uwar mutum na jajjaga ubansa a turmi.............
Katse ta Hashimu yai "wai dan Allah me kike haka wannan fa zubda girma ne gaban yara da manya kina matar aure harda d'a saurayi kina irin wannan abun" itama caraf tace "kai ka 'kyale ni saina fad'i abinda ke raina ko zuciya ta tayi sanyi idan na bari ni abun zai dama, kuna jina ba'a haifi wani shege a garin nan wanda ya isa ya ta'bo ni na rabu dashi ba ni bala'i da yake bacci ma Saida na tashe shi ni mace ce mai had'ari ku kiyayeni" 'bacin rai ne sosai ya kama Hashimu cikin fad'a yace "amma dai Ramatu kinyi asara kinji kunya wallahi har bansan yadda zan kwatanta miki ba saidai kawai nace Allah ya shirye ki" ganin zata magana yasa yace "bansan jin komai muje" wucewa sukai Ramatu na dawo da hannunta baya ta ware su alamar duk wanda yai zancen ta uwarsa.
Suna zuwa gida Hashimu ya hauta da fada a gaban Baffah yana cewa "mai kake kallo har Ramatu ta zama irin haka? Wato bata jin maganar ka ta rainaka bata da mafad'i kinga Ramatu kibi duniya a sannu".
Shiru Baffah yai yana kallon Ramatu zuciyar sa na suya yana matukar nadamar aurenta a rayuwa saidai kaddara ta riga fata zuwa shikam yanzu Ramatu tafi karfin sa babu abinda zaice mata sai Allah ya shirye ta, tunanin sane ya dawo jin hararramin yayan Ramatu Hashimu yana kai mata bugu da gudu tayi d'aki tsaki yai yana cewa "kana jinmu da mara mutuncin nan ko Baffah"? Sauke ajiyar zuciya Baffah yai "to me zance Hashim bani da abin fad'a fatana Allah yasa ta gane da wuri ta gyara kafin lokaci ya 'kure mata" juyawa Hashimu yai yana shirin fita yace "to ai shikenan Allah ya sauwake mata idan masifa ce sai anjima" da kallo Baffah yabi bayansa kafin ya kalli kofar d'akin Ramatu yana girgiza kai ciki damuwa ya mike yana ficewa daga gidan itakam Salamatu har ta daina mamakin abinda Ramatu take yanzu tafi tunanin kila Ramatu ba ita kadai bace akwai mutanen 'boye a jikinta.
Tun daga ranar da Ilyah ya samu goyon bayan Ramatu cewa basai kara taimakawa Baffah da aikin gonna ba sai Ilyah ya kangare ya koma bin abokai 'batattu wanda iyayensu suka sangarta su har suka koya masa munanan d'abi'u ciki harda sata da shan taba sukan rufe fuska dan kar a gane su idan yara yan mata sun tafi gona su tare su wacce tsautsayi ya fad'a kanta suyi mata fayde anyi shari'a dasu yafi sau a kirge yan sanda har sun gaji da kawo case din su ba irin azabar da basuyi musu ba amma sunki dainawa kamar kara zugasu ake har zaman gidan maza sunyi.
Lokacin kaka ma haka abun ya faru daga Baffah sai Sabi'u da Habu sukai aikin komai Ilyah ko tsinke bai dauka ba amma adalci irin na baffa daya tashi musu dinki tare ya basu ladan gona baya bambanta musu gudun rabuwar kai sai wannan shekarar ne ya zarta akan Ilyah ko kunya haka Ramatu ta rufe ido ta ri'ka zazzagawa Baffah magana wai yaji tsoron Allah dan kawai bana daya Ilyah bai masa aiki ba shine yabi ya tsane shi Baffah ci kanki baice da ita ba data dame shi ma tashi yai ya barmata gidan.
Alhamdulillah Lami ta soma karatu cikin sa'a gata da kokari sosai kuma ko kadan bata tunanin gida balle ace ta damu kawai karatun ta take saida akai jarrabawa ta kar'bo result dinta sannan Musbahu yai tunanin kaita gida taga iyayenta da danginta yasan duk tsiya yanzu kam Ramatu ta hakura ta risina bazata hana ta karatu ba ganin yadda ta dawo tayi kyau da kiba ta koshi abinta.
Suna zaune a d'aki Lami da Naja'atu suna hira mama ta shigo tana cewa "ku kam bakwa gajiya da zaman d'aki kamar munanan amare" dariya sukai Naja'atu na cewa "mama labari take bani wai tayi saurayi d'an makarantar su sunan sa Alpha shine nace zamu sha biki" bud'e baki mama tayi ita kuma Lami ta rufe ido tana cewa "mama ba haka nace mata ba sharri zatai min ba cewa yai yana sona ba kawai mutunci muke" dariya mama tay "eh ai na sani basai kince komai ba babanku yace ki fara shiri nan da sati zamuje garin ku ki gano iyayen ki" 'yar fara'ar dake fuskarta ce ta 'bace tana kallon mama jiki a sanyaye tace "to Allah ya kai mu" haka nan taji lokaci guda hankalin ta ya tashi bata tunanin kowa sai Ramatu.
Ganin yanayin ta yasa mama cewa "Lami meke damunki naga kamar canjin yanayi"? Kaita girgiza "babu komai" "shikenan to zakuje da Naja'atu ayi miki lalle da kitso" "to mama" mama na fita naja tace "aiko sai anje dani saina gano garin ku" murmushin dole Lami tayi gabadaya ta kasa sukuni batasan meyasa amma haka nan taji bata son komawa.
Washe gari suka gama shiri tsaf suka dauki hanyar 'kauye har suka isa garin Lami bata Sani ba kanta na sunkuye tana faman tunani da sa'ka da warwara saida taji mota ta tsaya sannan ta d'ago gabanta ya fad'i ganin Ramatu ta fito amma abinda daya bata mamaki ko kallon inda motar take batayi ba tai gaba abin da gyalenta mai datti kafarta ko takalimi shi kansa Musbahu bai manta da Ramatu ba amma yayi mamakin ganin ta kallesu sau daya ta kawar dakai tai gaba abinta.
Fitowa sukai suna shiga gidan Baffah na kofar d'akin sa a zaune gurin sa suka nufa suna zama shi kansa yayi mamaki sosai da annuri a fuskarsa yace "Musbahu kaine? Banyi tunanin ganinku ba sannu kuna tafe kaida iyalin"? Murmushi Musbahu yai yana gaida Baffah matarsa ma ta gaida dashi tare da yaranta.
"Ke Salamatu kawowa ba'ki ruwa da abinci yanzu" fitowa Salamatu tayi tana d'ebo ruwa tayo wajensu tana ajewa da tabarma ta zauna suka gaisa tana ta kallon Lami ba Salamatu ba hatta Baffah yanayin yadda yaga Lami tayi girma da kiba ya bashi mamaki.
Suna haka Ramatu ta dawo bata kuma kallon inda suke ba ta shige d'aki harda wa'ka itakam mama da batasan dawar garin ba batai tunanin ma wata Ramatu bace uwar Lami ta dauka Salamatu ce saida zance yai nisa sannan ta fahimta anan Musbahu ke cewa Baffah su zasu tafi amma Lami ta zauna tunda yanzu ba makaranta idan an basu hutu sai yazo ya dauketa.
"Kai Baffah ya jinjina yana cewa "naji zancen ka Musbahu kuma nagode sosai Allah ya kara arziki Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lafiya ka gaishe min da mahaifin naka" mi'kewa sukai Musbahu na cewa "to shikenan Baffah zamu tafi" mi'kewa shima Baffan yai zanyi musu rakiya shida Lami a hanya yana sake mishi godiya saida suka tafi ya dawo gida Lami zata zauna a gurin sa yace "a'a tashi maza ki shiga ku gaida da babar taki man ki bata hakuri kinji" kai Lami ta d'aga tana mi'kewa ta shiga d'akin Ramatu ganin ta tayi zaune har lokacin wa'ka take rerawa mamaki ne ya kama Lami yau Ramatu ke wa'ka kamar maro'kiya karasawa tayi tana cewa.
"Babah" d'agowa Ramatu tai tana kallon Lami zuwa wani lokaci tace "uban me ya kawo ki gurin na? Shiru Lami tayi Ramatu taci gaba "ai na dauka har abada a gunsa zaki tabbata tunda kin za'bi zama da wancan tambad'addan😲 saidai ki samu wata uwar daga yau amma badai niba".
Hawaye ne ya ciko idon Lami tana kallon Ramatu tace "dan Allah kiyi hakuri..................
Da yatsa Ramatu ta nunata "ke kada ki sake bani hakuri kinsan da hakurin kika za'bi zabin ubanki saboda kin maida ni sako tumaki 'ballo jakuna baki san wacece Ramatu amma yau zaki sani fita min a d'aki" kuka Lami keyi tace "dan Allah kiyi hakur.................
Bata karasa ba Ramatu ta bud'e kasan gado tana dauko sungumi ta mi'ke tsaye tare da cewa "dan ubanki kin dauke ni mutuniyar banza ce zaki fita ko saina rad'e ki" nufota tayi da gudu Lami ta fita a d'akin Ramatu ta rufa mata baya har gaban Baffah tana cewa "uban naki ma bai isa hani na karya miki 'kafa ba tunda kin za'bi kibi son ran ubanki na fad'a miki saidai ki nemi wata uwar" ta karasa maganar tana juyawa da sunguminta kuka sosai lami keyi ta durkusa a gaban Baffah tana cewa "dan Allah Baffah ka fahimtar da ita tayi min afuwa ita fa mahaifiya tace bazan iya jure fushinta a kaina ba hakan barazana ne ga zuciya ta da nasan abinda zai faru kenan bazan bishi ba zanyi ta hakuri ina zama cikin duhun jahilci na😔.